Showing 54001 words to 57000 words out of 217237 words

Chapter 19 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

185

ta bashi tausayi, ya san da ace tare take da mahaifiyarta ko mahaifinta ba zai su tafi su barta ba ko kuma su yi saken da zata bata, risinawa yai yana kallon fuskarsa.

“Miye sunanki”

“Namra”

“Wow cute you sunan yata, yanzu za ki iya gane gidan ku?”

Ta girgiza kai alamar no.

“Wace unguwa kike zaune?”

“Yan magurora”

“Gurin wa?”

“Karkar mu”

“Ita ke rikonku?”

Ta gyada masa kai.

“To yanzu kin san yadda za mu yi? Zan saka ki a motata na kai ki gidanmu da safe sai na kai cigiyarki, ko kuma naje unguwarku na nemi nai unguwar na damka masa ke kin yarda”

A take ta gyada kai sai ya rika hannuta ya nufo motarsa da ita ya saka ta shi ma ya zagaya ya shiga.

“Ita Mamanki wane unguwa take?”

“Ban san sunan unguwar ba”

“Ba ki taba zuwa ba?”

“Na taba zuwa sau daya”

“Sau daya?”

Ya tambaya yana kallonta da mamaki sai ta gyada masa kai.

“Miyasa sau daya kawai?”

“Kaka tace mana wanda ta aura baya son yara shiyasa bata tafi da mu ba”

Tabe baki yai yana yi ma motar key.

“Ji wani irin selfishness dan Allah mutum be son yara kuma ka yi aure ka tafi ya bar su, yanzu nan idan ni bana kwarai ba ne shikenan kin fada mugun hannu mtsszzzzzzzzzzzzzzzzz”

Yaja wani dogon tsaki yana jin kamar ace shine uban yarinyar ya ci mutunci uwar, ko da yake shi miyasa uban ma ya bar su hannunta.

“Imagine ayi ta haihuwa bana iya kula da yara ko ba a son dawainiya da su, shi uban baya so ita ma bata so”

Ya fada yana mai jin haushi iyayen duka biyu.

‘Ba ma gidan uban da zan kai ki cigiya, idan suna son ki su nemi ki da kansu’

Wannan karon a zuciyarsa yai maganar. Sannan ya cigaba da tuka motar, abun da yaro ta man ta sha kuka ta koshi kamin ya isa gida har ta yi bachi. After yayi farkin ya zagayo ya bude motar yana kokarin daukarta ya dora a kafadarsa ta farka, sai dai hakan be hana shi daukarta ba ya nufi cikin gidan da ita, kamin ya karasa Baby Namra ta fito daga falon tana masa oyoyo.

“Daddy sannu da zuwa”

“Yauwa Baby”

Ya fada yana shafa kansa da dayan hannunsa tare da murmushi.

“Daddy wacece wannan?”

Ta tambaya tana kallonsa be amsa mata ba sai da ya shiga falon Hajiya ya sauke Namra saman kujera.

“Je ki kawo mata ruwa ta sha, kawa na samo miki”

Sai ta bata fuska.

“Ni Allah ya tsare ni ba kawata ce ba”

Ta fada tana nufar hanyar kitchen, shi kuma yai murmushi yana kallon Namra wacce ta takure guri daya kamar mai jin tsoro, shi sai yanzu yake ganin kamar ma ya taba ganinta.

“Ina ka samo ya?”

Hajiya da ke tsaye upstairs tana latsa waya ta tambaya daga can inda take tsaye tana kallonsa.

“Wasu mahaukatan iyaye ne da ba su san darajar yaya ba suka jefar da ita”

“Jefarwa kuma?”

Hajiya ta tambaya tana saukowa daga stairs din.

“Yes”

Ya amsa mata yana maida dubansa gurin Baby Namra wacce ta fito kitchen rike da kofin ruwan.


