Showing 189001 words to 192000 words out of 217237 words

Chapter 64 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

210

sun tafi Islamiya sai ga Aminu ya sallamo ya shigo cikin gidan, kamin ya karaso falon Mama nai saurin dauko Hijabinta na saka ya rufe jikina sannan na dawo falon na zauna. Ya shigo da sallama na amsa masa ina murmushi kamar ba ni ba. Shi ma murmushin ne kwance a fuskarsa sai dai ba irin murmushin nan na jindadi ba irin murmushin nan mai kamar na dole.

“Ina kwana”

“Lfy kalau”

Ya amsa yana ta kallona kamar be taba ganina ba, a raina na raya cewar da ace Ahmad nan Aminu yake min kallon nan da yanzu wani abun ya faru, ban san lokacin da wani murmushin ya subuce min ba har sai da na ji Aminu na tambayar.

“Me kike yi wa murmushi?”

“Ba komai”

“Na ga alamar dai kina cikin farinciki”

Na yi kasa da kaina ban ce masa komai ba.

“Daman na zo ne na taya murna, na ji abunda ya faru ance kin yi aure jiya, shine nace abun babu gayyata”

“Nima abun ya zo min bazata ne shiyasa”

“To congratulations Allah yasa alheri Allah yasa wanda zai rike ki amana ne”

Yanayin yadda maganar ta fito daga bakinsa kana ji kasan ba dadi ya fade ta ba. Ni dai na amsa da Amin.

“Nima na zo na fada miki ne zan maida Murja”

Kallon Mamaki nai masa.

“Murja da wacce ta ci amanarka?”

“To ya za'ayi? Nima ba amanar wasu na ci ba? Kin mutum mai irin matsala ba ko wace mace yake aure ba, kuma idan nace zan nemi mace mai irin ciwona na aura, ban fallasa sirrina ne kawai, kara dai mu rufawa juna asiri ni da ita mu yi zama na tsakani da Allah”

“Allah yasa hakan shi ya fi alheri”

Na fada cike da tausayawa.

“Amin ina fatar dai yarana ba su san da maganar nan ba”

“Ban fada musu ba, kuma ba zan taba fada musu ba In-Sha-Allah”

“Na gode”

Ya ciro kudin da za su kai 30k ya miko min.

“Ga wannan kwai siye wani abu”

“A a muna da komai”

“Haba dai hakkina ne ai”

Na kai hannuna na karba sai ya sakar min murmushi.

“Ina taya wanda ya aureki murna, hakika ya samu mata mai kawaici, mai hakuri, kuma kyakkyawa”

A yau Aminu da kansa ne yake fadar ina da kawaice abunda be taba fada ba a lokacin da nake gidansa, a yau shi da kansa yake kina da kyakkyawa kyau da ya kasa gani a lokacin da nake kusa da shi.

“Ina fatar mutumen da kika aura zai rike miki yaranki”

“Ka yafe mushi su ne?”

“A irin wannan condition din dole nai nesa nesa da su, kuma kin san masu irin matsalar mu musamman maza ba wani dadewa suke a duniya ba, bana son na mutu na barki da dawainiya, ina son ko da zan mutu at least ace kina samun wanda zai taimaka miki wajen kula da su, maybe ma su ne kadai yayan da Allah zai ba ni a duniya i don't know”

Ya karasa hawaye na cika idonsa.

“Cuta ba mutuwa ba ce Aminu...”

“Tawa ta mutuwa ce Halima, kawai dai ki yi ta saka musu albarka”

Ya mike tsaye.

“I wish you all the best”

“Na gode”

Murmushi yai min as respond sannan ya saka kai ya fice, ni kuma na tashi na nufi dakina na saka kudin a cikin jakata, sannan na fito na fara gyare gyare dakina da dakin Mama daman Aisha ta share dakin Inna.
Da azahar aminiyata Hajara ta shigo gidanmu da murnarta kamar zata cinye ni, wai ita babu abunda yai mata dadi kamar yadda Ahmad yafi dukan mazanjen da na aura rufin asiri, domin da ce wani makaskanci na aura da yanzu makiya sun saka min dariya amman duk wanda yaji ga wanda na aura sai yace hakurin da nai ne Allah yai min wannan sakamakon, ni kan har ta ci ta shude ban ji komai araina ba wai dan Ahmad yana da arziki, wata kila saboda dukiyar tasa bata gabana ne, ni yi mamakin inda ta ji domin ban fada mata ba gashi line ma yana hannun Ahmad balle nace ko kiranta nai, ashe abun har ya fita da goron da aka raba a makota da kuma can family mu wannan ya fada wancan jin babban mutum ne nn da nan maganar ta yadu ita ma gurin wata kawarta tace wacce ita kuma yar'uwarmu ce.

