Showing 18001 words to 21000 words out of 217237 words
mutumen nan ba, ba ki fada min ba amman nasan Aminu yace miki yayi tafiya zuwa Kaduna to Wallahi ya tafi tare da kawarki Sa'adatu, Sa'adatu kin san ai kanwar Basira kawata ce ita Basira kawar Sa'adatu ce ita ta fada mata ita kuma Rahila ta fada min, yanzu irin wannan mijin har abun so ne? Irin wannan mijin ABOKIN RAYUWA ne?”
Tsame hannu na yi daga cikin shimkafar da na ke wankewa na sake kallonta na ce.
“Rayuwar da Aminu yake a yanzu bata dame ni ba, shawara nake da zuciyata na rasa abun dauka, maganar su Mama ko kuma kyato hakkin yata, ta wani bangaren gaskiya suke fada, idan na fita rayuwar yayana zata zama abar tausayi, idan kuma na cigaba da zama zan cutarta da kaina, dalili na farko da ya saka Aminu ya fara sakina saboda na yi fada da kanwarsa, na biyun kuma saboda aikina ne yace kar nai na ce sai na yi saboda be dauke min duka hakokina ba, akan hakan ya sake ni daga baya yace ya yarda na dawo na yi aikin, yanzu kuma saki daya ya rage idan ya sake ni babu zancen komawa saboda shika uku ne babu gyara, kuma bana jin zan tana iya auren wani mutun na fito saboda yayana na tsabawa mahallincina, idan har Aminu yai kuskuren rabuwa da ni a yanzu mun rabu kenan har abada ko da kuwa zan rasa duka yayana ne, amman a yanzu da nake cikin igiyar aurena ina kokarin zaba tsakanin auren, rayuwar yayana da kuma Gobena, duk idan auren da zanje duk more jindadi da soyayyar wani mutum da zan yi a gidan wani auren zuciyata tana gurin yayana, idan na bar gidan nan kamin Aminu ya auri wata matar gidan iyayensa zai sai su kuma idan har ya zama saboda fyaden da akai ma Namra na fita tabbas ba za su taba son yayana ba, idan kuma yai aure wace uwar zai auro musu?”
“Amman kina da tabbacin wata rana Aminu zai iya sakinki ko baki masa komai ba? Saboda ya gaji da zama da ke? A lokacin ne sakin zai fi miki zafi fiye da yanzu, zancen ki zabi aurenki akan abunda akai wa namra be ko taso ba, Halima ya kamata ki sani ba Aminu ne kadai mikin aure ba, kuma akwa yara da yawa da suke tashi ba uwa ba uba balle ke da har kina da rai, kar maganar Mama da Inna ta karya miki guiwa”
Kallona ta nake maganganunta na shiga jikina ta ko wace shiga, sai dai har yanzu idan na tuna maganar Mama sai na ji kamar ba zan iya komai ba. Ita ce ta karasa min girkin ni kuma na cigaba da gyaran gidan kaina a kulle, misalin biyar da yan mituna ta tafi gida ni kuma na dauki wayata na kira Hajara. Bugu daya ta dauka sai hayaniyar mutane nake ji sauti na tashi.
“Halima muna gurin biki, ga yarki Amal ta dame ni da kuka wai ita Momy Momy”
Na yi dariya kadan ba dan ina jin dariyar ba.
“To ai ya kamata dai ta dawi gida haka nan tun safe ba bata gan ni ba”
“Da na gama bikin za mu dawo ai In-Sha-Allah ya jikin Namra? Abban su Baby yace kin ce masa bata jindadi na so na shigo kuma dai sai na wuce sai idan na dawo dan nasan kina gurin aiki”
“Eh to sai kun dawo a kula min da yata”
Daga haka na kashe wayar, kamin na aje ta kiran Kabeer ya shigo wayata har na yi kamar ba zan daga ba sai kuma na daga a tunani wata maganar ce.
