Showing 150001 words to 153000 words out of 217237 words

Chapter 51 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

180

kunnata, and he press the power button ya kunna wayar. Hoton yaranta hudu a screen din wayar, he found himself smile yana shafa screen din wayar.

“Beautiful kids”

Ya furta yana maida hankalinsa sosai gurin kallon Amal, a zatonsa ita akai wa fyaden tunda ita ce karama marar wayo. He was just imagine if ace shine mahaifinta, ya zai yi wa mutum yana jin aransa zai iya kashe wanda yai wa yarsa haka, but look at them a maimakon ma ya yarda da mahaifiyarsa sai ya karyata ya saketa akan hakan, tunawa yai da lokacin da Namra ta bata har ya tsinceta, yanzu ya gane duka responsibility na yaran akan mahaifiyarsu, shi uban babu ruwansa, zuciyarsa ta cika da tsananin mamaki ashe ana samun useless father like her husband? Wayarta ce tai ringing sunan Abdallah ne rubuce a saman wayar, haka yai ta kallon wayar har tai ringing ta katse be dauka ba, at the end yai deciding ya sake kashe wayar ganin wata Number ma ta sake kira mai sunan Hajara.
Yana kokarin mayardar wayar aljihunsa aka turo kofar dakin aka shigo, wata dattijitowa ce da ba zata gasa 50+ ba, ko tantama babu yasan yar'uwar Halima ce tun da ya aika direba a can gidansu a fada musu ta suma ya kawo ta asibitin kuma wani nata ya zo ya zauna da ita.

“Sallamu alaikum”

Matar ta fada da katon Hijabinta, sai ya amsa mata yana binta da kallo.

“Ke ce?”

“Yayar mahaifiyar Halimatu”

“Alright, ga wayarta aje mata Allah ya sauwake”

Ya fada yana mika mata wayar, ita kuma ta karba tana masa godiya.

“An gode Allah ya saka da alheri ya kara sutura”

“Amin, an kai shi ne?”

“Eh an kai shi gidansa na gaskiya tun dazun”

“Ok”

Juyawa yai ya fice, sai da ya biya ya samu Doc Nura a Office dinsa yana duba wasu marar lafiya, tsaye yai har sai da ya gama.

“Doc zata kai yaushe kamin ta farka?”

“Zata dauki lokaci, tun har bata farka na da aka kawo ta nan, kuma a gida ma kace ai kun saka mata ruwa ko”

“Yes a can din ma bata farka ba”

“Hakan na nufi zuciyarta ba kamar tawa take ba, gaskiya akwai damuwa sosai a zuciyata, irin wannan bugawan zuciyan wani lokacin ya kan so da ajali, kara ma naka idan rai ya bace yana nunawa duk da shi ma mai hadarin ne, amman irin nata yafi naka hadari domin irinta za a cigaba da bata mata ran ne, ba tare da an san tana da wannan ba, idan kuma zuciyarta ta cigaba da buga kamar haka zata iya mutuwa a take, kuma ina tunanin bata shan magani ko?”

“Ban sani ba gaskiya”

Ya amsa zuciyarsa na kara cika da tausayinta.

“To ya kamata a tambaye ta, ko kuma a ga likitanta, yanzu dole sai ta farka zamu iya yin wasu gwaje gwajen, amman jinin zuciyarta yana gudu da karfi fiye da kima wanda hakan matsala ne babba gaskiya, har yanzu da take sume zuciyarta na bugawa fiye da yadda ake son tana bugawa”

“Babu wani abu da zaka iya yi mata Doc i trust you”

“Yeah dole ne sai mun san irin gwaje gwajen da akai mata, kuma tana karkashin shan magani ko a a? Kamin yanzu ya zuciyarta so dole sai ta farka ko kuma idan kasan likitan da ke dubata zaka iya hada ni da shi”

“Ban sani ba, ban san komai akan hakan ba, dole sai ta farka ko kuma wani daga danginta ya fada”

