Showing 75001 words to 78000 words out of 217237 words
Mommy's Boy”
Rahim ya fada yana dariya.
“Ba fa abun dariya ba ne seriously bana jindadin abunda kake min”
“Okay sorry but abun nan yana ba ni dariya”
“Ba abun dariya ba ne, abun nan gaba yake kara yi ba baya ba, na rasa yadda zan bullowa lamarin nan, yanzu fa ta kai har wayata Hajiya ta ke karba ta duba, irin ita bata yarda da ni ba,kullum ganin take kamar yan mata wayo za su min”
Rahim ya kara matsowa kusa da shi ya da fashi.
“Magani kawai kai aure Gwarzo, matukar ba aure kai ba zai Hajiya ba zata daina ganinki a yaro ba”
“Auren ba mafita ba ne, yaure uku nai kamin na auri Halima amman ko wace ta kasa zama da ni sai Halima ita ma kuma saboda ta yi hakuri ne, bayan rasuwarta mace biyu na aura Hajiya bata barin na zauna da mata, tun da idan bata ga dama ba sai ta hana ni cin abincin mace ta ce bata yarda da shi ba, kuma ko yarinyar na nemo idan bata gamsu da ita ba ba zata bar ni na aureta ba”
“Wata mace zaka aura ba yarinya ba, mace mai hakuri da sanin ya kamata, kuma kamin ka aureta ka fara gabatar mata da Hajiya ka fada mata komai na ka karka boye mata, kai idan ta kama ma kai auren a boye kai yi dan samawa kanka mafita, dan Hajiya har yanzu bata daina ganinka a yaro ba, bata yarda ka girma ba”
“Wallahi abunda take min ko Baby Namra albarka, dan yau idan Baby Namra ta ga dama zata iya zuwa wani guri a cikin familymu tace can zata kwana kuma Hajiya ta barta amman ni ban isa ba, abun da Hajiya take min har dauren min kai yake wani lokacin har daure min kai yake”
“Ka samu wata ka aura, irin macen nan da ta saba shan wahalar gidan aure, ka aureta kuma ka fada mata komai karka bi soyayya ka auri yarinya ta zo tai ma Hajiyarka hauka ko ta kasa hakuri da kai, iirin dai mace mai yaya biyu uku aha”
“Kai ba zan iya auren macen da wani ya aura ba, you know ina da kishi sosai, ba zan iya zama macen da wani ya aura ba balle ma wacce tai aure har fiye da daya”
“To ai kaji matsalar ka fi son ka auro yan matan nan na zamani kansu na hayaki dole su ce ba za su zauna da Hajiya ba, ba wai dan kana sonta zata aureta ba, kai ko auren kwangila ne kai kawai da zarar ka samu yancinka gurin Hajiya sai ka rabu da ita ta auro wacce kake so, ya kamata ka amsa sunanka na Gwarzo fa, na san baka daukar rainin kowa a kamfani, idan ka bawa mutum umarni jikinsa har rawa yake ya cika maka aikinka, to ko a gida ya kamata kana motsawa”
“Da Halima na nan da yanzu na amsa, Ba zan taba son wata ba Rahim, ni mijin matacciya ne, na riga na auri Halima kuma na auru, duk mace da zan aura zan aureta ne kawai dan samun mafita amman ba dan kauna ba”
Yayi maganar cikin sanyayyiyar murya, yana sotsa lips din, zuciyarsa na sosuwa da kauna Halimatunsa Uwar Baby Namra.
“Halima ta yi min abunda wata macen bata taba min ba, ta haifa min Baby Namra, ta yi hakurin zama da Hajiya har na tsawon shekara biyu...”
Rahim ya soma lura da yanayin abokinsa, daman ya saba shiga a irin wannan yanayin a duk lokacin da aoa dauko maganar Halimatu, a kokarinsa na kawar da maganar ya dauko masa maganar kamfani.
“Yauwa na manta ban fada maka ba, sun fa turo takardun nan ta mail din kamfani amman sai mun yi printing out....”