Sai yamma ta tafi gida, bayan Abban Afrah ya zo daukarta da kansa har da shi yake min murna wai ya ji na yi aure Allah ya sa alheri, a wunin ranar na damu matuka da ban ji daga Ahmad ba, duk be wani saba min sosai da kira ba amman a yanzu ai ni matarsa ce ya kamata ace ya kira ya ji tashina, ko da yake line yana can hannunsa kuma ban san uzurinsa ba.
Can da la'asar sai ga Siyama ta shigo gidanmu, sai da ta gaisa da kowa sannan ta bukaci ganina aka fada mata ina dakin Inna, ina zaune a dakin ta shigo sanye da atamfa mayafinta a hannunta tare da jakarta, da sauri ta zo ta rumgume ni.

“Matar Yaya”

Na yi dariya ina dan jin kunyarta sai ta zauna kusa da ni muka gaisa cikin far'a.

“Hajiya tace tana gaishe ki”

“Ina amsawa”

“Yaya yace ya zo na karbi takardar idan kin rubuta”

Sam ni na ma manta da zancen wani rubuta abubuwan da muke bukata sai a yanzu.

“Wallahi ban rubuta na manta”

“Ayyah za ki iya rubutawa a yanzu?”

“Ko kuma mu bari har gobe ko jini saboda ko na rubuta wani abun zan iya mantawa da wani a yanzu”

“Okay to ba matsala”

Ta saka hannunta a jaka ta dauko sabon line ta miko min.

“Ga line yace ki saka zai kira ki”

“Okay lafiya yake”

Na tambaya bayan na karba.

“Lafiya kalau”

Sai ta mike tsaye

“Ni zan tafi in-law Allah ya baki ikon rike min brother na da gaskiya, because yayana yana son ki sosai, Hajiya da ni duka muna son ki Allah yasa kar ki ba mu kunya”

“Allah ya bani ikon kula da ku duka”

Na fada ina murmushi sai ta amsa da amin ta fice rike da makullin motarta. Ban tashi daga inda nake ba na kira Aiman ya dauko min wayata na saka line ciki, ina kunnawa kiransa na shigowata sai nai picking na kara a kunne tare da sallama.

“Tun dazun nake ta kiran line ne ina son ki saka na ji muryarki, ya kike?”

“Ina lafiya, Siyama ta kawo min shi yanzu nan”

“Na sani kin bata list din”

Yanayin yadda yake amsa min kamar a wahale, ni kuma na amsa masa cikin sanyi jikina.

“Aa na manta ban rubuta ba sai gobe”

“Ba ki da matsala Queen, za mu yi waya anjima”

Daga haka ya kashe wayar.




ABDALLAH POV.

Har a yanzu bana ganin laifin Halima a iya abunda yake gani Ahmad kamar ya mata cilas ne tun da gashi abun daga sama suka ji daurin auren.
Zai iya rasa komai ya hakura ban da Halima, in his own life ya san Halima ba son Ahmad take ba, kuma yana ganin Ahmad kamar ba zai iya rike Halima da gaskiya.
Duk kuwa da irin kirarin da mahaifiyarsa take na cewar wai daman can Halima haka take so ta bata alakar da ke tsakaninsa da dan'uwansa yanzu kuma ta hana dan'uwansa aure kuma ita ta yi aurenta, a yanzu babu abunda Hajiya bata sani ba na abunda Abdulhamid ya aikata da alakarsu da Ahmad amman saboda bakar kiyayay ta kasa daina ganin laifin Halima, a ganinta ai saboda ita asirin Abdulhamid din ya tonu gashi ta kassarasa masa rayuwa ita ta gyara nata. Abdulhamid ma da Hajiya ta kai masa labarin auren Halima kam yayi farinciki da ba Abdallah da aura ba duk kuwa da ya san Hajiya ba zata bari ba amman auren Abdallah zai fi komai tsaya masa a rai idan har ace haka din ta kasance. Babu abunda yafi yi ma Hajiya ciwo kamar sanin cewa mutunen da Halima ta aura a yanzu yafi yayanta rufi asiri, babu abunda take fata take kuma son ganin kamar lalacewar auren ko kuma Halima ta shiga wani hali. A ranar da za a fara shiga kotu da Abdulhamid da Abraham da wasu mutane hudu babu irin kukan da Hajiya ba tai ba sai ta ji kamar ta hade zuciyata ta mutu dan bakinciki.




AHMAD POV.