“Yanzu dai best medicine shine a daina bata mata rai ko barinta da damuwa, duk maganin da za a bata zai taimaka mata ne kawai abun yai kasa, amman ba zai iya wakar da ita ba, matukar ba ta daina damuwa ko kuma a daina bata mata rai ba”

“Thank you”

Shine abunda ya fada ya juya zuciyarsa cike da tunani kala kala ya fice daga office din. Harabar asibitin ya fito ya nufi gurin da ya aje motarsa ya shiga yai mata key, ba gida ya jufa kai tsaye ba, family house din su Halimatu ya nufa a gurin yai musu gaisuwa ya kuma shiga har cikin gidan yai ma mahaifiyarta da yan'uwanta gaisuwa. Ko da ya fito unguwar ana Sallah magariba a hanya ya tsaya yai sallah sannan ya karasa gidan Hajiyarsa jikinsa duk a sanyaye, mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna masa da mutuwar nasa mahaifin da kuma matarsa da yarsa, kuma ta tuna masa cewar Hajiya da Siyama ne kawai suka rage masa. A falon Hajiya ya zauna tasa aka kawo masa abincin amman ya kasa kallon abincin ma balle ya ci. Ita kanta mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna mata da mutuwar mijinta mutum mai dattako da taimako.
Haka yai zaune ya zubawa katon tv ido duk da hankalinsa ba a can yake ba.

“Allah yai muka albarka Ahmad kai da Siyama, ya yalwantar zuri'ar Muhammadu ta karkashinku”

“Amin Hajiya”

Ya fada yana dauke kansa daga kallon tv ya kalleta.

“Ina tunanin aika abincin a gidansu What do you think?”

“Hakan na da kyau, a yanzu mai taimaka musu suke nema, Allah dai yai masa rahama”

“Amin, dazun da safe nake ta tunani a raina cewar ya kamata na samu mahaifinta da maganar mutumen nan mai bibiyarta, domin ina tunanin iyayenta ba su sani ba, a gidansu ma bana tunanin akwai wanda ya sani, a tare muka je meeting dazun ina son nai mata maganar ganin mahaifinta, amman duk sai naji ina jin nauyi na kasa yi mata magana, ashe duk lokacin ma ya rasu”

“Allah be kaddarar ganawarku bane, amman wannan yarinyar tana cikin taskon rayuwa, a halin da take ciki kuma wani ya fada mata, Wallahi ta bani tausayi sosai, tana bukatar farinciki ko yaya ne a yanzu”

Be yi kasa a guiwa ba ya labartawa Hajiya abunda Doc Nura ya fada masa.

“Irin wannan mahaifiyar da ace tana da kudi sai ta dauke ta ta kai ta can wata kasar ta huta ta wannan kunci har sai ta samu sauki ta dawo, Allah sarki rayuwa kenan Allah ya yaye mata”

“Amin”

Ya amsa yana sauke ajiyar zuciya.






HALIMATU POV.


Ba zan iya fadar awannin da na dauka a sume ba, dan dai ba a mutuwa a dawo na nace mutuwa nai na dawo, domin komai na dakin ganinsa nake fari tas, ina jin yawun bakina ya kafe, hayaniyar mutanen uku da ke tsaye kaina ma jinta nake kamar wani yare, ina jin suna taba jikin suna soka min abu suna danna zuciyata can kuma suka daga idona, na kusan minti goma shabiyar a haka sannan idanuwana suka fara gani daidai, sai dai jikin babu kuzari ko kadan yawun bakin ma har a yanzu babu su, numfashin ma ina jin kamar baya isata.

“Sannu”

Likitan ya fada, sai na gyada masa kai, ina kallonsa ya sake yi min wata allurar a cikin ruwan dake shiga cikin jikina. Bayan fitar likitocin na fara kokarin tuna abunda ya kawo ni dakin, a take kaina ya saka hawaye suka samu haya, a hankali na juya kaina sai nai arba da inna Lami, hakan ya tabbatar min da mahaifi na rasa kenan, domin da Mama na rasa da Inna Lami ba zata iya zuwa nan ba saboda kukan rashin yar'uwarta uwa daya uba daya.

