Showing 165001 words to 168000 words out of 217237 words

Chapter 56 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

214

da kayan.

“On your birthday, I want to remind you that you are special, not only to me but to all those who are privileged enough to know you for the amazing person you are. People like you are hard to come by, but getting to have a woman like you is indeed a gift, People tell me that the best years are still to come. I have to agree with that because my upcoming years will be spent with the world’s most amazing woman.
Happy birthday to someone who improves every life she enters. You always know how to make an impact, but none so strong as the one you made on my heart. I will turn your black and white world into full-blown technicolor. Happy birthday to the leading actress of my life,
If anyone is deserving of all the happiness in the world, it’s you, you are a wonderful mom, a loving woman, and a fantastic human being.

Happy birthday Lims❤️”

Kamar sautin waka haka nake jin ko wane kalami da Hafiza take karantawa a bayyane, wani irin shauki da jindadi naji ya kama ni, ba na kalaman da Ahmad yai min kadai ba har na kyautar da yai min a yau da kuma nuna min ranar haihuwata tana da muhimmanci abunda wani be tana min ba, jin ziciyata tana kokarin alakantuwa da wani abu yasa nai saurin kawarda abun a zuciyata, domin idan har na nace zan sake biyewa kalamai ko wasu abubuwan na koma dakin so to lallai ban dauki darasi akan abunda ya faru da ni ba, domin Aminu ma yana nuna son kamar ba gobe a lokacin da yake nemana, Abdulhamid ma mun yi soyayya da shi a boye kamin daga baya ya dawo min, kuma dukansu ban tsammaci haka daga garesu ba sai gashi sun juya min ba, miyasa shi ma Ahmad din ba zai juya min ba, shi ma ai namiji ne kamar su, ba a gane na gari a fuska ko a aiki har sai an zauna da mutum musamman maza.

“Ke me kike tunani? Ni daman na san wannan rawar kafar da yake son ki yake, ya ga ruwan da ke masa wanka.... Oh wayyo ni inama ace Aminu zai ga wasikar nan yau”

Dan murmushi nai.

“A cikin wasikar kin ji yace yana so? ku rika fahimtar abu mana”

“Ohhh se dis woman, sai ya fito ya furta miki ne? Ai su manyan mutane basa fada maka suna sonka, ke bari ma na fada miki ko zancen basa zuwa sai dai a kai musu mata, yanzu idan ya fara zance da ke sai dai ya aiko mata a dauke ki akai masa ke”

“Oh really?”

“Yes Lims”

Sai duk suka kwashe da dariya, a gurin suka gutsitsira cake din aka cirewa su Namra na su na debi kadan na ci na sha lemun sannan na tashi na shirya na nufi gurin aikina.
  As usual ina shiga na nufi office dina kai tsaye, ina shiga office din gabana yai mugun faduwa, zuciyata ta soma bugawa da karfi kamar zata fito sakamakon arba da nai da Ahmad tsaye jikin tebur dina yana sanye da farar shadda kansa da hula sai kamshin turare yake, rikewa nai na kasa sake daga ido na kalleshi kuma na kasa juya na fita daga office din kamar yadda na kasa karasa ciki.

“Lims shigo mana”

Kamar mai koyon tafiya haka na fara takawa na karasa cikin office din. Har na kai gurin kujerata na zauna ban iya daga ido na kalleshi ba.
Wani dan karamin abu mai kamar akwati ya aje min yan zagaye shi da wani jan zare.

“Happy birthday, kin san on my birthday kin bani kyautar agogon da me ma?”

Ya tambaya yana yatsina fuska kamar da gaske ya manta. Muna hada ido sai ya kanne min ido daya ya sakar min kyakkyawan murmushi, sannan ya juya ya fice yana kokari saka hannayensa aljihu. Murmushi nai haka nan kawai sai na ji farinciki ya cika min zuciyata ya wanzarda nishadi da cikinta. Zaren na fara budewa sannan na bude box din mai kama da box din agogo, domin shi na fi kyautata zaton gani a ciki.
To my surprise sai nai arba da chewing gum, irin wanda na bashi a ranar birthday sa, ban san lokacin da murmushinsa mai sauti ya subuce min ba.







*** **** *****

Kana kallon fuskar Abdallah kasan yana cikin tashin hankali kamar yadda Hajiyarsa ma take ciki, kusan na nashi tashin hankalin ne ke saka shi a damuwa ba kamar na Hajiya wacce ta bi ta gigice saboda batan Abdulhamid, wanda yau kwana uku kenan ba san inda yake ba kuma ba a ji duriyarsa ba, idan kuma aka kira wayarsa bata shiga shi kuma be kira ba, yawancin mutane sun fi kyautata zaton an garkuwa ne suka dauke shi duba da halin da ake ciki a kasar.
Hajiya kuma tana ganin kamar yan yankan kaine suka sace shi, domin idan yan garkuwa ne ba zai kwana har uku a gurinsuba, ba tare da sun kira waya sun fadi abunda suke bukata ba, yayinda dan'uwansa Abdallah kuma yake wani tunanin na dabam.