“Allah yasa ba abunda ya faru tsakaninmu ne ya saka kika ki zuwa aiki ba”
“Bana jindadi ne”
“Subhanallahi kin sha magani?”
“Allah ya sauwake ya baki lafiya, oga Dahiru ma ya tambaye ki dazun sai na ce masa kin ce za ki je ganin wata yau ba za ki samu shigowa ba, ita fatar ban yi laifi ba”
“Ba kai ba na gode”
Kamin ya sake cewa wani abu na kashe wayar, na bar jikin dinning din ina ta tunanin yadda zan fadawa Aminu abunda ya faru, na kyale shi har zuwa lokacin da Mama tace idan ya dawo, anya zan iya haka? Ba zan bar Sadi ya sake daukar min yara daga makaranta ya kai su gidansa, ba ma shi kadai ba ko mijin Hajara ba zan sake yarda ya kai yarana makaranta na ni zan kai su ni zan dauko su, Amal ma ba zata sake zuwa gidan ita kadai ba sai idan tare da ni ne, ba zan sake yarda da kowa akan yarana ba ko da kuwa mahaifinsu ne.
Dole na fara fada masa a matsayinsa na ubansu kamin na dauki wani matakin, ko kuma yin gargadin kar Sadi ya sake dauko min yara daga makaranta, aikin nawa ma ina jin ajewa zan yi na tsaya na kula da yarana. Komawa nai dinning din na zauna na danna Number Abban Namra na aika masa kira, na yi sa'a bugu daya ya daga da far'arsa, ko da ma be daga ba na yanke shawarar aika masa sako.
“Hello ya kai?”
“Komai an yi Aminu, hankalinka kwance kana can tare da wasu matan ka tsare musu hakokinsu mu ka kasa tsare mana namu, mu da Allah ya dora maka, mu da idan ka mana zaka samu lada, tirrr da wannan kazamar rayuwar da kake zina har da matan aure? Duk karuwan garin nan ba su isheka sai ka nemi mai aure! Abunda kake aikatawa yau kaja an aikatawa yarta, ka yi da yar wani an yi da taka ka lalata rayuwar yar wani na lalata taka, ban tana zina ba kullum burina na kare mutuncin kaina da na yayana da na aurena da na iyayena da naka amman kai kullum burinka ka zubar mana da kima, yau saboda abunda ka ke Aminu wani ya yi ma yarka fyade”
Tun da na fara jera masa zancen be ce uffan ba har na kai aya.
“What! Me kike fada? Wa akai wa fyade, uban wa ya taba min ya? Kin je gurin bakin aikinki kin barta hannun wani an lalata ko? Waya sani ma ko can gun aikin kika tafi da ita kika sake ta? Saboda ba ki san zafin haihuwa ba sai son haihuwar kike baki iya zama ki kula da su, to Wallahi idan kin san wani ya taba min ya kamin na dawo ma gidan nan ma ki tattara kayanki ki koma gidanku”
Duk fadan da yake a daukarsa Amal ce aka lalata ganin itace karamar su kuma ita ce marar wayo sosai.
“Wanda ya lalata Namra a jininka yake, wanda kuka fito daki daya da shu uwa daya uba daya, Sadi Aminu Sadi dan'uwanka kanenka shi yai ma Namra fyade...!”
Shiru yai na wasu yan dakiku kamin ya sake yin wata maganar kamar a rikice.