“Sannu Halimatu Allah ya baki lafiya”

Unkura nai na tashi amman na kasa sai hawaye nake jikin nawa har lokacin babu kuzari.

“Lafiya kalau na fita na bar Baba, miya same shi?”

“Ai baya bata da kadan Halimatu, ciwon ciki ne ya taso masa sai amai ko kamin ayi wani abu yace garinku”

“Da gaske Uba na rasa”

Na fashe da wani irin kuka mai ban tausayi. Ban tana jin irin abunda na ji a yau ba, kamar nai hauka nake ji, kamar nai ihu na dawo da shi, ashe haka yaran da suka rasa iyayensu suke ji? Ashe haka mairaici yake da ciwo, ga ni kenan da nai aure har na haifi yara, ina ga kanena da basu yi auren ba, a take tausayinsu ya kara rufe min zuciya.
Na dade ina kukan duk yadda Inna rai rarashina sai na ji kamar tana kara kura wutar kukan ne, misalin karfe daya aka bani tea na sha sai lemun hausa da aka yanka min, a daren ban sake runtsawa ba har safe.
Duk yadda likitan ya so na sauna har nan da kwana biyu ban nuna masa amincewa ta ba, a dole ya sallame ni bayan ya bani shawarar na sake dawowa nan da kwana biyu domin a duba lafiyata. Ya fada min halin da zuciyata take ciki da kuma irin treatment din nake bukata.

Misalin goma muka baro asibiti tare da Inna, da wasu yan'uwanmu da suka zo dubamu, kamin mu isa gida Mama ta fado min rai, sai duk tsoro ya kamani kar na zo na rasa ta ita tun da tana da hawan jini, tun a napep din nai ta kokarin tsayar da hawayena amman abun ya gagara ashe hawayen mutuwa su suke yin kansu, ina ta ganin kamar idan na isa gida zan yi arba da Baba ne a inda ya saba zama, sautin muryarsa yana ta dawo min a kunne, yadda yake dariya da duk wani hali nasa na kirki zuciyata tana ta janyo min shi. Ban kara tsinkewa ba sai da nai arba da yan karbar gaisuwar a kofar gidanmu, lallai mutuwa babu wanda ba shi da tambonki, a lokacin dana shiga cikin gidan sai kukan kowa ya koma sabo, saboda yadda nake ta nawa kukan, idan na kalli kanena da mahaifiyata da abokiyar zamanta sai na rasa wa zan tausayawa.
Hakika mutuwa bata da dadi, duk wanda ya zo mana gaisuwa sai yai mana nasiha akan hadin kai da son junanmu, an yi ta zuwa mana gaisuwa mutane da yawa wasu har bana ganesu, abunda Abdallah yai min ya kara min son sa sosai a raina, ya nuna min na zama mai karfin zuciya da dakiya, ni ce babba idan kanena sukai ba daidai ba na musu fada kamar yadda zan yi ma yayana, ya kawo abinci mai yawa da kudi. Abdulhamid ma ya saka an kira masa ni yai min gaisuwa, Aminu kam da shi akai zaman uku har aka gama, ranar da akai sadakan ukun mama take fadin cewar Ahmad ya aiko muna da abinci da kudi mai dama kuma ya shigo har cikin gidan yai musu gaisuwa.
A daren ranar Abraham ya ziyarce ni, irin ziyarar da ya saba kawo min a duk lokacin da ya so ganina.
At first fuskata ya fara haskawa da wayarsa.

“Ki yi hakuri, rashin wani ba dadi duk da dai ban rasa kowa ba, amman na san babu dadi can I hug you”

“Na gode”

Na fada ban jira cewarsa ba na jiya na bar masa wajen, a daren ranar sai gidam ya zame mana kamar wani kango, muna ta firar Baba muna kuka, Aisha take cewa kara ni na yi aure na haihu har yaga yayana su ko auren ba su ba, sai naji duk tausayinta ya kara kamani.

