Showing 159001 words to 162000 words out of 217237 words
gaban mahaifiyar Aminu yayi ne just to make her feel special, wani irin tausayi take ba shi ko kallonta yai sai yaji kamar zai zubar mata da hawaye.
Part dinsa ya nufa a ranar kwana yai da tunani kala kala, sai sake sake yake a ransa. Misalin tara da wani abu ya shiga part din mahaifiyarsa, sai ya same ta a kitchen kamar kullum mai aikinsu kuma na jera abinci a dinning.
“Ina kwana Hajiya”
“An tashi lafiya?”
Ta amsa tana murmushi jinginawa yai jikin kofar kitchen din yana murmushi.
“Al-hamdulillah, Hajiya ba zaki daina wahalar da kanki akan girkin nan ba”
“Na san baka son abincin mai aiki shiyasa nake girka maka da kaina, amman idan kai aure zan huta”
Murmushi yai ya kai hannunsa a kirjinsa yana shafa farar shaddar dake jikinsa.
“Soon In-Sha-Allah”
Da sauri Hajiya ta juyo ta kalleshi.
“Da gaske?”
Ya gyada mata kai.
“Khadija dai?”
Sai ya bar jikin kofar ya nufo inda take yana murmushi.
“Wata ce dai wacce ta cancanci rayuwa mai kyau, wacce ta yanke kauna daga samun jindadi, wacce take bukatar tallafi ita da yayanta da yan'uwanta, wacce zuciyata ta cika da tausayinta”
“Halima ce?”
Hajiya ta tambaya tana murmushin jindadi. Sai ya rumgume ta ta baya ya dora kansa saman wuyanta.
“Hakan nan kawai nake jin kamar idan ba ni na aureta ba, zata iya auren wani ya ci amanarta kuma ta sha wahala, and idan ta auri wani ba ni ba, zai so yayanta? Zai iya taimakonta? Zai jin tausayinta kamar ni? Kin san me take fada min jiya? Wai tana tsoron kar kaddararta ta shafe ni, tsoro rabar mutane take, ina son na cire mata wannan tsoron i want to make her feel special, and duk wani kalami da mahaifiyar mutumen tai jiya da ni take, a tunaninta ina son Halima ne, Idan har ta amince min na aureta, zan aureta ne kawai saboda in tausayinta amman ba dan ina sonta ba”
Ya sake ta ya juyo gabanta ya tsaya.
“And ina son mace mai hakuri kamar ta, the way she talk, yadda take gudanar da rayuwarta da yadda take taka tsantsan everything is perfect i like her, and her name, ke ma kuma naga kamar ta ku zata zo daya”
“Duk macce da ta auri dana ta yi babban dace, and i believe matar na deserve a better life, ban kawo maka zancen ta bane saboda na san baka son bazawara, sai dai na lura jininku ya hadu hankalinku da tunaninku yana kokarin zama daya, zan fi kowa farinciki idan hakan ya tabbata saboda tana burgeni, daga ganinta kasan macece mai hakuri mai tarbiya mai hankali mai natsuwa da yadda da ko wace irin kaddara, irin matar nan duk namijin da ya aureta yayi sa'ar aure, abunda kake kudiri idan alheri a tsakaninku ina rokon Allah ya tabbatar”
“Amin Hajiya”
Ya amsa yana murmushi, har ga Allah shi dai kam ba son Halima yake ba, domin tuna tayi aure har biyu ga fyade yana bata masa rai, dukan wani abu da zai mata na tausayi ne kawai da kuma gudun halin da zata fada nan gaba, and the way ta Hajiya take son yai aure zai sake cika mata burinta na auren, sai dai yana jin inda har zai yi auren so Halima ce macen da tafi cancanta ya aura, ko ba komai ita kadai zata iya hakurin zaman da Hajiya, kuma a yadda ya lura da Hajiya tana son ta tan tausayinta ba zata cutar da ita kamar sauran matan ba.
