Showing 24001 words to 27000 words out of 201092 words
Chapter 9 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt
tayin nata, babu yanda bata yi ba amma muka kartake cewa dole sai ita d'in zata je.
Haka aka zo har gida aka tafi da ita da Mallam, aka yo mata passport na tafiya aikin Hajji. Saboda nan da sati bitu za a fara tafiya.
_Rayuwar nan cike take da k'alubale masu girman gaske. Mafi girman jarrabta shi ne a had'a ka da ciwo. Duk wani talauci mai sau'ki ne idan kana da lafiya. Cutar sickler na d'aya daga cikin manyan cutuka, sai dai kar mu d'auki hakan a matsayin iyakar rayuwarmu ke nan, sau da dama masu lafiyar suna mutuwa su bar masu fama da ciwon. Allah Ya 'kare mu da lafiya, Ya bamu ikon cinye jarabawoyinmu._
Pinky durling💗
*RAZ 2*
[8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥
(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)
Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_
1⃣6⃣
Shirye-shiryen tafiyar su Amrah ya kankama sosai, har a makaranta ta yi bankwana.
Sai dai kuma abin da yake ci min tuwo a akushi, sanin lalurin Amrah da na yi, tana da buk'atar mataimaki a aikin Hajji da zata yi.
Yarinya mai yawan ciwo, bai kamata ta yi tafiyar d'in mako biyar ba tare da mai kula da ita ba.
Duk sanda zan mata maganar sai dai kawai ta yi murmushi, ta ce,
"Umma babu komai insha Allahu. kin ga ai na riga da na saba."
"Kayya, Amrah ai shi ciwo baya da sabo. Sai dai addu'a kawai."
Ranar da ya rage kwana biyar su tashi ne Hajiya Suhaila ta zo, take shaida min wai zata je aikin Hajji ita da Islam, sai dai su d'in ta Abuja zasu tashi, kyauta aka ba mai gidanta kujerar guda d'aya, yanayin aikinsa ya sa ya ce ba zai je ba. Shi ne ya had'a da Islam ita ya biya mata su yi tare.
Duk da ba ta gari d'aya zasu tashi da Amrah ba, si da na samu kaina da kwanciyar hankaali, na ji wani sanyi sanyi a zuciyata.
Shi kan shi Annur ya ji da'di sosai, a ranar ya zo mata bankwana saboda zai je Bauchi gobe, akwai wata University da ya zana, yake son zuwa don ganin yanda aikin ya kasance.
Har da kuka Amrah tayi sanda zasu rabu, ji take tamkar ba zasu sake had'uwa ba.
Canjin riyals ya mata na dubu hamsin, sanin ko ya bata ba zata karb'a ba ya sa ya bani cewa na ajiye mata.
Na masa godiya sosai tare da fatan alkhairi a tafiyarsa.
Haka lokacin tafiya ya yi muka raka ta har Hajj camp, daga can aka mana iyaka da ita, cewa za a fara kwasarsu a marcopolo zuwa Airport.
Tafiyar Amrah ta zame min wani gagarumin abu, kwata-kwata hankalina ya kasa kwanciya, duk da muna waya da ita akai akai, tun daga ranar da suka dira Jidda har yau da zasu bar Birnin Madina, zuwa garin Makka.
Bayan sun isa Makka ma sai da ta kira ni, a lokacin har harami ta je ta dawo.
"Umma yau sai ga ni ga abin da nake gani a kallo, ka'abah. Umma ashe k'atuwa ce ba k'arama ba, amma a kallo sai nake ganinta kamar k'arama."
A yanayin da ta yi maganar kawai ya isa ya tabbatar da halin farin cikin da take ciki, sosai take nishad'i.
"To Amrah dama ina ta ga zama k'arama? Ki ce sai kika ga muk'ama Ibrahima."
Na fa'da da fara'a sosai kamar tana a gabana.
"Umma na ga muk'ama Ibrahima, sai dai daga nesa ne ban matsa inda take ba saboda cinkoso. Insha Allahu nan ba da jimawa ba zan matsa har inda take in tab'a da hannuwana."