Wasa wasa aka dauki sati daya babu Baba Mama da Inna suka shiga takaba, a lokacin ne na kara tabbatar da mutuwarsa, a kowace rana sai na tuna yadda nake zuwa gaishe shi da yadda yake shigowa cikin gida.

Haka na kwashe sati biyu ban leka gurin aikina ba, kowa kuma be leko ni daga can ba, sai dai wata na karewa na ga albashin 67000, maimakon na jidadi sai na ji rashinsa domin na saba a lokacin da nake aiki nakan cire wani abu nai ma Baba da Mama da Inna siyaya.

Washe garin ranar da na ga albashin na shirya na tafi gurin aikina, ban ji kowa ya min gaisuwa ba hakan yana nufin babu wanda ya san da zancen mutuwar kenan, na nufi office dina cikin rashin walwala, sai na samu matar can a ciki wato Zainab, mun gaisa da ita cikin mutuntawa sannan tai min bayani wai oga ne yace ta zauna na wucin gadi har zuwa lokacin da zan dawo.

“Okay”

“Amman ki fara zuwa ki fada masa kin dawo tukuna”

Ba musu na juya na fita daga office din na nufi hanyar da zata sadani da office dinsa, sai na shiga office na farko na shiga na biyu sannan na isa nasa. Ko da na shiga yana zaune jikin kujera yana waya, ganina ya saka ya yanke wayar ya taso da far'ar shi ta wayayin mutane kamar ba Ahmad ba ya tare ni.

“Wow my friend na dauka zaki yi wata fa”

Na yi kasa da kaina.

“Ina kwana ranka ya dade”

“Lfy kalau ya hakuri”

“Al-hamdulillah, na zo office na tararda wata”

“Yeah kin san gurin ba a barinsa hakanan ba kowa, shiyasa muka sakata kamin ki dawo, ina fatar ba mu yi laifi ba”

“Kamfaninka ne kana da dama da yancin da zaka yi duk abunda kake so, ciki har da korata ko canja min gurin”

Na fada muryata na fita so slow.

“Hajiya tace kar na koreki, yanzu ko kin min laifi bana da halin korarki tun da Hajiya ta shiga tsakani, kin shiga ranta sosai kusan kullum zancen ki muke.....”

Na yi murmushi ina murza yatsun hannuna, yatsun nawa ya kalla sannan ya kalli fuskata kamin ya juya zuwa gurin teburinsa.

“Na gode”

Daga can inda yake tsaye ya dago ya kai ya kalleni.

“Da me?”

“Da komai da komai, na gode Allah ya saka da alheri”

“Amin Allah ya bamu hakuri we almost sharing the same journey, yanzu kin fahimci yadda rashin mahaifi yake kamar ni, gashi kece babba duk wanda zai miki magana zai ce ki yi kokarin hada kan yan'uwanki right”

Ya karasa yana murmushi kamin ya cigaba.

“Haka akai ta min sai nake jin kamar an dora min wani nauyi akai, na rika ganin kamar ba gaske ba ne, ina ta ganin kamar idan na shiga gida zan ga Abbah, idan na kalli Hajiya ta bani tausayi haka ma Siyama, yanzu da nai hakuri na dauki nauyin sai abun ya zo kin da sauki, amman fa har yanzu Hajiyata bata yarda na girma ba, idan zan fita zata bani time din dawowa idan na dade zata kirani tace na dawo dare yayi ko rana, babban mutum kamar ni”

Daga ni har shi murmushi muke sai ya tako ya karaso kusa da ni ya miko min tissue, ashe ya lura da hawayen da suka taru a idona.

“Miyasa ba ki koma gurin Doc ba?”

Na yi shiru ban ce komai ba, be kuma be fasa kallona ba, can kuma ya karasa ya dauki wayarsa ya taba sannan ya kalleni.