*Khadija Abubakar Alkali*
7/20/21, 8:33 AM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


1️⃣9️⃣

Labarin GOBE NA ba labari irin wanda na saba yi ba, shiyasa tun kamin na fara sakinsa na fada muku cewar rayuwar aure ce mai cike da kalubale, idan ba ku manta ba inkiyar labarin ZAWARCIN HALIMATU, labari ne na rayuwar kala kala ta gidan aure da zawarci, da kuma rikon yara da kula da tarbiyarsu, zancen dan Allah Candy kar ayi kaza ko ki canja kaza be taso ba, matukar ana son labarin ya tafi a yadda aka tsara kuma a isar da sakon da ake son isarwa.

GOBE NA ba labarine na zallar soyayya ba, yana tafe ne da kalubalen na rayuwa, duk irin halin da Halimatu take ciki ko zata kasance a ciki akwai mata da yawa da suka dade da shiga cikin wannan halin, ko suka fita shiga matsala ma. Wallahi a three weeks ago akwai wacce ta kirani tana kuka tana fada min abunda akai wa Namra a labarin haka akai wa yarta kuma har yau babu wanda ya sani mijinta ya hanata magana, secondly mijinta kamar Aminu yake, a lokacin da ta ba ni labarin mijinta sai da kaina ya daure Wallahi. So akwai mata da yawa da suke fuskantar rayuwar gida aure kala kala, ko da ba mu tabo duka ba ya kamata ace muna taba wani bangaren na rayuwarmu ta yau da kullum ai.

Labarin zai tafi a yadda na tsara shi ga wanda yaji zai iya bi fine.


*** *** ***

“Aa Gwarzo wace uwar ce zata jefar da yarta haka nan kawai? Ka taba ganin bolar yaya?”

Momy ta fada bayan ta zauna tana kallon Namra.

“Oh Momy ba ki ji inda na samo ta ba, uwarta na son ta zata jefar da ita”

“Idan ma haka ne ai ba laifi uwar ba ne, na uban ne akan me zaka bar yarinya na tsawon lokaci ba ka neme su ba? Taya ma zaka bar ma mace dawainiyar yara bayan ba da su ta zo ba?”

“Ita na fa uwar da laifinta”

“Baka san abunda ya fito da ita daga gidan mijin ba, ba duk mace ce bata son yaranta ba ni ban yarda akwai mace da bata son yaranta ba, wata kila ma hankalinta yana can tashe”

“Ko dai zan maida ita sai gobe sai jikinsu ya fada musu, ko goben ma sai da maraice”

Ya fada yana shafa kan Namra.

“Yarinya kyakkyawa suna son wufintar da ita”

Momy ta yi murmushi.

“Ya sunanki?”

“Namra”

Ta amsa hankalinta kwance kamar ta san su.

“Allah sarki Baby Namra kin samu takwara”

Baby Namra dai bata komai ba sai wani shigewa take jikin Momy.

“Sai gobe zan bada cigiyarta a radio idan sun ga dama su zo nan su dauke ta”

Ya fada yana mikewa tsaye. Sai ita Namra ta mike tsaye zata bi shi.

“Zauna nan Momy zata kula da ke”

Momy ta mika mata hannu tana murmushi.

“Zo nan jikata yar albarka”

Ba musu taje ta zauna saman kujerar sai Momy ta dorata a kafafuwanta.

“Ajikin nawa?”

“Uku”

“Wace makaranta kike?”

“Gwarzo International school”

Momy ta yi dariya, Ahmad ma da ke kokarin fita juyowa yai ya kalleta.

“Wow i feel it tun farko na ji kamar ina da alaka da ita, ashe yarinya yar makarantar mu ce shiyasa take da natsuwa”

Ya fada yana wani miskilin murmushi. Momy dai ta girgiza kai tana kwantar da Namra a ciyarta.

“Idan kuma iyayenki sun ba mu ke sai mu rike abar mu mun kara samun wata daman ina son yara”

“Da gaske?”

Namra ta tambaya Momy ta gyada mata kai.



HALIMATU POV.