Shiru na yi jim, kafin na ce,
"Amma ki kula sosai Amrah. Kin ga ke d'in ba wani girma ne da ke ba, kar a je a matse ki ki gagara numfashin kirki. Ina jin labarin yanda cunkoso yake kashe mutane fa."
Murmushi ta yi mai sauti kafin ta ce,
"Insha Allahu Umma zan kula sosai. Da yake ma tare muke da Maman Abba, nan d'in ma d'akinmu d'aya da su."
"Allah sarki! Matar kirki ke nan. Na ji da'di sosai da Allah Ya had'a ku, dama tun a Hajj camp d'in nan na fahimci suna da kirki sosai.
To ya maganar su Hajiya suhaila? Kun had'u kuwa?"
"Bamu had'u ba umma. Jiya dai mun yi waya cewa sai gobe zasu zo nan Makka. Kin san su basu je Madina da wuri ba."
"Haka ne." Na furta ina canza salon maganar daga wasa i zuwa ta kirki sosai,
"Dan Allah Amrah kar ki manta da abin da na saka ki. Ki ma kanki addu'a sosai, Allah Ya yaye miki cutar nan, da dukkan 'yan uwa musulmai."
Ajiyar zuciya ta sauke had'e da fad'in,
"Insha Allahu zan yi sosai Umma. A Madina ma na yi ai."
Murmushi mai sauti na yi,
"Allah Ya karb'a to. Da duk wata addu'a da ta dace ba sai na fa'da miki ba. Ki gaishe da maman Abban, sai anjima." Na tsinke wayar.
Haka Amrah suka yi ibada sosai, kamar yanda nake ji daga Maman Abba a duk lokacin da muka gaisa da ita, tana yawaita fad'a min,
"Gaskiya Maman Amrah kin yi sa'ar 'ya, mai hankali, tarbiyya da kuma ilimin addini.
So tari idan wani abu ya shige min duhu, ita take tunasar da ni, da duk sauran 'yan d'akin ma.
Bata wasa da zuwa masallaci, duk irin laziness d'in da nake ji a kan zuwa masallaci, ita zata kwantar da kalamanta, ta sanyaya min jiki, wanda dole sai na je masallacin.
Baccinta k'alilan ne, tana raba darenta da nau'ukan ibadu, wanda ko a cikin manyan mata da suka gama mallakar ilahirin hankulansu, ba lallai a samu kamarta ba.
Na matuk'ar jin dad'in shigowarta duniyata, ta gyara min kurakuraina cikin hikima da fasaha, yanda ba zan tab'a jin haushinta ba. Ta tunatar da ni abubuwa da dama, wanda ba llallai ba ne na tuna su a duniyata.
Ina mai k'ara jaddada miki maman Amrah, ki k'ara gode wa Allah da kyautar Amrah da Ya baki."
A dai-dai lokacin da ta kai aya a zancenta, na murmusa cike da jin dad'in kalamanta, had'e da furucin,
"Alhamdulillah." A tak'aice.
Jin Amrah ta karb'i wayar ya sa na ce,
"Sai anjima Amrata, a yi ibada sosai."
"Insha Allahu, Ummah. 'Yan jirgi na farko ma har an saka su yin d'awafin bankwana."
"To madallah. Sai anjima."
Cike da jin dad'in kalaman Maman Abba na ajiye wayar bisa kujera. Ni kad'ai ke sakar ma kaina murmushi. Ko da maman Abba bata fad'i ba, na sani, na san cewa na yi sa'ar 'ya, abar alfahari, wacce zata iya rayuwa a duk duniyar da zata tsinci kanta, ko da ni ko babu ni.
Murmushi bai fice daga fuskata ba na ji salllamar Annur, amsa masa na yi da murmushin da ban kawar da shi ba.
"Maraba da Annur."
Na furta had'e da mik'ewa na bashi wurin zama.
Bayan mun gaisa ne yake shaida min jiya ya dawo daga Abuja, maganar sabon ginin da zai ma kamfanin magani na dana, sabon reshen da zasu bud'e a garin Minna.
Fatan alkhairi na masa, sannan ya zaro kud'i naira dubu goma ya ajje min,
"Annur baka gajiya ne wai? Wasu lokutan har kunyarka nake ji, wasu lokutan na kan ji ina ma zaka duba zuciyata ka ga yanda nake ji a duk sanda zaka yi min kyauta? Na so dai a ce abin ya tsaya a tsakanin kai da Amrah kawai."