AMINU POV.
Ko da suka isa har an fito da shi, sun zuba shi nan jikin wani siminti fuskarsa duk ta kumbura jikinsa ma kana gani kasan ya sha duka, da ido daya yake iya dagawa ya kalli mutane, jin muryar Hajiyarsa yasa shi jin sanyi, dacan kam ya dauka ko kashe shi za su yi. Hajiya da kuka da komai suka dauke shi suka saka shi a motarsa da direban Ahmad ya biyo su da ita, daga barak din suka wuce da shi asibiti, sai da suka kusa isa asibitin sannan Hajiya ta fara Allah ya isa dan can kan kasa daga ido tai ma ta kalli tarin sojijin, domin ba a bar su sun shiga ba sai da Direban ya kira Faruk din ya sanar masa sannan Faruk din ya bada umarnin a zo a tafi da da su ciki.
“Wannan ai zalunci ne, to shi Bazawarin nata soja ne daman”
Kanen mahaifinsa wanda shima sai a yanzu ya samu baki ya fada, babu dai wanda ya amsa shi duk jimamin abun kawai suke. Bama kamar Hajiya da take jin kamar ita aka daka.
“Wallahi duk inda zan shiga sai na shiga sai na ga inda za ayi auren nan, bakar azzalumar mata, da shegen bazawarin nata daman can ba son shi take da alheri ba, wannan bakin zalincin wallahi Allah ya saka muna”
Riri Hajiya take kuka tana jin kamar ace sun fi Ahmad arziki da iko da sai ta saka an wulakanta shi fiye da yadda yai ma danta amman ba dama, tun da sun fisu arziki da komai ma ciki har da sanin darajar dan'adam.
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣0️⃣
TWO MONTHS LATER.....
Alhamdulillah Thumma Al-hamdulillah.
Godiya ce abunda ta cancanci fita daga bakina na yanzu, izuwa ga mahallincina ko da kuwa ina cikin tsananin rayuwa ballantana yanzu da rayuwar ta fara sauya min.
Abubuwa da yawa da ban zata ba daga Ahmad suna ta samu na, ni da shi a yanzu kusan mun zama abokai, yana sake min sosai yana fada min abubuwan da za su kwantar min da hankali, yana dora ni a kowace hanya ta jagoranci.
Ban tana sani haka yake da sakewa da son jama'a ba sai yanzu, a cikin abubuwan da yai minba kamar yadda ya dukufa a nemawa Kabir Lafiya, wanda farinciki ba ni kadai ya saka ba har da yan'uwansa domin na ga hakan a fuskarsu, asibiti aka maida shi suka masa duk wani gwaje gwaje daya kamata, sannan suka dora shi akan magani, duk wani abu da za a kashe masa ko aka kashe masa ta aljihun Ahmad yake fita.
da abun ya ki yi a nan ne suka tura asibitin sokoto wato uduth, tare da yan'uwansa biyu aka je, da kuma matarsa.
Bayan nemawa Kabir lafiya kuma yarana ya saka su a makarantarsa, school bus ke kaisu tana daukosu.
Wani lokacin ina da na kalleshi sai na ji kamar na bude masa zuciyata yaga irin farincikin daya saka ni, idan kuma na tuna abubuwan da suka faru tsakaninmu sai nai dariya, farkon haduwarmu da kuma abubuwan da yai min na cin fuska kamin yanzu, da kuma yadda muke a yanzu sai wani abun ya bani dariya wani kuma ya bani mamaki.
Kamar ko yaushe yau ma na shirya shirin zuwa aikina, cikin bakar abaya kusan abaya tafi yawa a cikin tufafi domin ina jin sakewa sosai idan na saka ta gashi babu ruwanka da wani rike hijab ko gyara gyale.
Ban yi kwalliya ba, hoda ce kawai na shafa bayan mai sai dan turaren da na saka, sannan na shafa dan mai a bakina na dauki bakar jakata na rayata na nufi dakin Mama nai mata sallama, a tsakar gida na samu Inna ita mai mata sai na dawo na kama hanyar zuwa office din rai na fes.