“Ya dade a nan zaune, yana ta latsa waya can kuma sai ya kalleni yai shiru kamar mai tunani, ashe yana ji a jikinsa”

Hajiya ta fada cikin kuka.

“Yana zaune aka kira sallah isha'i, a gida yai ta be je massallaci ba, har na yi mamaki dan be saba sallah a gida ba ko ta asuba balle isha'i tun tashinsu shi da Husaini ba su saba sallah gida ba saboda Alhaji ya koya musu sallah masallaci, na ce masa ga abinci yace min a a ya koshi na bashi ruwa shayi ya sha, na sa Furera ta hada masa ruwan shayi ya sha, be bar gidan nan ba sai kusan 11pm sannan yai min sai da safe ya tafi, ita ake har yau be dawo ba, kuma ya saba zuwa da safe ya gaishe ni haka da dare kamin ya wuce gida kusan ma nan yake wuni saboda ba shi da mata a yanzu, kuma dan shirye shiryen bikin nan da ake kusan kullum yana nan da shi ake duk wasu shawarwari tun da lokaci ya kusa”

“Allah dai ya bayyana shi a duk inda yake”

Wata dattijiwa dake kusa da Hajiya ta fada fuskarta dauke da damuwa.

“Amin”

Abdallah ya amsa tare da sauran mutanen da suke falon, gaba daya idonsa da hankalinsa yana gurin Mahaifiyarsa.

“An kai report gurin police amman har yanzu shiru”

“Ai wannan abun bana police bane kawai, ya kamata a shiga malamai ayi sadaka Allah ya bayyana shi a duk inda yake, massada babu abunda basa yi gashi ana kusan biki saura wata daya ace babu ango ina lafiya?”

“Amaryar ita ma ai tana can hankalinta tashe ance sai kuka take, ko abinci bata iya ci”

Cewar Hajiya. Hajiya Rukaiya wacce kanwace ga Hajiya ta rausayar da kai cike da tausayawa.

“Wayyo Allah, ai dole Allah dai ya bayyana shi”

A nan ma Abdallah ya sake amsawa da Amin sannan ya mike tsaye.

“Hajiya bari na leka office na dawo”

“To Allah ya tsare ka kai ma”

“Amin, In-Sha-Allahu za a ganshi ki kwatarda hankalinki dan Allah”

Kai kawai ta gyada masa ta Lumshe idonta dake cike da damuwa. Shi kuma ya fice daga falon jiki ba kwari.




__________

Ayi hakuri da wannan 🙏
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


5️⃣2️⃣

Garin daukar cingan din naji na taba wani abu mai kamar karfe, da na ciro cingan din na duba da kyau sai nai arba da makullin mota.
  Ba shiri na mike tsaye ina dubawa duk da bani da motar ina kallon wannan makullin na san cewa na mota ne, wani irin faduwa gabana yai sai an rasa abunda zan yi kuma na kasa yarda cewar makulin motar ne, yana sane ya saka min shi ko? Ko dai ba da gangan yai ba. Maida makullin nai na dauki box din na nufi office dinsa.
  Tsaye na tararda shi jikin fridge ya kafa gorar ruwa a bakinsa yana sha, ganina yasa ya sauke ruwan ya juyo yana kallona.

“Ina....ina tunanin ka yi mantuwa a box din na ga wannan”

Na fada ina budewa na dauko makullin na nuna masa. Sake cika bakinsa yai da ruwan sannan ya aje ruwan ya rufe fridge din.

“No ina sane na saka, na yi ta tunanin abunda zan ba ki as birthday gift, sai na ga babu abunda ya dace a yanzu nai miki kyauta da shi kamar mota, saboda zuwa aikin da kike sai ki huta da hawan napep”

“No i can't accept this”

Na fada ina nufar teburinsa na aje makullin.

“Lims why”

“A'a Halima dan Allah, ranka ya dade kana min abunda ba a cikin dokikin kamfanin nan yake ba, ko da kana taimako ina tunanin kana taimako na ne saboda Allah, ba zan iya karba kyauta mai girma irin wannan ba, bana son alakar mu da wuce haka”

“Why? Kina tsoron an sake shiga rayuwarki? Saboda Aminu ya cuce ki? Abdulhamid ya juya miki baya? Abraham ya yaga rigar mutuncinki? Dukansu maza ne ko ba haka ba? Kina tsoron ki sake komawa wani hali ko? Kina tsoron kar wani yace yana son ki wata rana ya juya miki ba right? Kina da gaskiya kuma kina da hujja kuma dole ayi miki uzuri....”