Mikewa Ahmad yai tsaye cikin damuwa.
“Dan Allah ka daina maganar wani kamfani a yanzu, lemme go and rest...”
Fita yai daga gurin ya nufi motarsa, yana shiga ya dauki hanyar Exclusive City.
HALIMATU POV.
Na yi kuka iya wanda zan iya, na yi na gaji na rarrashi kaina domin ba ni da mai rarrashina a wannan lokacin. Daya daga cikin waitress din dake gurin ne ya zo yana tambaya idan ina bukatar wani abu?
“Bana bukatar komai, akwai wanda na ke jira ne”
Juyawa yai ya koma gurin da yake tsaye, ya cigaba da danna wayarsa, binsa nai da kallo kamin na ji wata murya mai cike da bacin rai tana min magana.
“Waya aje wannan matar a nan?”
Juyowa nai na kalleshi da kumburarrin idanuwana, mutunen nan ne daya taba ture ni a keke, kuma shi ne wanda na gani a lokacin da naje kai Namra School, kuma shi ne mutumen da ya tsinci Namra. Da saurin waiter din dazun ya zo yana tambayar ba'asi.
“Taya za a bar wata ta zauna a seat din nan? Me ke damunku? Da alama kai bako ne, kuma laifin ba na ku ba ne laifin shugabanku ne, for more than ten years ina biyan kudin gurin nan saboda tsabar rainin hankali yau za ku bar wani ya zauna? Oh haka kuke idan bana nan daman you're very stupid”
Sauran waitress din suka zo suns bashi hakuri, wanda ni ban ga dalilin hakan ba, ko da yake na ji ya ambaci sama da shekara goma yana biyan seat din da alama baya son kowa ya zauna ne.
“Ke dalla malama tashi ki rasa kujerar da za ki zauna sai wannan”
Ko kadan maganarsa bata 6ata min rai ba, da alama macen da yake biyawa kudin kujerar tana da muhimmanci a gareshi, ba kamar ni ba. Mikewa nai tsaye na kalli kujerar sannan na kalleshi na ce.
“Ka yi hakuri ban san cewa kujerar ta ka bace, ban san alakarka da mai seat din ba, mata, yar'uwa, uwa, ko ya ko kanwa, amman ka bata hakuri a madadina, domin ko wacece duniyarta kyakkyawa ce, kuma mai fadi ce shiyasa tai dace da mai kare martabar gurin zamanta ba ma ita din ba”
Hannu na kai na dauki jakata na yi gaba abuna ina jin zuciyata kamar zata fito, na taki sa'a ina kawowa bakin gate din gurin Motar Abdulhamid na kunno kai a harabar gurin, sai da ya faka motar yana kokarin fita na nufi gurin motar na bude na shiga. Ba tare da yace da ni komai ba yai ma motar key muka kama hanyar gida.
__________________
Wai ni kadai na ke hango wani abu?🤔
Bari mu ga masu brain me kuke hangowa? 🤔
Tafdijam 😲 fatar dai kun shirya tafiyar domin yanzu aka fara..... 😊
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣6️⃣
Na yi mamakin ganin kawata Sa'adatu tana jirana a farkon shiga falona, ko wa nuna mata gidana ma oho ni har na manta da ita a cikin duniyar nan. Tun kam Abdulhamid ya faka motarsa ta mike tsaye tana ta kallon motarmu. Har ya faka motar ya bude ya fita be ce mim komai ba kamar yadda nima ban ce masa ba tun bayan shigowa a motar.
Irin kallon nan da ta saba na yan bariki ta fara yi min kamin ta mikawa Abdulhamid shi tare da gaisuwa. Shi kuma ya amsa mata da fuskarsa ta rashin sakewa da mutane, ma'ana ba yabo ba fallasa ba kamar Aminu ba da idan ya ganta bakinsa har rawa yake wajen amsa mata gaisuwa.
“Wa nake ganin kamar Sa'adatu?”