Ban samu wani sakewa da ya kamata ko wace matar da ta yi a gidan uwar mijinta ba, saboda ban ga fuskar Hajiya ba, kamar wata bakuwa haka na zama a cikin gidan.
Har aka kira azahar babu komai a zuciyata sai tunanin dalilin tsanar da Hajiya tai min daga auren dan ta zuwa yanzu amman ban samu dalili ba, a iya tunani wanda ya ce yana son naka ya gama da kai ko da kuwa Abdulhamid yana da lafiya kamar kowa ballanta ta san yadda lalurar danta take amman na amince a haka na ce zan zauna da shi a kalla na cancanci girmamawa da ganin mutuncin da kauna daga gareta. Amman ban samu haka ba sai wulakanci da tsana da suka boyo baya bayan a baya kuma ba haka take min ba.
Wata kila kuma jinina ne a haka domin Hajiya ma mahaifiyar Aminu da kanensa basa kaunata saboda gani suke na tare komai na mallake musu dan'uwa wata kila ita ma tana min wannan kallon ne.
Bayan na shiga bandakin tsakar gidan nai alwala na yi sallah a saman dankwalina, ban jira ta ce min na shigo ciki ba,kamar na san ba zata ce na shigo din ba domin ko ruwa bata ba ni ba, abincin rana ma da aka gama kanen Abdulhamid ne suka kawo min.
Ina zaune ina lazimi da hannuna Abdulhamid ya kira cikin sauri na daga kiran domin duk na tsawwala da zaman gidan na yi zaton zai fada min na fito mu tafi ne kamar yadda yace zai dawo ya dauke ni.

“Aiki ya min yawa Haima, sai da la'asar zan zo daukarki”

Bana son na kara zama gidan ko da na minti talati ne a yanzu hakan yasa nai saurin yi masa requesting.

“Ko na tafi gidan su Hajara kamin ka zo? Ba nisa sosai daga nan zuwa can daman tana ta min complain wai ban je gidanta tun da nai aure”

“Bana son ki hau achaba”

“Napep zan hau”

“Okay sai kin dawo”

“Na gode”

Har dakin Hajiya na shiga nai mata sallama ta amsa min ciki ciki, na fito raina babu dadi na nufi gidansu aminiyata Hajara, har ga Allah ban jidadin yadda mahaifiyar mijina take min ba, domin ni mace ce mai son dace da uwar miji yadda yake ganin wasu iyayen mijin suna nunawa surukansu kulawa abun har burgeni yake amman ni na kasa samu a aurena na farin a wannan ma ban dace ba.
Na isa gidan a Napep kamar yadda na fadawa Abdulhamid, sai dai ban jidadin samun mijinta a gidan ba, domin kunyarsa na ke ji tun daga lokacin da ya nuna yana son ya aure. Da sallama na shiga shi ya fara mika min gaisuwa sannan na zauna saman cushion dinta shi kuma ya tashi ya fita.

“Amarya ba kya laifi yau an tuna da mu”

“Kullum ai kina cikin raina”

“Ni ai fushi na ke da ke ni da nai miki kyautar miji sukutun kika gujemu kika kama dan'uwanki”

Ta fada bayan ta dire min kofin ruwa, murmushi nai sai na maida kaina kasa ina kallon carpet dinta.

“Kawata kamar kina cikin damuwa”

Dagowa nai na kalleta ina ta tunani ta ina za ki fara dora mata bayani.

“Ina ciki ba daya ba ma, amman naga kamar Abban Afrah na nan....”

Rufe bakina ke da wuya muka ji tashin motarsa, sai ta tashi ta sakawa kofar key sannan ta dawo kusa da ni ta zauna tana kallona cike da damuwa.

“Ban san wane zan fara fada miki ba, tsanar da mahaifiyar Abdulhamid tai min ko kuma ganin Kabir da nai a titi yana yawo a haukace? Ko fyaden da akai min, ko kuma son yayana da Abdulhamid ba yayi?”

Ina maganar hawaye na sauko min, rikicewa tasa ka ta kasa ce min komai, har na wadansu dakiku.

“Halimatu akai miki fyade ko kuma wanda akai wa Namra kike magana?”

“Ni dai akaiwa”

“How, when? Waya miki fyade?”

“Ban sani ba Hajara shi nake kokarin sani yanzu, kaina gaba daya ya kulle”

“Fada min yaushe abun ya faru?”