Ya matsa kusa da ni sosai yana kallon cikin idona.

“Duk abunda nake miki, ina yi ne saboda na ga na faranta miki rai, ba ke kadai kika cancanci farinciki ba, nima na cancanci farincikin, amman na danne nawa na manta da nawa, na danne duk wani bakin rai da damuwa da suke raina, saboda ke na sama miki farinciki, daga lokacin da samu labarinki sai nai kokarin mantawa danawa kin san saboda me? Saboda tausayinki ya cika min zuciya”

Ya kara matsowa daf da ni.

“Dukan abunda nake miki ina yi ne saboda zan iya kuma saboda na fi karfin abun, ba zan taba yi miki wani abu dan kawai ya tambayi so daga gareki ba, zuciyata bata taba raya min na siye soyayya kowa ba, balle kuma ke, ban taba jin cewar nai miki wata kyauta ko wani abun jidadi dan na tambayi soyayyarki da shi ba, Lims ina son shiga rayuwarki na taimake ki na taimaki yayanki da yan'uwanki”

Na yi saurin kaucewa ina aje numfashi.

“Ni ban shiryawa aure ko soyayya a yanzu ba, duka mazan nan da suka yaudare ni babu wanda be nuna min so na gaskiya ba, amman daga baya komai ya canja, kai mai gidanane be kamata alakar mu da wuce haka ba, indan har da gaske taimako na zaka yi to ka taimake ni saboda Allah kawai”

Dayan hannunsa ya saka aljihu, ya juyo yana kallona.

“Ni ma ba zan bari kiyi yanka akan danye ciwo ba, ai baki gama warkewa daga ciwon ba, ke kike kokarin saka kanki a so ba ni ba, na kai ki a restaurant din da nake cin abinci ne har na zaunar da ke a kujerar da kike zargin wani abu ne saboda na yarda da ke, na daukeki yar'uwa ne shiyasa na tura miki sakon cewa I'm not just your friend, na aika miki da sakon birthday ne a gidanku saboda kina daga cikin mutane masu muhimmanci a rayuwata, dukan abunda nake miki saboda kawai ina tausayinki ne kuma ina son ki samu farinciki, idan zan siye soyayyarki ba ta wannan sigar zan biyo ba, shim fada min na taba furta cewar ina son ki? Ko na taba zuwa gidanku da sunan zance? Idan zan nemi aureki a gurin iyayenki zan tafi ba a gurinki ba, domin ni kallon budurwa nake miki yar 18, ba zan yi magana da ke ba har sai da izinin iyayenki, amman abubuwan nan da nake yasa kin fara tunanin son ki nake? Ashe son ki yana da arha da yawa”

Na kasa cewa komai sai hawaye nake, wani irin abu na rashin jindadi da kunya ya baibaye ni, tabbas be furta yana so na ba, amman ya nuna yana kokarin boyewa a yanzu saboda yana ganin kamar ba zan ba shi hadin kai ba, wata kila kuma na yi kuskuren fahimta taya babban mutum mai rufin asiri kamar Ahmad zai ce yana so na? Taya mutumen da ya san wani ya min fyade zai yarda ya zauna da ni? Taya mutumen da samu komai na jindadin rayuwar duniya zai ce yana so na?
      Matsowa ya sake yi kusa da ni ya mikomin tissue.

“Share hawayenki, babu kalmar da na fada dan na bata miki rai, babu kalmar da na fada dan na muzanta ki, ba zan ga wanda zai fada miki wata magana marar dadi ba na saurara masa, ba zan cilasta karbar abunda ba ki da ra'ayi ba, lokaci yayi da ya kamata ace kin samu jindadi rayuwa kin daina kuka, ko akan yara ko akan komai ma, shi nake kokarin nuna miki, ki kwantar da hankalinki ki sake jikinki”

Ya fada cike da nuna damuwar hawayen da nake zubarwa, da kansa ya janyo min kujera ya aje bayana.

“Zauna”

A take na zauna daman jikina ya dade da yin sanyi. Sai ya risina gabana yana kallon fuskata, fuskarsa na dauke da murmushi.

“Fada min gaskiya ko dai ke kike so? Dan kin ga ni kyakkyawa ne?”

Yanayin da kuma sigar da yai min maganar na san ya fada ne kawai dan ya saka ni murmushi, kuma na yi murmushi ina share hawayena.

“A yafe min hawayen nan da na saka kika zubar, seriously bana son naga kina kuka, bana son na ganki cikin damuwa, idan har ba zan iya cireki a ciki ba to be kamata na saka ki a ciki ba”

Ya karasa yana kama kunnesa kamar wani karamin yaro. Sannan ya mike tsaye ya nufi gurin kujerar.