“Ba kamar ba ce ni dince, tun da kin yadani ni ai na nemo ki”
Na yi dariya kamar yadda ita ma tai tana bin Abdulhamid da kallo har ya shige falon sannan ta kalleni.
“Shine angon na mu?”
“Eh shine”
Sai ta tabe baki har da wani lumshe ido ta bude.
“No wonder ake mana rowarsa, ashe kyakkyawa ne mai naira, gaskiya Halima kina dacen auren maza masu kyau da kudi, ko da yake kina da kyau ne shiyasa, da ni ke da kyaunki da yanzu na ci kudi”
‘Yes ina dacen aure a gidan hutun amman ba dan na hutu ba, sai dan na fuskanci wani kabulen’
Na fada a raina a fili kuma sai nai dariya na ce.
“A takaice dai mijina ya burge ki, gashi kuma shi ba kamar Aminu ba ne balle ku kulla”
Kallon rashin fahimta tai min tana yar dariya kamar ta ji kunya.
“Ban gane ba?”
“To ya za'ayi ki gane kuwa? Ke dai zo muje ciki”
Ina gaba tana biye da ni a baya har muka shiga falo. A kujerar da ke kusada kofar ta zauna ta zubawa Abdulhamid ido ni kuma na nufi two seater da yake zaune yana lasa waya na zauna a kusa shi, kamar wanda wani abun ki ya zauna kusa da shi haka yai saurin tashi ya nufi dakinsa, iyakar kokarin da nai na danne damuwar da na ji ne dan kar Sa'adatu ta zargi wani abu. Na tashi na shiga kitchen na dauko mata ruwa da lemun mu na hausa na kawo mata. Sai gashi ya sauko ko inda nake be kalla ba ya nufi kofa ya fice a uzurce.
“Halimatu wane irin zama kike da mijinki?”
Kamar daga sama na ji tambayar Sa'adatu tana mire baki.
“Kamar ya?”
“Ato kin san ni bakina baya shiru, na ga kamar akwai yar matsala a tsakaninku ko kuma shi haka rayuwarsa take?”
“Wai Sa'adatu sakin fuska yasa raini ya shiga tsakaninmu har ta kai kike iya fada min duk abunda ya zo bakin kina mu'amulantata yadda kika ga dama”
Sakin baki tai ganin kamar na taso mata da fada.
“Haba Hajiya ta, makano ne kawai zai shigo gidan nan yace be fahimci akwai rashin jituwa tsakaninki da mijinki ba, kuma wanda ya damu da kai ne ya damu da matsalar ne kawai yake nuna maka damuwarsa, kalle ki Halima Wallahi har kin fi auki a gidan Aminu dama da nan”
“Zuciyarki bata raya miki ko bana da lafiya ba? Babu abunda ya zo kanki sai rashin Jituwa?”
“Hmm yanzu dai Allah ya baki hakuri, mu bar wannan maganar, ya yaranmu ya su Amal?”
“Suna lafiya”
Na amsa mata ina kara hade fuska tare da dauke kai. Shiru ya shiga tsakaninmu kamin ta sake dauko wata maganar.
“Amman wai Halimatu ba kya kewar yayanki? Na ga Aminu ma da ke damu da yaya ba, yanzu yana ta shiga damuwar rashinku balle ke da kike tare da su kullum”
“Ke da kike iya barin Salim da Yusura kina zuwa wani gurin, ba tare da sanin irin kulawar da za a basu ba kika tafi hankalinki kwance har wani gari, balle ni da a gari daya ne kuma bautar Allah zan yi?”
“Ba ki gane ba ne, ni ai tafiyar kwana biyu ce ko uku, idan na dade na yi sati ke kuma aure ne fa, kin san wani lokacin baka sanin darajar abu sai idan baya kusa da kai kamar yadda Aminu yake a yanzu karki so ganin yadda ya koma abun tausayi duk inda ya zauna sai zancenki yake da na yaransa”
“Idan abu yana da muhimmanci a gurinka baka taba yarda ka rasa shi, tattalinsa kake, kana Ala ala kar ya subuce maka, domin duk ranar da ka rasa abun nan ka rasa shi kenan har abada, be kamata ki kawo min zancen wani namijin ba a gidan mijina, na dade da mantawa da Aminu ko wani abun daya shafe shi, ko da wasa karki sake min maganar Aminu”
“Ai na san Aminu ya kuntata miki amman Wallahi Halimatu yana cikin damuwar rashinki a yanzu, matar da ya aura ma ta rasa gane kansa”
“Wai Aminun ne ya turo ki yace ki zo ki fada min yana cikin matsala?”