"Bana son jin haka daga bakinki Umma. Ko kin manta cewa ni ma d'anki ne kamar Amrah? A ganina, duk abin da zan iya yi ma Momy ba tare da haufin komai ba, haka zan miki shi ba tare da wani abu ba.
Please and please Umma, ki d'aukeni tamkar yanda na da'uke ki, ki bani matsayi kamar yanda na baki. Ki daina k'o'karin dakatar da ni daga kyautata miki."
Sai a sannan ya dakata da maganarsa, yana mai duk'ar da kansa k'asa.
Ajiyar zuciya na sauke,
"Haka ne Annur. Kar ka tab'a tunanin akwai wani banbanci a tsakaninka da Amrah. Yanda take tawa haka kaima kake nawa. Allah ya maka albarka ya taimake ka a kan duk k'udururrukanka na alkhairi."
"Har na ji dad'i Umma. Bara in tashi. Su momy ma gobe muke tsammanin dawowarsu."
cikin Mamaki na ce,
"Tun da wuri haka? In ce ko su Amrah sun riga su tafiya?"
Bayan ya mik'e tsaye ya ce,
"Sun riga su kam. Kin san yanayin tafiyar tasu ba d'aya ba. Su ta can b'angaren tuni aka fara kwasar Alhazai, tun sallah da kwana hud'u."
Mi'kewar na yi ni ma na ce,
"Allah Ya dawo mana da su lafiya. Sai anjima."
Bayan kamar sati d'aya su Amrah suka dawo, sosai na yi mamakin yanda ta koma, ta yi b'ul-b'ul gwanin sha'awa kamar ba ita ba. Ta yi kyau matu'ka, ciwo kuma dama tun da ta je sau d'aya kawai ya taso mata, kuma Hajiya suhaila da Maman abba suka kai ta Saudi German, inda aka bata treatment mai kyau, suka kula da ita, suka killace ta har sai da suka ga ta murmure kamar ba ita ba.
Har da hak'orin Makka na zinari ta saka, wanda ya haskaka hak'oranta, ta sake cika sosai.
Sosai Annur ya yi farin cikin ganinta, wanda a ranar da ta dawo ya d'ora idanuwansa a nata, ya shiga wani irin hali mai wuyar fassara, duk irin dod'ad'diyar k'walwar mutum dole ya fahimci halin da suke ciki, dole a ga tsantsar kewar ganin fuskokin junansu da suka yi, na tsawon kwanaki talatin da takwas.
A cikin wannan rana ne Annur ya furta mata kalmar *"I LOVE YOU AMRAH."* Kalmar da bata tab'a shiga tsakaninsu ba tun da suke, saboda ita Amrah har a lokacin gani take kamar ba son soyayya take ma Annur ba, kamar sha'kuwa ce kawai a tsakaninsu. Sai dai kuma jin kalmar da ta fito a tsakanin lab'bansa, ya sa ta kasa gasgata kanta, take jin wani sabon yanayi a duniyarta.
*Sai yanzu, Annur? Duk iya zamanku da Amrah sai yanzu ka iya furta mata wannan gagarumar kalmar, wadda baka tab'a furta ta ga kowa ba?*
*Masha Allah! Hakan ya yi kyau ai.*
*Ina team Amranoor? Abin da kuka jima kuna tsumayi ko? To yau dai ta faru, sai kwasar rawa ke nan.*
*Wiyara wattpadians? Simply search PrincessAmrah. Vote and comment on each line, I'll be glad if you do so.*
Pinky durling💗
*RAZ 2*
[8/30, 3:35 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥
(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)
Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_
1⃣7⃣
Tun daga lokacin da soyayya mai 'karfi ta gama shiga tsakaninsu, zuciyata take ciki da farin ciki.
Sosai ciwonta ya yi sauk'i kuma, tun daga sanda suka dawo daga Saudiyya, har yanzu.