Na samu napep daf da kofar gidanmu ya sauke wasu sai kawai na tsayar da shi na fada masa inda zai kai ni sannan na shiga.
Misalin tara da yan mintuna na isa office din, ko da na shiga na samu komai tsaf kamar kullum, wato masu gyara office din sun gyara shi sai kamshi yake. Jaka na aje a inda na saba ajewa na nufi window ya bude abun mamaki yau Ahmad ya shigo da wuri na hango shi jikin windows sa tsaye hannunsa daya rike da mug dayan kuma a aljihunsa har yana dago min mai kofin alamar gaisuwa. Ni kuma na daga masa hannu ina murmushi sannan na juyo na zauna a kujera na fara aikina.
Knocked akai kamin na ce komai Yunus ya turo kofar office din ya shigo.
“Good morning”
“Morning how are you sir”
“Fine, hope dai baki gaji da ni ba”
Ya fada yana murmushi kamar yadda nima nake mayar masa da murmushin.
“No haba dai Bismillah”
Na fada ina nuna masa gurin da system din take. Yau kusan kwana biyu kenan a office dina yake aikinsa saboda system din da ke office dinsa ta samu matsala kamar yadda ya fada min.
“Yau ma dai kin yi kyau kamar jiya, wai kiye sirrin”
Ya fada yana nufar gurin da System din take yana aje kayan dake hannunsa. Ni kuma sai nai dariya mai sauti.
“Na gode, sirrin aikin kamfaninku ne ka san yana karawa ma'aikatanku kyau da natsuwa”
He was laughing so hard kamar na fadi masa wani abun dariya sosai.
“Oh wow okay zan fadawa mutanen kamfaninku haka kuwa, so that kowa ya rike aikinsa da kyau kar yai laifin da zai saka a koreshi”
Nima dariyar nai.
“Gaskiya ya kamata kam, ko ma an koresu ku makale kar su je”
“Hahaha Haima kenan”
Ya fada yana cigaba da dariyar, wani abu na ji marar dadi ya ratsa zuciyata sakamakon kirana da yai da sunan da Abdulhamid ke kirana da shi. ban sake cewa komai ba na cigaba da aikina, sai jin nai wayata ta yi kara alamar sako, a zato na mtn ne hakan yasa na share wayar ban duba.
“I think this week zan je Abuja In-Sha-Allah”
Na kalleshi.
“Gurin me?”
“Wani aiki ne, kin san can din ma muna da branch, so idan mai gida be je ba dole ni zan je”
“Okay kace zaka leka garin manya kenan”
Dariya yai.
“Kin tana zuwa Abuja?”
“No ni ai ban taba wuce Gusau ba”
“Oh duk wayewar nan taki? Ya kamata ace kin zagaya manyan birane ai”
“To ai ban san kowa ba, kaga ko ai ba zan tashi naje garin da ba dangi ba na zauna”
“Ba dole sai kana da dangi zaka ziyarci gari ba, idan kina da friends ko ma a karan kanki zaki iya zuwa ki huta”
“Hm da dai ace ni namiji ce zanje amman ina mace ai be kamata ba”
“Believe me akwai matan da suke zuwa garin da ba su san kowa ba, wasu idan za su yi birthday haka ko suje bikin friends dinsu”
“Tab ni kam ba zan iya ba, na je garin da ban san kowa ba? Amman masu zuwa birthday a wani garin basa celebration ko? Dan na san ba za su samu masu binsu ba”
“Irin yaran manya haka, ko manyan mata wasu ma ba su tsayawa kansu ba, so suna zuwa da friends dinsu sai a hadu can ayi ta abubuwa wasu har kasar suke bari fa, kuma kin san ba kowa ke celebration din birthday ba, like me ni ma bana bikin birthday amman a ranar zan ci na sha na yi duk abunda na so”
“Nima haka nake yi gaskiya, ban tana bikin birthday ba, ko cake ban tana ci a ranar birthday na ba sai dai na gode Allah nai saka a status shikenan”
“Ni ina ciye ciye gaskiya, kuma zan iya ma mutane abu albarka birthday na, my is 22 December”
“Mine is 4 October”
Ya kalleni.