“Kin san abunda kike fadawa kuwa? Sadi fa kika ce? Taya Sadi zai wa Namra fyade? Kuma idan ma an mata uban waye yaja mata? Da kin zauna kin kula da su wani abun zai same su ne? Karya ma kike Sadi ba zai yi ma Namra haka ba akwai dai abunda kike nufi me Sadi zai ji a jikin karamar yarinya? Kuma yata? Wallahi ki yi hankali da igiyar aurenki Halima.... Mace kamar riga take a wuyana”
“Abunda kake ji a jikin wasu matan shi yake ji a jikin yarka, zaka gene ba ni da hankali idan kotu ta kwatar mata yancinta, tirrr da uba irin ka Aminu na yi nadamar aurenka a yau na tsare ka bana kaunarka Aminu, kuma idan ka haihu ga Zainab da Ibrahim ka sake ki a cikin wayar nan Aminu, abunda akai ma yarka be dame ka ba sai wasu maganganun banza! Tirrrr na yi nadamar haihuwar da nai da kai a yau, na gaji da auren yau ka baro garin Kaduna ka zo gusau ka sake saki dari ba daya ba....!”
Na karasa fadar hakan ina buga hannuna da karfi a dinning table din, yarana gaba daya kallona suke har Namra da ke bachi sai da ta farka ta sakar min ido..
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: https://chat.whatsapp.com/EYNw36FV1ttAsmCUnTsXLH
*GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
8️⃣
Ina kallonta sai tausayinta da nawa ya rufe ni, ban san lokacin da na fashe da kuka ba na dafe kaina.
“Kai Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Na fada cikin kuka, sai Adnan ya nufo ni yana fadin.
“Yi hakuri Momy sannu”
A zatonsa ciwon da nake masa ina na na dazun da ma fada masa ban sda lafiya ne yake damuna. A dole na share hawayena na kirkiro murmushi na mike tsaye na nufi inda Namra take.
“Kin tashi?”
“Ya jikin?”
“Bana jin ciwon komai”
Ta fada tana ta kallona da idonta da sukai ja saboda bachi, sai kuma ta kwanto da jikinta jikina.
“Bari na kawo miki wani abun ki ci kinji yar kirki”
Ta gyada min kai sai dai ina sauka mikewa tsaye daga kan kujerar sai ita ma ta sauko ta matsa kusa da ni kamar zata shige cikina.
“Zauna bari na kawo miki”
“A'a Uncle Abdallah yace ya daina bari kina yin nisa da ni duk inda kika je na biki ko da gurin aiki ne idan ba haka ba Baba Sadi zai iya zuwa ya yanke ni saboda na fada”
Kamin nai wata magana Adnan ya nufo inda mike da sauri yan zaro ido.
“Baba Sadi ne zai yanke ki? Mi kika fada”
“Ba komai, zo muje”
Hannunta naja ban bari ta sake cewa komai ba. Na nufi kitchen din da ita.
“A cikin gidan nan wani be isa ya zo ya taba ki ba, ke ba a nan ba ko a wani wajen ne wani be isa ya taba ki ba, ki kwantar da hankalinki kinji yar kirki”
Na fada mata ina kokarin zuba mata abincin, sai ta fara motsa ido.
“Mama ina jin tsoro”
“Ai Baba Sadi be san kin fadi wannan maganar ba, kuma ba fada masa zan yi ba dan haka ki kwantar da hankalinki kinji?”
Ta gyada min kai, a plate na zuba mata abincin sannan na janyo hannunta muka fito falo, zaunar ita nai ina kokarin bata abincin sai ta ce.
“Momy ban wanke baki ba”
“To je ki wanke”
Bata min musu ba ta tashi zuwa cikin dakinsu, daman can Namra ba yarinya ce mai kiriniya da jan magana ba, ko abu yake cinta yana da wahala ta iya fada ga ladabi da hankali kamar ita ce yayar Adnan, duk abunda na saka ta sai ta yi ba musu idan nace daina zata daina, ga jinkai duk abunda ta samu ita dai Momy dai Momy dai. Rashin ji da kiriniya sai Adnan shi da yake babba da Aiman dakr binta sai kuma wannan yar berar nan Amal ita kam fitinar ta tafi ta kowa ga barna komai ta dauka sai ta lalata.
Wayata ce dake kan dinning tai kara, sai na aje plate din a kasa na tashi na nufi inda wayar take, number Abdallah ce har na yi kamar ba zan dauka ba idan sai kuma wata zuciya tace min na dauka wata kila wata maganar ce aka Namra.