Yanzu haka Amrah ta shiga SS2 ne har ma sun kusa shiga 3, Annur kuma ya samu aiki a wani babban kamfanin k'ere-k'eren motoci da ke Birnin Abuja, yana masu aiki ta b'angaren zane-zane.
Hajiya Suhaila kuma ta samu Dady'n su Noor da maganarsa shi da Amrah, bai hana ba, saboda shi dama babban burinsa dai yaransa su ginu bisa tafarki mai kyau, su samu ingantaccen ilimi wanda zasu amfana da shi, kuma ya yi alfahari da su. Kuma Noor d'insa ya samu. Dan haka ba zai hana sa auren duk wacce ransa ke so ba.
A lokacin da ta shiga SS 3 ne aka fara maganar aure, har ma manya sun shiga maganar.
Har a tsawon wannan lokacin Amrah bata daina tunanin mutumin da ta yawaita gani a asibiti cikin keken guragu ba, bata daina mamakin mutumin ba, sau da dama ta kan same ni da maganar,
"Umma na rasa yanda zan yi na cire wancan mutumin daga zuciyata. A duk sanda zan zauna ni ka'dai, ya kan fad'o min a rai. Na rasa ko shi d'in waye, ban tab'a ganin kama irin tasu ba."
"Ba abun tunani ba ne wannan ba Amrah. Kin san a duniyar nan ana kama, akwai wanda kai kanka idan ka kalle shi zaka san kuna kama, kuma a zahirin gaskiya baka had'a komai da shi ba. Dan haka ki daina wannan tunanin. Annur d'inki dai shi ne kawai, kuma insha Allahu shi zaki aura."
Da kunya ta duk'ar da kanta k'asa, tana wasa da yatsun hannunta.
Kud'in neman auren Amrah kansu dubu d'ari biyu aka kawo, a raina har ina jin kamar sun yi yawa.
Haka kayan saka rana da aka kawo, komai a wadace, katan katan d'in abubuwa haka aka ringa dire su a tsakar gidanmu.
Wata bakwai aka saka auren, wanda ya yi dai-dai da gama makarantarta.
Daga sanda aka kawo kayan saka rana, kafin a raba su sai da ta yi saukar Al-Qur'ani, tana fatan Allah Ya saka albarka a rayuwar da zata tsinci kanta, rayuwar da take yawan tunanin fad'amawa, take jin ina ma a ce a gidansu zata yita zama ko bayan auren. Ko kad'an bata son abin da zai raba ta da gida. Duk sanda zan yi wata tafiya zuwa garinmu, kafin in dawo sai ta yi ciwo, ba wai ciwon sikilarta ba, ciwon rashi na a kusa da ita kawai. Saudiya ma da ta je ashe daga farko sai da ta yi, daga baya ne ta koma dai-dai. To bare kuma yanzu da zata tafi ta bar ni, bari na har abada. Zata fad'a wata sabuwar rayuwar, mai cike da k'alubale.
Ba wai Amrah kad'ai ba, ni ma kaina da na haife ta dan dai aure ya zama dole ne. Har ji nake a raina 'Banda aure ibada ne, me zai sa ka haifi 'yarka, ka raine ta tun tana 'karama, ka so ta, ta so ka, amma rana d'aya wani ya raba ka da ita?'
Hawaye nake ni kad'ai a duk sanda na keb'e, nake irin wannan tunanin.
Ya zan yi da tunanin Amrah bayan barinta gida? Ya zan yi na cire tunaninta daga zuciyata? Wane hali zata ringa shiga a duk lokacin da ciwonta ya taso?
Sauk'in ma d'aya, bani da haufi ko kad'an a rayuwar da zata fad'a. Bana haufin wanda zata yi rayuwa a k'ark'ashinsa. Na tabbata zai kula da ita, tamkar yanda zan kula da ita. Zai nuna mata soyayya, fiye da yanda ni zan nuna mata. Zai bata ingantacciyar rayuwa, fiye da yanda ni zan bata.
Sallamar da Amrah ta yi ce ta dakatar da ni daga duniyar tunanin da na lula,
"Umma, ke kad'ai?" Ta furta had'e da zama kusa da ni.
Murmushi na k'irk'iro had'e da furta,
"Ni kad'ai fa. Ya makarantar?"