Ban boye mata komai ba tun daga a to z ganin ita din ta zama kamar yar'uwata, kuma daman can ina bukatar abokin tattaunawa.

“Amman miyasa kika boye masa Halima? Miye ribar boyewar? Mijinki ne kuma shi aka zo nema da ba a tararda shi ba akai miki haka ai ya kamata ya sani”

“Hajara kina ganin idan na fada masa zai zauna da ni? Ba zai iya zama da ni ba, na ji kuma na gani da yawa akwai matan da suke fansar ran mazajensu a yi mu su fyade saboda kar a kashe mazanjensu daga karshe mazanjen su rabu da su su kasa zama da su, babu namijin da zai ji anyi ma mace fyade tana a gidansa kuma ya cigaba da zama da ita, ballanta Abdulhamid da baya iya komai da mace”

A firgice ta kalleni.

“Kamar ya baya iya komai?”

Tun daga farko nai mata shimfidar labarin har zuwa auren mu.

“Amman Halimatu kin yi wauta, akan mi za ki auri miji kamar wannan? Ba ki san za ki iya jefa rayuwarki cikin hatsari ba?”

“Na riga na raba tun a gidan Aminu yana da lafiya amman sai mu kwashe wata hudu uku har biyar be neme ni ba, shi ma da yake da lafiya na daure balle wannan?”

“Ba daga nan take ba, a can baki da kwanciyar hankali, a nan kuma hankali a kwance yake za ki ci ki koshi dole wata rana ki ji kina bukatar mijinki a kusa da ke, bayan rashin lafiyar na Halimatu mutumen baya son yara kuma kika aureshi a haka, and kin san dan'uwansa yana son ki kuma kika take hakan kika aure shi? Fada min taya mahaifiyarsa zata so ki wata kila ita din ta san dan'uwansa yana son ki amman kika zabi ki auri daya ki bar daya, wanda be dace ki yi haka ba tun daga farko”

Hannu na saka na rufe fuskata ina kuka a hankali.

“Ki fada masa gaskiya na san ba zai gujeki ba, duk namijin da za ayi ma wannan Sadaukarwar ba zai taba gudunki saboda wannan ba, musamman idan yaji cewar shi aka zo nema”

“Idan kuma ba shi aka zo nema ba fa Halima? Idan wanda yai min fyade ya zo ne saboda kawai yai min fyade fa?”

“Akwai wanda kike zargi?”

“Dan'uwansa?”

Ta yi saurin rufe baki tana kallona.

“Ya taba miki maganar banza ne?”

“Be taba ba, amman zoben da na gani a hannun mutumen da ya min fyade yau na ganshi a gurin Abdullah har na kai hannu na dauka ya ce na bashi”

“Amman daman can yana da dabi'ar neman mata ne? Kuma jiya kawai kika gan shi da zobe?”

“Ban san shi da wannan dabi'ar ba, ko a lokacin da yake ta son na kashe aure be taba min maganar banza ba, ni ban taba lura da hannubsa ba balle har na tantace kalar zobensa, amman ba a shaidun mutum kuma yanzu yana ganin na auri dan'uwansa babu yadda zai yi”

Hannu ta kai ta dafa kafadata.

“Ki kyautata masa zato Halimatu ganin zobe kawai ba zai tabbatar da cewar shi din ne ba, ba ayi ma mutum daya zobe kuma idan har shi din ne mi zai saka ya aje zobe a inda za ki gani? Mi ma zai saka ya nemi yi ma matar dan'uwansa fyade? Dan'uwan ma twin brother? Haba Halimatu”

“Zai iya mana ko kin manta abunda Sadi yai ma Namra?”