“Assalamu Alaikum”
Na masa sallama da sanyayyiyar muryar da ke fassara irin damuwar dake tare da ni, domin bana da wani sauran kuzari a yanzu. Sai da yai shiru for few seconds sannan na amsa min.
“Wa'alaikissalam Halima ya jikin Namra na san ta farka yanzu ko?”
Na gyada kain kamar yana gabana, shi kuma kamar ya san abunda nai sai ya ce.
“Good ki yi hakuri na fada miki magana marar dadi dazun, rai na ne ya bace shiyasa, kuma dan Allah Halima karki saka damuwa a ranki, karki kamar ba zaki iya ba, kina da yan'uwan da zasu iya goya miki baya ki yi komai, karki bar Baba Sadi ya ci bulus”
“Zan aje wayar”
“Okay ki kula da kanki”
Sauke wayar nai ina ta tunanin ranar da Abdallah zai canja, wannan wa'azin ma yana min shi ne saboda ya san idan har na ce zan kwace hakkin yata dole aurena zai mutu, shi kuma abunda ya dade yana jira kenan tun kamin na haifi Namra, ya kwallafa min rai kullum burinsa da addu'arsa aurena dai ya mutu shiyasa yake yawan fada min maganganu marasa dadin ji akan Aminu, ko da yaushe yana fada min be kamata na zauna da shi ba.
Ni kuma ina daukar hakan da son zuciya da kuma son kai irin na bahaushen mutum, taya zaka kwallafawa ranka son matar aure matar wani? Saboda kawai kana da alaka da yan'uwantaka, wani lokacin har haukarsa nake gani domin mutun mai hankali da tunani ba zai yi abunda yake ba.
Ina cikin wannan tunanin na ji an buga kofar falon.
“Shigo”
Na fada domin na san kofar a bude take ban saka mata key ba. Hajara ce ta turo kofar falon ta shigo tana dauke da Amal sai dariya take bakina har kunne, rayuwarta na burni ne ita kan ta yi dacen aure ba kamar ni ba, abu mai wahala ka ganta a cikin damuwa duk wani abun da take bukata a take mijinta yake mata shi sai idan ba shi da hali.
“Ga yarki nan ta ishe ni da kuka daga kawai na taimaka na je da ita biki, sai ka ce na sato ta”
Na mika hannu na karbe ta sai ta ki zuwa sai ita fushi take tana turo baki.
“Yi hakuri Amal kyale Mama Hajara mun bata da ita har da tufafin Afrah aka saka miki iyeee yarinyata ta yi gayu”
Daker ta zo gareni shi ma da kuka, sai na rungume ta ina dariya. Sai dariyar da nake bata hana kawata kuma aminiyata fahimtar ina cikin damuwa ba.
“Halima kamar akwai damuwa ko?”
Dagowa nai na kalleta kamin na ce wani abun Namra ta fito daga dakinsu ta nufo inda nake.
“Momy ina abinci Maman su Salma ina wuni”
Hajara ta amsa mata ni kuma na fada mata inda tuwon yake.
“Ina cikin damuwa Hajara, damuwar da ta fi ta ko da yaushe kuma damuwar da zata dauwama a zuciyata har abada, ko da kuwa yan hukunta Sadi, ban taba jin na tsani Aminu ba sa yanzu, ban taba dana sanin auren Aminu ba sai yanzu, ban taba jin natsani rayuwa ba sai yanzu, ban taba mafarkin ko jin ina son mutuwa a kusa da ni ba kamar yau, Wallahi Hajara ji nake kamar na sha wani abu na mutu na huta, ina ma Allah be hallice ni ba da duk wannan rayuwar ban ganta ba, ita ba bata gan ni ba, da Aminu be aureni ba”
Da hawaye na ke maganar hawayen da ban yi zaton akwai sauransu ba. Cike da tashin hankali take kallona.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Halima me ya same ki haka?”