A ranar da ya bar gidansu Halima be iya kai kansa gida ba, saboda wani irin azababben ciwo da ya rika jin yana masa yawo a jiki, a dole ya faka motarsa gefen titi ya kira driver din gidansi yace ya zo ya tuka shi. Da suka isa gida sai ya wuce part dinsa ya kwanta yana ta jin abun na masa yawo a cikin jiki sai dai hannunsa ya fi ko'ina yi masa zafi domin yai masa nauyi kuma ya masa kamar an dora shi akan garwashin wuta. Duk yadda yake da juriya da iya dakewa a daren kasa hakuri yai idan yai tsaye ya zauna ya tashi haka yai ta yi har garin Allah ya waye. Da asuba ma kasa sallah asuba yai saboda bala'in ciwon da hannun yake masa, gumi sai ke to masa yake ta ko'ina kamar wanda maciji ya tsara, kamin haske ya dan shigo Hajiya ta shigo part dinsa ganin shi be fito ba har jin yai kamar ba zai rayu ba. Tana ganin halin da danta yake hankalinta yai mugun tashi da taimakon mutanen gidan suka saka shi mota aka nufi asibiti da shi, wani abun mamaki da aka yi kwaje kwaje aka duba hannu ba a same shi da komai ba, amman Ahmad azabar ciwo yake masa sosai idan ya samu sauki sai idan an masa allurar kashe ciwo sannan zai ji abun ya kwanta masa amman ko allurar bachi aka masa baya jin sauki domin ciwon baya bashirin bachi.
Sai dai likitocin sun fada masa yawan yi masa allurar matsala tun da ba aiki za ayi masa ba, hakan yasa shi da kansa ya shirya fita waje ganin likita, ko da wasa be fadawa Hajiya cewar tun daga lokacin daya gaisa da Abdallah abun ya sameshi ba domin baya son tai blamed Lims dinsa, secondly kuma ya hana kowa ya fadawa Halima halin da yake ciki saboda kar hankalinta ya tashe kuma kar canfin da take na cewar duk wanda ya kusance ta sai wani abu ya same shi ya tabbata, yana son ganinta amman ba dama sai dai ya kirata a waya, ko video call be son yi da ita saboda kar ta fahimci halin da yake ciki.



HALIMATU POV.

Wasawasa aka kwashe kwana takwas ban saka Ahmad a ido ba hakan kuma ba karamin damuwata yai ba, domin sai na ji kamar na saba da shi a kullum ne, zai kira ni a waya da safe da rana haka ma da dare amman hakan be wadatar ta da ni ba. Ya aiko an karbi list din duk abunda na rubuta an siyo har ma da wanda ban rubuta ba duk an siyo kuma ba kadan ba da yawa aka siyo wanda zai dauke mu tsawon lokaci muma amfani da shi.
A iya sanina yadda Ahmad yake nuna min kauna kamar ba zai iya kwana biyu be saka ni a ido ba balle kuma yanzu da nake matarsa, amman miyasa ya dauke min kafa tun daga wacan ranar? Ko dai shi ma mahaifiyarsa bata so? Ko kuma wani abun ne? Ina tsaka da tunanin nan wayata tai ringing ganin kiransa ne yasa nai hanzarin dauka.

“Hey Babe na ykk”

“Ina lafiya”

“How are my kids?”

“Suna lafiya”

“Na kira na ji muryarki, kuma na miki albishir cewar Kabir yana ta samun sauki ana tunanin end of this month ma su sallame shi, domin an masa tiyata an kwashe jinin daya taba kwakwalwarsa yanzu sun dora shi akan magani ne”

“Ma-sha-Allah Allah ya saka da alheri”

Na fada cikin rashin far'a kamar ba labarin nake son ji ba, ban san abunda ya hana ni jindadi ko murnar samun lafiyar Kabir ba bayan kuma na dade ina fatar samun haka.

“And... I think gobe ko jibi zan je United Kingdom wato London for some works”

Na y shiru ban ce komai ba, domin ban san abunda zan ce ba gaba daya jikina sai ya ba ni kamar ba lafiya ba.

“Idan akwai abunda kike bukata ki fada min”

“Kai nake bukatar gani Ahmad i need to see you”

Daga can cikin wayar ya jiyo sautin murmushinsa mai kama da dariya.

“Wow i got lucky Matata tana so na da yawa haka nan, idan na dawo zan zo In-Sha-Allah”

“Ba zaka zo mu yi sallama ba?”

“Ba zai yiyu ba ne yanzu haka ina Abuja, daga can zan wuce i'm ban fada miki ba, but karki damu next time tare za mu tafi In-Sha-Allah”

Jin na yi shiru yasa shi cewa.

“Kin ji Baby na? Are you there”

“Allah ya tsare”

“Amin i love you”

Na aje wayar ina ta kallon screen din, idan har da gaske wani aikin ne zai kai shi da sai yaje da ni, ko dai shi ma mahaifiyarsa ta masa katanga da ni ne? Ko ba da amincewarta ya aure ni ba? Tun da akai auren ba ban taba gaisawa da ita ba, ni kam dai ina rashin dace da in-laws, but wait miyasa zan zargi mahaifiyarsa? What if ba shi da lafiya? Domin a duk lokacin da nake waya da shi ina jin muryarsa ba a yadda na saba jinta ba. A take gabana ya fadi hankalina yai mugun tashin da sauri na dauki wayar na aika masa da kira amman haka tai ringing har ta katse be dauka ba.....