“Saboda Sadi ya lalata diyar yayansa ba shi yake nufin Abdallah yai ma matar yayansa fyade ba, duk yadda duniya ta lalace akwai na gari, duk kuma yadda duniya take ciki da mutane kirki dole akwai bata gari, karki saka ranki a rudu ki sake janyo wata matsalar a tsakanin yan'uwa, ni yanzu abunda na ke so da ke ki shirya gobe zan zo na rakaki kije asibiti a duba lafiyarki domin irin waennan mutane wani lokacin baka san ko suna dauke da ciwo ba, kuma baki sani ba ko ciki ya shige ki tun da abun ya faru ya kamata kije ayi miki wankin mara”


A take hankalina ya tashi da Hajara ta kawo min maganar ciki, dacan ban kawo hakan a raina ba hankalina ya karkata ne a gurin fyaden kawai ba dan kuma na san bana iya daukar cikin ba, lallai na zama doluwa wani lokacin haka nake abu kamar marar kwakwalwa kuma marar ilmi, tabbas idan nai ciki na shiga uku kuwa.

“Yaushe rabon da ki ga al'adarki? Idan ma akwai cikin ai za ki gane”

“Bana iya ganewa saboda ina wata shida ban yi al'ada ba wani lokacin biyar, idan ina al'ada akai akai sai idan ina shayarwa, shiyasa na ke saurin daukar ciki idan ina shayarwa, amman bana jin wata alama da ke nuna ina da ciki bana jin komai a yanzu”

“Duk da haka muna bukatar zuwa asibiti saboda cire kwankwanta, ai wani cikin sai ya fara girma yake wahalarwa kin manta cikin Adnan? Shi da ma yake cikin farin amman ba ki sha wahala kamar sauran ba?”

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”

Shine abunda nai ta maimaitawa na dafe kaina ina kuka.

“Ki kwantar da hankalinki Halimatu, akwai mata da yawa da aka ketawa haddi ba ke kadai ba, wasu ta dalilin wani abu kalilan, ba ke kadai ce a cikin wannan halin ba, amman shawarar da zan baki ki fadawa mijinki gaskiya idan ma ya zabi rayuwa da ke ai ba akanki farau ba”

“idan na bar wannan gidan auren Hajara ban san ina zan sake shiga ba, ban san wa zan fadawa ba, a can mi zan tarar, idan kuma na zauna zaman gaban iyaye ba dadi da shi ba ko ga budurwa balle a gurin mai yara kamar ni, bana son a fara kirga min aure Aminu ma idab ya samu labari ai zai ce gashi nan har aurena ya mutu tun ba a je ko'ina ba, zaman zawarci ba shi da dadi Hajara dan zaman da nai na iya sakin da Aminu yai min zuwa auren Abdulhamid ban jidadin ba ga natsatsin iyaye, ga lalurar yara tun da mahaifinsu babu ruwansa da su, bana son na fadawa Abdulhamid wannan abun ya sake ni saboda haka, idan ma har na samu cikin zubarwa zan yi a sirrance na cigaba da zama da mijina, ina jindadin Abdulhamid kuma ina son sa bana son shiga wata matsalar a yanzu, idan na fada masa ba lallai ne ya yarda ba, saboda ba ni da wata shaidar, wata kila ma ya zargi cewar na kasa tsare kaina ne na kasa hakuri shiyasa na aikata hakan yanzu kuma nai masa wannan karyar, tun da Allah ya rufe min asiri kara na rufewa kaina ko na samu salama”

Kai ta gyada min tana share hawayenta.

“Hakan yayi idan ma kin samu cikin ki zubar kawai mu rufe wannan sirrin, Allah ya dafa miki ya rufe mana asiri”

Jinginawa nai da kujerarta ina jin zuciyata na wani irin kona marar misaltuwa.
Hajara ta yi ta saka min maganganun na kwantar da hankali da karfafa guiwa a gareni har zuwa lokacin da Abdulhamid ya zo daukarta, ba ni kadai ba shi kansa na lura kamar baya cikin walwala sosai, ni da shi mukai shiru cikin motar kamar wasu kurame ni da abunda nake ta sakawa a zuciyata shi kuma yana ta tukinsa yana kallon titi.

Daf da za mu isa kiran Mama ya shigo wayata, ba tare da tunanin komai ba na danna picking na soma magana cikin muryar da ke karantar damuwarta ga mai saurarenta.

“Hello Mama”

“Halimatu Namra na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login