Ban boye mata komai ba, tun daga zubin farko na fada mata komai ina kuka, ita ma fashewa tai ya kuka ta saka hannunta biyu ta dafe kanta.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Allah ka tsayar mana wannan abun a nan”
Sannan ta dago ta kalleni.
“Ban taba ji uba kamar Aminu ba, taya za ayi ma yarka fyade kuma ka tsaya karyatawa, ai ko ubanka aka ce yayi ma yarka fyade ba zaka karyata ba saboda duniyar yanzu ta lalace, ammn ke yake dorawa laifin? Da ya tsaya ya kula da iyalinsa yadda ya kamata kuma ya tsare mutuncin kansa hakan zai faru ne? Ban taba goyon bayan ki yi ma Aminu komai ba ban taba goyon bayan ki kashe aurenki ba, a kullum ina cikin addu'ar Allah ya karkato miki da mijinki gareki, amman yau kam ba zan goyi bayan ki bar wannan maganar ba, gobe zan je nai magana da Mama zan fahimtar da su abunda kika kasa fahimta, kuma zan tsayawa Namra sai inda karfina ya kare saki ne dai ko? Aminu ya sake ki Abban Afrah zai aureki In-Sha-Allah, ko kin yi lalacewar da kika rasa mijin aure ba zaki rasa nawa ba”
Kallon yar'uwa nake mata ba kawa ko aminiya ba, na san a yadda Hajara ta dauke ni da kuma yadda yake jina zata iya min komai, ko da bana raye balle yanzu da take ganin idona. Sai dai na san abunda ta fada ta fada ne kawai a yanzu saboda ranta a bace yanke, domin ba wata macen da zata yarda mijinta ya auro mata kawarta da amincewarta. Hannuna na kai ya rika hannunta.
“Na gode Hajara kin karfafa min guiwa sosai”
“Wannan abun yayi yawa Halima Aminu yai miki yan'uwansa su rika ganin laifinki kina ganin kin maye komai na dan'uwansu sun dauki kiyayya sun dora miki, yanzu kuma abun ya wuce kanki ya koma har akan yaranki? Ace Kanen mijinki ya kai yana lalata da yaranki? Miyasa be yi da nasa ba sai na ki? Ko naki ne kawai yayan dan'uwansa, kai wannan tashin hankali da me nai kama? Kina cikin jarabawar aure kuma wani ya karo fado miki? Allah ya miki mafita Halima”
“Ameen”
Mun dade muna ta fira da ita tana ta kwantar min da hankali sannan ta tashi na rak har gurin gate ta wuce gidanta ni kuma na dawo cikin. Ina shigowa na shiga kitchen na debowa su Adnan na su tuwon na kawo musu sannan na dauko maganin Namra da ruwa na soma bata. Ina jin lokacin da mota ta tsaya da karfi har na daga labulen windows na leka waje sai na hango Hajiya tare da yayata mata uku wato mahaifiyar Aminu ce da kenensa. Ban ji komai a raina ba domin a yanzu zuciyata a dake kuma na san zuwan nata baya rasa nasaba da fadan da mukai da Aminu a waya dazun wata kila ya fada mata ne. Ashe kuwa na canka a dai dai domin ta shigo falon babu ko sallama tana shigowa cikin falon ta hau fadin.
“Halima mi kika fadawa Aminu a waya?”
Juyowa nai na kalleta na saba sauka na risina har masa na gaisheta idan ta zo gidan ko ni aje ko muka hadu da juna, sai dai yau bana jin zan iya yin haka.
“Hajiya sannu da zuwa”
“Ba sannu da zuwanki na ke so ba, wata magana na ji nake son ki sake maimaita min da bakinki”
“Indai har Aminu ya fada miki, to ba bukatar na sake maimaita miki, iya kar abunda ya kamata ki gane shine ba zan yi