“Zaki iya zuwa office dinki”

“Na gode”

Na fada sannan na juya na fito daga office dinsa na nufi nawa office din, ko da na shiga matar bata nan, sai na suke jakata na zauna a kujerar ina ta tunanin mahaifina.
Ban yi aikin kamar yadda na saba ba, domin rashin kowa a kusa da ni sai ya kara saka ni cikin damuwa da tunani kala kala ciki har da na rayuwata da kuma Kabir ko yana ina ma yanzu Allah masani.
Misalin biyu da rabi Ahmad ya shigo office dina ganinsa yasa na tashi tsaye.

“Wata takardar nake nema, ta green light company”

A take na fara duba takardun da suke gaban teburin sai kuma nai arba da ita.

“Takardun da kika san zan yi amfani da su ki rika kai min ko kuma ki bawa sakatarena”

“Okay In-Sha-Allah zan kiyaye”

Har na mika masa takardar ya juya nace.

“Ranka ya dade ina son tambaya”

Juyowa yai yana kallona.

“Dan Allah Kabir nake tambaya, wani mahaukaci wanda ya makure ni ka”

Murmushi yai.

“Mutumen da kika ja min ya naushe ni ido kenan”

Nima murmushin nai.

“Kina son ganinsa ne?”

“Eh tun ranar ban sake ganinsa ba”

“Na saka a dauke ke shi ne akai shi gidan mahaukata”

Na ji ba dadi har hakan ya kasa boyu a a fuskata, sai kallonsa nake na rasa abunda zan ce masa. Dawowa yai gaban teburin nawa ya tsaya yana kallona.

“Karki damu, ina son ki samu natsuwa ne sai mu fara processing din nema masa lafiya, tun da naga ciwonsw ya dame ki”

Da sauri na mike tsaye baki sake ina zaro ido.

“Da gaske?”

“Da karya”

Ita ce amsar daya bani ya juya ya fice daga office din yana murmushi.



__________________

Assalamu Alaikum.
Ban yi niyar cewa komai akan littafin nan ba, duk kuwa da irin comments din da nake gani musamman whatsapp, wasu na complain abunda nake ma Halima yayi yawa so so this and that, akwai ma wacce tace min tana kwankwanton imani akan irin halin da nake saka Halima, na ji zafin maganar amman nai mata uzuri saboda ina daukar tana cikin irin mutanen da ke karatu basa daukar darasi burinsu kawai a samu nishadi.
Ina son ku sani idan ma baku sanin ba, idan kuma kun manta na tuna muku tun farkon fara labarin nan sai da na fada cewar ban sani ba ko zai muku dadi ba labari ne na soyayya ba kamar yadda aka saba, labari ne na fadi tashin rayuwa, kalubalen rayuwar da na aure wanda zai tabo wani bangare na rayuwarmu ta yau da kullum.
Duk yadda kike jin dadi Wallahi baki kamo wata ko a farce da jindadi ba, haka duk yadda kika a cikin tsanani baki kai kan akaifar wata shiga kunci rayuwa ba, labarin nan kirkiren labari ne amman ni nasan ba za a rasa wandanda suke rayuwa irin ta Halima ba, domin na ci karo da wasu a lokacin da nake rubutun nan, wani jarabarwarsa kadan ne wani da yawa, kuma kowa da inda Allah yake jarrabarsa. Idan baki cikin matsala wata na ciki, kuma ban cilastawa kowa karantawa ba sai wanda yaji yana ra'ayi, dan haka dan Allah kar wacce ta sake yi min wata magana marar dadi akan rayuwar Halimatu, duk wanda ya sake fada min rashin arziki goma billahil azeem zan fada masa ashiri, ba dole sai rai na so.

And wandanda suka tuna mahaifansu jiya, wasu har da kuka, ina addu'ar Allah ya jikansu, mu kuma ya sa mu cika da imani.

Ameen thumma Ameen.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


4️⃣8️⃣

Tun daga yanayin tafiyata zaka fahimci ina cikin wani irin nishadi marar misaltuwa,  na fito daga cikin gidan na nufo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login