“O really? That's mean gobe kike birthday kenan?”
Na yi dariya ina gyada masa kai.
“Wow ki ce ke princess ce kenan”
Dariya na sake yi, a raina ina fadin princess sai kace wata yarinya. Wayata ce tai ringing sai da na dauke kaina daga computer sannan na kai hannuna na dauko wayar ganin bakuwar ce yasa ban damu na dauka ba sai kawai na aje wayar a saman tana ringing.
“Ah gaskiya ya kamata ki yi mana celebration”
“Haba wannan kuma ai sai yara”
Na fada ina kallon number kiranta ya sake shigowa. Hannuna kai na dauka na danna picking nakara a kunne.
“Hello Sallamu alaikum”
“Zo office dina yanzu nan”
Yana fadar hakan ya kashe wayar, ko ba a fada min ba na san mai murya, kuma na san duk a kamfanin nan shi kadai ne zai kira haka kai tsaye ya bani umarni, duk da be taba ba, be ma taba kiran wayata ba, and the way da yai maganar kamar yana cikin fushi. Hakan yasa na dan tsorata, a take na fara tunanin abunda nai wanda ba daidai tsakanin jiya zuwa yau, domin hausawa na cewa karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifin da kai, but if i can remember ai dazun da na shigo mun gaisa da shi idan fushi yake da ni ba zai daga min hannu ba, oh maybe wani abun nai ba daidai ba, a take na fara duba sakkwanin mail din wai ko akwai wanda ya kamata na aika masa kuma ban aika ba.
“Ko a kamfanin nan ne ya kamata ki yi mana celebration”
Yunus ya fada yana danna computer dake gabansa yana murmushi, nima murmushin nai na mike tsaye rike da wayata da sai a lokacin na ke ganin sakon da ya turo min.
“Same ni office yanzu”
Oh ashe ba mtn ba ne kenan dazun, na fada a raina sannan na nufi kofar fita ina fadin.
“Ina zuwa Sir”
“Okay”
Ya amsa hankalinsa na gurin abunda yake, cikin faduwar gaba da fargaba na nufi office din kuwa da nasan ban yi wani abun ba, kuma a yadda nake da shi a yanzu bana tunanin akwai wata matsala a tsakaninku, sai muryarsa ta tabbatar min da ba lafiya ba.
Na tura office din na farko na shiga har na gaisa da mutumen dake ciki, haka a na biyu har na kai a nasa office din na tura na shiga bayan na yi knocked.
Ina shiga ya watsa min wata uwar harara, har sai da gabana ya fadi.
“Sai yanzu kika ga damar zuwa?”
“Ban ga sakon ba ne sai yanzu, ina zaki gan shi hankalinki yana can wani guri, me Yunus yake yi a office dinki?”
“Aiki”
“Shi office dinsa kwantarsa ake a ciki?”
“System dinsa ce ta lalace”
“Kuma ba zai iya magana a gyara ba, sai dai ya zo office dinki ya zauna shi tsohon dan iska, ke kuma kin saki jiki sai dariya kike kin kebe da shi kamar wani muharraminki”
The way da yai maganar sai naga kamar ba shi ba, to miye laifi dan Yunus ya zauna a a office dina? Naga dai idan wani abu zamu aikata ai ba za mu bar windows a bude ba, kuma yana maganar Yunus din ba muharramina ba ne shi din muharramina ne da na kebe da shi a nan? I was so so confused.
“Zauna nan”
Ya nuna min kujera, na yi zaton wani abun zan masa dan haka na nufi kujerar na zauna.