__________________

Ina yan Team Kabir kun ji ya fara jin sauki 💃
Jiya wata yar Team din Abdallah tana ta min rankwashi a kai 😢😪
To ai ba san maci tuwo ba sai miya ta kare 😥🙄

*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:10 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


5️⃣9️⃣

Kwance take a dakinta tana kallon windows din dakinta da suke bude, pillow na rumgume a kirjinta babu abunda ke fita daga idonta sai hawaye masu zafi.
  Mai aikinsu ce Hindatu ta turo kofar dakin ta shigo da sallama.

“Assalamu Alaikum, Siyama Hajiya na nemanki”

“Ki ce zan zo”

Ta amsa ta ba tare da ta juyo ta kalleta ba. After like one hour Hajiya ta turo kofar dakin ta shigo.

“Siyama....”

Sai a lokacin ta fara kokarin yin kamar bachi take, hakan yasa Hajiya ta karasa kusa da gadon ta zauna leken fuskarta da hawaye ya gama yi mata kwalliya.

“Miye abun kuka kuma? Me yake damunki?”

Juyowa tai da kyau ta kalli Hajiya wasu hawayen na cika mata ido.

“Hajiya...”

Sai kuma tai shiru ta tashi zaune tana matsar yatsun hannunta.

“Ba ki fito kin ci abinci ba, ko yau ba kya zuwa makarantar ne?”

“Hajiya bana son na sake rasa kowa”

Ta fada cikin hawaye.

“To wa za ku rasa?”

“Ban sani ba, amman yanzu idan ciwo ya kama wani a cikinmu sai na rika ganin kamar zan rasa shi ne, i don't want to be alone....”

Ta fashe da kuka, tana kwantawa jikin Hajiya.

“Babu abunda zai samu yayanki zai samu sauki In-Sha-Allah, ki daina tada hankalinki kin ga nima kina daga min nawa, da kuzari da karfin zuciya da nake da shi sai ki sa ya karye”

“Hajiya ina jin tsoro”

“Ki daina kawai ki yi masa addu'a, ki tashi ki wanke bakinki ki fito ki yi breakfast”

Ta gyada kai tana share hawayenta Hajiya ma ta yi saurin tashi tana tare hawayen da ke son zubo mata, cikin rashin kuzari ta fita daga dakin ba Siyama kadai ba ita kanta abun ya bata tsoro jin cewar ba a ga komai ba kuma gashi yace yana jin ciwo, tun daga lokacin da ciwon ya same shi baya iya komai daga zaune sai tsaye sai kwance wani lokacin kuma ya kan dan zagaya cikin asibitin amman fa sai idan am masa allurar kashe ciwo, ga shi baya wani iya cin abu mai nauyi daga lemu sai ruwa sai tea shi ma can ba a rasa ba, sai dai tana addu'a kuma tana fatar idan an je check up din nan a gano matsalarsa. A dinning din take zaune amman ta kasa taba komai balle ta ci kamar ba ita ta dafa abun karyawar ba, yadda yake fito daga part dinsa ya zo part dinta su karya ko kuma idan ba shi da lokaci sai ya dauki breakfast din ya tafi da shi ko mug ne abunda yafi tsaya mata a rai, yau kusan 7 days yana asibiti mutumen da bata bari yai nisa da ita, and the most saddest part is aurensa aka daura yana cikin farinciki wannan abun ya same shi.
A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta dora hannayenta saman dinning din ta dafe kanta kamin ta kike tsaye ta nufi upstairs dan jin tai bata bukatar cin komai.


HALIMATU POV.

Ba karamin tsoro ne ya kama ni ba, na san ban tana kiran Ahmad ba tun da nake a rayuwata, amman mi zai saka yanzu na kira shi yaki dagawa? Amman ya kamata nai masa uzuri, after like seven minutes a sake gwadawa still be daga ba na sake gwadawa be daga ba haka nai ta yi har kusan 20 miss calls amman be yi picking ba, a lokacin ne fargabana ya karu tsoro ya auri zuciyata na fara sake sake kala kala, ji nai bana da natsuwa kwata kwata a rayuwata jikina ya bani cewar akwai abunda Ahmad yake boye min.
Tashin nai na shiga dakina na canja tufafin jikina na saka wata rigar yadi na dauki medium veil na yafa na saka talkamina na dauki yar purse dita cikin dabara na fice na bar gidan domin na san idan nace zan fadawa Mama zata iya cewa ba zan fita ba tare da izinin mijina ba, tun da ba fada mata zan yi gurinsa zan je ba, ina tafe ina waige waige kar wani dan gidan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login