Ta dan wara ido.
“Ahhh ni ina na ga Aminu da har zai ce min haka”
“Za ki gansa mana ke ai falkalsa ce, za ki iya sanin halin da yake ciki ko ma ya fada miki da kansa”
“Subhanallahi Haba Halimatu wannan bawa irin magana ce, na san dai ina raba wasu mazan, amman taya za ayi na raba mijinki Fisabilillahi, ni ba zan iya wannan cin amanar ba”
“Shiyasa a kike biyarsa kuna zuwa har wani garin kuna kwana, ke fa san komai da ke tsakaninki da Aminu, na samu ido ne kawai saboda na bar ku da Allah, shiyasa na tattara lamarinku na aje gefe, ba Aminu ba ko mai sunansa bana son ji yanzu balle shi din da kansa daga ke har shi na tsaneku tashi ki bar min gida”
Da sauri ta mike tsaye jikinta har bari yake.
“Kamar ba Halimar da na sani ba, da alama dai wani ya shiga tsakaninmu”
“Za ki fita ko sai na wulakanta ki”
Daukar jakarta tai ta juya da sauri ta fice tana waigena. Har bakin kofar gate na bita na tsaya sai da na tabbatar ta fice daga gidan sannan na rufe gate din na dawo cike da bacin rai.
A lokacin dana zauna falo sai bacin ran abunda Abdulhamid yai min a gaban Sa'adatu ya tsaya min a rai, yanzu har ta kai Abdulhamid na kyamar zama a kusa da ni kuma ba zai iya boyewa a gaban mutane ba sai ya nuna? To ko dai ina dauke da cutar ne?ko kuma kiyayyar ce tai zurfi har haka a zuciyarsa. Ba yau kadai ba tun daga lokacin da abun nan ya faru na fahimci irin zaman da nake da Abdulhamid sai dai na yau yafi na ko yaushe.
Ba zan iya wannan zaman ba, sai kace an masa dole da ni ko kuma auren kiyayya mu ka yi? Idan har ya zai iya rabu da ni kai tsaye ba to ni zan iya neman rabuwa da shi domin rabuwar ce mafi a'ala a yanzu, zai fi samun natsuwa idan bana kusa da shi kamar yadda ni ma zan fi samun natsuwa idan na san bana tare da shi.
Ba Abdulhamid kadai ba ni inajin idan ma na rabu da shi ba zan sake auren wani namijin ba, domin na fahimcin gaba daya maza basa da kirki kansu kawai suka sani, ina ji a raina da ace ni ce ba zan iya yi ma Abdulhamid haka ba bazan iya rabuwa da shi ko nuna masa damuwa ba.
“Gaba daya mazan duniyar nan ba su da karki, gaba daya kansu kawai suka sani, su auri mace suna wulakantata suna yi mata yadda suka ga dama”
Na furta da karfi ina fashewa da kuka tare da dafe kai.
“Zan nemi saki, dole ne Abdulhamid ya sakeni, kuma ba zan sake aure ba, zan samu wani aikin zan rike yayana na cigaba da kula da su, ba zan sake yarda ciwon da namiji ya kashe ni ba, na gahi hakan nan wahalar ta isa haka...... ”
Wani abu na ji ya taso min ya tsaya min a kahon zuciya ya danne min numfashi, a guje naje na bude freezer na dauko ruwa mai sanyi na sha sannan na samu relief. Ji nai bana bukatar komai sai shan maganina shi kadai na ke sha ya lulani wata duniyar da nake mantawa da komai, gashi kwana biyun da nai ba sha ba har wani abu nake ji a cikin kaina kamar hayaki. Falon na dawo na bude jakata na dauko 2k na saka Hijab din da n cire na shiga bedroom na dauko keys na rufe gidan na nufi chemist din unguwar inda na saba siyen maganin.