“Idan kina son motar zaki iya dauka, idan kuma ba kya ra'ayi”

Na karasa yana daga kafadunsa alamar hakan be dame shi ba.

“A a na gode”

Na fada sannan na tashi na nufi office dina ina jin nauyi, zuciyata kuma babu dadi, kamar be dace nayi masa maganar ba, idan ma zan maida kyauta ba sai na nuna dan wani abu ya ba ni ba, sai a lokacin ne na ji wata kunyar ta kara baibaiyeni.
Cikin rashin kuzari na zauna na fara aikina ina jin jikina sai a hankali, haka ma rai, juyawa nai na kalli windows dakina dake rufe sai na mike tsaye na karasa gurin ya bude windows din, hangoshi nai tsaye yana kallona fuskarsa ba yabo ba fallasa, kamar kullum hannayensa na zube aljihu. Juyowa nai na dawo na zauna amman na kasa samun natsuwa lokaci zuwa lokaci sai na waiga na kalli windows a duk lokacin da zan kalli windows sai na ganshi tsaye yana kallona.
Tashi nayi naje na rufe windows din sannan na samu natsuwa, bugun zuciyata ya daidaita har na samu damar fitar da numfashi a natse.
Na cigaba da aikina amman sai na nemi natsuwata na rasa gaba daya na kasa tsayarda hankalina guri daya, kuma na rasa dalilin haka, after every two minutes sai na ji gabana ya fadi, ba faduwar gaba irin na tsoro ko fargabar faruwar wani abu ba, faduwar gaba ne irin wanda ban saba jin irinsa ba.
  Misalin sha biyu saura wayata tai ringing, sai na saka hannu a jakata na dauko wayar. Abun mamaki yau Abdullah ne yake kirana, abun ka da mai nema jiki na rawa na dauka ina doka sallama kamar yana gabana, da fari na yi zaton ko zai min murnar birthday na ne tunda na dora a status kuma na san zai gani, amman bayan mun gaisa sai ya bijiro min da wani batun na dabam.

“Abdulhamid ya bata yau kwana uku”

Da mamaki na ce.

“Abdulhamid ya bata kamar ya? Sai kace karamin yaro?”

“Nima ban sani ba, an nemi an rasa wayarsa kuma bata shiga, so na fada miki ne saboda ki kula saboda ina tunanin batansa baya rasa nasaba da Abraham”

“Abraham kuma?”

“Eh Abokinsa ne, so be careful”

Yana fadar hakan be tsaya komai ba ya kashe wayar, mamaki da al'ajab suka rufe ni, daman Abdulhamid yana da alaka da Abraham ne? Amman a cikin babu wanda ya taba nuna min cewar ya san wani, shi kansa Abdallah be tana nuna min haka ba duk kuwa da kasancewar na fada masa komai a game da Abraham din.
  To idan ma Abraham ya saci Abdulhamid me zai masa? Me zai saka ya sace shi? Hakan na nufi Abraham yana da alaka da Abdulhamid kenan shiyasa yai min fyade ko kuma me? Ko kuma shi Abdulhamid din ya san Abraham din ya min fyade? Amman kuma Abraham din ai shi police ne, sai dai a sigar da suka shigo gidan zuwan farko da kuma na biyu duka ta sigar fashi suka shigo, a zuwansa na farko ma ya bukaci kudi kuma ya tambayi ina Abdulhamid yake, ba kowa na sani a abokaninsa ba, amman be taba min labarinsa ba, ko da yake Abdulhamid ba mutum ne mai yawan magana ba dan baya son hayaniya.

Wani tunanin ne ya fado min a rai, ba ni ce kadai a cikin hadari ba har da Ahmad, domin kuwa Abraham yasan da cewar Ahmad ya san sirrinsa, idan har zai iya sace Abdulhamid to ba zai bar Ahmad ba, jiki na rawa na tashi da sauri na nufi office dinsa, domin gaba daya tsoro ya gama kamani, ko da na shiga na tarar yana waya, sai dai ganina yasa yayi saurin yanke wayar ya ta so ya nufo inda nake tsaye.

“Lafiya ya naga hankalinki tashe?”

“Yanzu Abdallah ya kira ni ya fada min wai Abdulhamid ya bata, kuma yana zargin da sa hannun Abraham”

Kansa ya daga kasa ya lumshe ido ya busar da iskar bakinsa sannan ya bude ya kalleni.

“Kin tada min hankali sosai na dauka wani abu ya same ki, to miye naki a batan Abdulhamid din ko Abraham”

“Zai iya cutar da kai, tun da ya san kasan sirrinsa, ko da yana da sanda, a lokacin da suka shigo min ta siffar yan fashi suka shigo min, zai yi maka komai, zai iya kokarin cutar da kai, idan wani abu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login