"Makaranta lafiya k'alau Umma. Yanzu ma Mallam yake fad'a min wata musabak'a da ta taso. Wai za a yi ta nan da wata biyar, ta k'asa ce. Kin san ni na wakilci jihar Katsina waccan shekarar, har na zo ta biyu. To yanzu a cikin mu ukun da muka zo farko ne aka d'auke mu, mu za a had'a da mutum uku da suke ko wace jiha, idan an had'a mu a nan ma wata gasar ce, wanda suka zo farko ciki za a fitar da wanda zasu wakilci Najeriya."
"To fa!" Na jinjina kai.
"Abun na yi ne ashe. Ba dai sai an k'ara k'unshe ku ba wannan karon ma ko?"
Murmushi ta yi bayan ta mik'e tsaye, ta cire hijabin jikinta.
"Ba za a 'kunshe mu ba umma. Wancan ma dan muna da yawa ne sosai, akwai wanda suke da bu'katar gyara sosai a karatunsu. Amma wannan mu uku ne kawai, ni ce ma kawai fa daga islamiyarmu, sauran mutum biyun kowa da tasa makarantar."
"Yauwa to, yanzu na ji magana. Allah Ya taimaka Ya sa a yi a sa'a."
"Ameen Umma." Ta fura tare da shigewa cikin d'aki.
Babu jimawa kuma ta fito, fuskarta babu annuri ta ce,
"Umma, wai kuma yanzu Mallam Kamala ya kira ni, wai akwai wani wa'azin aure da aka gayyace shi ba zai samu damar zuwa ba, wai in taimaka in wakilce shi.
Umma wallahi ni ban shirya ma wa'azi ba yau, bare kuma na aure wanda dole sai an tsara komai." Ta dafe kanta had'e da zama.
Kad'a mata kai na yi, fuska d'auke da murmushi na ce,
"A'a 'yata. Bana son jin hakan daga gare ki. Malaminki fa ne ya buk'aci ki taimaka masa."
Ajiyar zuciya ta sauke,
"Ba wai bana son yi ba ne Umma, shirya masan ne dai ban yi ba. Kyau a ce tun jiya ya sanar da ni, ko kuma islamiyyar safe. Amma sai yanzu da azahar ta kusa ne zai fad'a min? Wai kuma da la'asar ake son in fara?"
Dafa mata kai na yi, cike da bata k'warin guiwa na ce,
"A hakan dai zaki daure ki yi. A cikin mutum nawa da ke makarantar, ya ware ki ke kad'ai ya ce ke zaki wak'ilce sa? A ganina ai wannan ma abin alfahari ne, ko?"
Bata son jayayya da ni ko kad'an, a bata so d'in ta hak'ura, ta d'auko takarda da biro ta fara rubutu.
Ko da la'asar ta yi ta gama shirinta, dama ya turo mata inda yake son ta je d'in.
Hijabinta ta saka har k'asa, mai kalar ruwan toka. Mai hannu ce, hakan ya bata damar fiddo tafukan hannyenta a waje, ta rataye k'aramar jakarta, ta d'aura ni'kabinta, sannan ta min bankwana.
Fatan alkhairi na mata, sannan mahaifinta ma da ya dawo dai-dai lokacin ya mata, ta tafi.
Daf da magrib sai gata ta dawo a rikice, tamkar wacce bata cikin hayyacina.
Kallo d'aya zaka mata ka tabbatar bata cikin natsuwarta, kamar akwai wani abu na tashin hankali da ta gani.
Tambayarta nake me ke damunta? Me ya same ta? Amma ta kasa furta min komai, kallona kawai take tana zazzare ido.
Salati nake ina mai k'ara dubanta, duba ta tsanaki na ce,
"Zauna ga tabarma nan. Ki natsu sosai sannan ki min bayani."
Bata musa min ba, zaman kuwa ta yi, ta had'e kanta da guiwoyinta, ga jikarta a ma'kalk'ale da ita, sai nik'ab d'inta a d'ayan hannunta.
Dama na bata sosai ta samu natsuwa, har sanda aka kira sallah na zuba mata ruwa a buta, ta tashi ta gabatar da sallar.
A dai-dai gamawarta Mallam ya dawo, bayan ya