“Look at you kuna da exchanging words, mi kuke cewa”
Kallon mamaki nai masa.
“Magana kawai muke”
“Mi yace miki?”
Na yi shiru ina ta tunanin ta inda zan fara, ni kam yaushe rabon da ayi min haka wai a tsareni ana son na fadi wani abu da na fada ko kuma wani ya fada min.
“Maganar zuwa Abuja ne da yai min, sai maganar Birthday, sai.... At first dai cewa yai na yi kyau sai..... Maganganu dai haka... ”
Sama sama na tsakuro abunda zan iya fada na fada masa, domin na lura ba da wasa yake tambaya ba.
“Ji dan Allah kin saki baki kina ta magana da shi har da zancen zuwa Abuja, cewa yai ki bishi ku tafi?”
Na zaro ido ina bude baki.
“A a Wallahi ya za ayi yace haka? Na fada masa ban taba zuwa ba ne, shine muke zancen”
Kamar hadin baki sai ga Yunus din yayi knocked.
“Yes”
Ahmad na bada umarni ya shigo rike da wasu files a hannu, kallo yai ya sakar min murmushi kamin ya karasa gurin Ahmad din yana fadin.
“Tace gobe ne birthday ta shine nace ya kamata tai mana celebration, kuma tace bata taba zuwa Abuja ba, gaskiya ya kamata a turata ko ta hanyar aiki ne taje ta gano Abuja”
It's normal for a friend like Yunus yai magana da friend dinsa like that kamar Ahmad, kuma ban ga wani illa a ciki ba, amman sai Ahmad yai masa banza ya karbi files din kawai ya aje.
“Miya samu System dinka?”
“Wallahi ta tsaya ne gaba daya, ban san abunda ya same ta”
“Kuma ba kai magana ba”
“No na yi magana da Tukur yace min baya gari shiyasa”
“Kuma Tukur ne kawai yake mana gyara a kamfanin nan?”
“No na dai fi yarda da aikinsa”
“Ka dauko wata ka kai office dinka”
“Okay”
Ya amsa sannan ya juya ya fice, yadda Ahmad yake masa maganar kai ka rantse da Allah be san Yunus din ba aiki ne kawai ya hada su, domin yana masa magana ne ta sigar yaro da ubangidansa babu alamar murmushi ko wasa a duka Maganarsa, bayan kuma shi Yunus din ya fada min cewar Ahmad din childhood friend dinsa ne kuma kaf a kamfanin ba shi da aboki irinsa, saboda ya yarda da shi 100%
Haka Ahmad ya zaunar da ni a office din for more than 3 hours, ba dan na masa aikin komai ba, after every 30 minutes sai yaje gurin windows dinsa ya leko sannan ya dawo ya zauna wata kila Yunus din yana can yana aikin ne tun da ya riga ya fara.
Ban san abunda ya zo masa a rai ba sai ganin nai yana kallona yana murmushi.
“I know zaki ce ni din ai ba muharraminki ba ne ko? Yes amman ni ina da karfin jini the way da zan iya controlling kaina akan wasu maganganu ko aikata wani abun ba, ba kowa zai iya haka ba, and ita mace komai shekarunta komai girmanta sai ana controlling dinta saboda karamar kwakwalwa ne da su, more especially Lims”
Ya fada still smile, ni dai ban da idon da na sakar masa babu abunda na ce, har na fara tunanin to ko dai Yunus din dan iska ne?
“Dauko lemu ki sha”
Ya fada yana dora duka kafafuwansa saman katon tebur din, tare da kai yatsansa jikin dogon hancinsa.
“No Na gode”
Sai ya dan tabe baki.
“Kamar kin ji haushi ko? Ke ana tausayinki kin gagara ganewa, by the way likitocin da suke uduth sun bada shawarar a fitar da Kabir india saboda a can ne za a iya masa aiki mai kyau a kwashe jinin daya kwanta a