AHMAD POV.
“Maganar gaskiya ba ka kyauta ba Gwarzo....”
Yayi saurin taron numfashinsa yana shafa kansa.
“Na sani.... Ni kaina bayan na mata fadan na ji cewar ban yi daidai ba, musamman da bata min tsawa ba kamar yadda nai mata, you know i hate mutum yai min tsawa”
“Ita ai ba laifinta ba ne laifin ma'aikantan gurin ne kuma.... ”
“Kuma What Rahim...? Sai son nanata maganar nan kake yi, i feel like na yi abunda be dace ba hakan be wadatar ba?”
Da mamaki Rahim yake kallon abokin na sa, daman can haka yake wani irin murdaden mutum ne mai wuyar sha'ani, shi ya kawo maganar abunda yai ma Halima, kuma ya fadawa masa be ji dadin yadda yai mata ba and now yana kokarin bleme Rahim akan ya bashi laifinsa.
“Muna magana ka ce you need to rest ka bar nan baka ce min ga gun da zaka je ba, ashe Exclusive City ka nufa, yanzu kuma ina zaune ne ka dawo ka bani labarin abunda ya faru, and now kana son ganin laifina, shiyasa kake samun rashin jituwa da mutanen ka, mutum ko naman jikinsa zai yanka ya baka sai ka ce da biyu yai, Hajiya ce kawai maganinka Wallahi, ba Hajiya ce kadai take saka matanka na guduwa ba Gwarzo Kai kanka matsala ne”
Tsaki yaja ya dauki hularsa ya saka ya fice daga falon yana ciro keys din motarsa a aljihu.
@360 isa gidan Hajiyarsa, as usual sai da ya fara shiga falonsa kamin ya wuce dakinsa, sai dai wannan karon be shiga da yanayin da ya saba ba, idan har bw shiga da sallama ba to zai shiga da far'a fuskarsa a sake sai dai yau babu ko daya. Be ma ankaro da ba kuwar da ke falon ba har sai da ta gaishe shi.
“Ina wuni”
“Lafiya kalau”
Ya amsa mata sannan ya zarce dakin Hajiya kasancewar be same ta a falon ba. A daki ya same ta tana aikin fesa ma jikinta turare da alama wanka tai ko kuma ta saka sabon kaya kamar yadda ya ga kwaliya a fuskarta.
“Gwarzo yanzu nake kokarin kiranka fa?”
Ta fada far'a fal tana aje turaren da ke hannunta.
“Amman dai a lokacin dawowa ta bwyi ba ko?”
“Ba wannan ba ne, ba ka ga bakuwa a falo ba?”
“Na ganta”
“Je ku gaisa”
“Mun gaisa ai”
“Je ku gaisa dai, ai ba irin wacan gaisuwar ba ka kalleta da kyau”
“Eh sai in ji me?”
“Ka ji kana sonta mana”
Kwantawa yai a kan kujerar da ke dakin yana girgiza kai.
“No no no no Hajiya, yanzu kuma ai bata mata na ke ba, ina ni ina mace yanzu”
Wani kallo Hajiya take masa shi kan be ma kula ba sai zuba zance yake.
“Da ma namiji ne sai naje na zauna mu sha fira amman mace a yanzu ni... No lalalalala, na dai namiji ne”
“Mace ta daina baka sha'awa a yanzu”
“Eh mana da ma namiji ne”
“Mazan ke burge ka kenan?”
Dagowa yai ya kalleta ganin ta zuba masa ido yasa ya tashi zaune.
“A'uzubillahi bafa can nake nufi ba, i mean da namiji ne dan'uwan sai mu yi fira”
Ya mike tsaye tare da zuba hannayensa aljihu ya