Showing 114001 words to 117000 words out of 217237 words

Chapter 39 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

195

bar gidan”

Ko jakata ban aje ba na ja kanwata Husna muka nufi asibitin domin an fada min Mama da Aisha suna can sun tafi, haka muka shiga cikin asibitin mukai yawon duniya muka gama ba mu gane inda aka kwantar da Amal ba, daga karshe n yanke shawarar kiran Aminu a kan dole na tambaye shi, shi ma nai ta kiran wayarsa ya ki ya daga har yamma.
Ga shi daga Mama har Aisha babu mai waya balle na kira su, hankali yai mugun tashi, wata zuciyar na ce min naje gidansu Hajiyarsa na tambaya sai kuma na ji kamar ba zan iya zuwa ba, ba hatsarin Amal ne kawai ya daga min hankali ba har da rashin ganin Adnan Aiman Namra da ban yi ba domin ance suna can tare da shi.

“To ko kuma din sun samu hatsarin ne?”

“Waya sanar mishi? Mu dai kar ya kai mana uwa ya halaka”

“Wai ina ka kai min yara ne Aminu.....”

Kamar hadin baki ina rufe baki sai ga kiransa ya shigo a wayata. Da sauri na daga jikin har ba ri yake.

“Ina Amal din ina yarana...”

“Muna nan Royal Hospital tare da su”

Tsakanin akatse kiran wayar da mikewa ta tsaye bana jin ya ci dakika daya ma, cikin sauri na fita cikin gidan na isa titi na hau achaba na nufi asibiti. Sai da na sake kiransa na tambaye shi gurin sannan na karasa, a waje na samu Mama da Hajiyarsa suna zaune kamar abun arziki, Hajiyarsa na ganina ta taso ta tare ni da yar far'arta ni kam ko kula ta ban yi ba na tura dakin na shiga. Daga Aiman har Adnan da Namra da Aminu da kuma Aisha suna cikin dakin, Amal na kwance an saka mata bandeji akai sannan an saka mata wani karfe a baki an kware bakin ga halshenta da dinki.

“Miya same ta me kai mata?”

Na tambaya a tsawace ina kallonsa. Sai ya kalleni a sanyaye ya kasa ce min komai. Sai mahaifiyarsa ce ta amsa min.

“Ya dauko su daga Scul ne yana kokarin tsallaka titi da su sai wani mai Napep ya hade Amal”

“Momi kuma halshenta ya cire yanzu aka dinke mata shi..... ”

Aiman ya karasa mata, ban san lokacin da na kalli Amal ba na sake kallon Aminu ya ce.

“Kaga abunda ka ja min a gurin ya ko? Miya kaika daukar min yara?”

“Mhaifinsu ne ni Halima ki rika tunawa da wannan... ”

Ya fada ido raurau kamar zai fashe da kuka.

“Sai yanzu ka san kai mahaifinsu ne? Sai yanxu kasan su din yayanka ne?....”

“Haba Halimatu”

Mahaifiyarsa ta tari numfashinta sai yai saurin daga mata hannu.

“Barta ta fadi duk abunda take son fada Hajiya...”

Wannan karon nuna shi nai da yatsa.

“Ba fada kawai zan yi ba, gargadin ka zan yi akan yarana? Karka sake kula su ko kallonsu karka sake yi balle har ka dauke zuwa wani gurin karka sake nuna hada jini da ni...”

“Ba zan yi abunda zai jefasu a matsala ba, abunda ya faru kaddara ce wacce ko wane dan'adam be isa ya wuce ta ba, kuma ina son ki rika tunawa cewar har gobe ni mijinki ne domin akwai yaya a tsakanin mu kuma ba a san abunda gaba zata haifar ba..... ”

Taba sanin cewar kiyayya Aminu a zuciya ta kai min makura ba sai a wannan lokacin, tasss na wanke masa fuska da mari, mari daya be min ba har sai da na kara masa na biyu ina kokarin yin na uku Namra ta rike min hannu tana kuka sai ta rumgume Babanta. kasa cewa komai nai na fice daga dakin ina hawayen da ban san na minene ba. Ko da na fito ana ta kiraye kirayen sallah mutane waje kowa harama yake hakan yasa na nufi gurin da aka tanada dan aje motoci na zauna saman wani tebur da wasu maza suka tashi, a lokacin da na zauna sai na saka kaina cikin kafafuwan na rushe da sabon kuka, ji nai an zauna a saman tebur din da nake zaune da sauri na dago kaina na kalli gefena. Abraham ne sanye da blue T-shirt da facing cap black kamar yadda wandonsa yake, ko da wasa be kalli inda nake ba sai raba ido yake yana kallon harabar asibitin, Bluetooth din dake gefen kunnensa na ta balli da jar wuta.

“Mi kike yiwa kuka?”

Kawar dai nai wasu hawayen na sauko min.

“Abubuwa da yawa da yawa da yawa... ”

Na kasa daina fadin da yawa din har sai da ya kalleni.

“Kamar me da me?”

“Ba za su lissafu ba, idan na fita daga wannan na shiga wannan na gaji da rayuwar nan, na rasa yadda zan yi.... ”

Ji nai ya rika hannuna...

“I will be safe in this hand of mine, fada min matsalarki kuma ki fada min wanda ya saka ki a damuwa yanzu nan... I can give you another life..... ”

Kamar an min shocking haka nai saurin fisge hannuna na mikewa tsaye ina kallonsa. Kamar yadda shi ma yake kallona.

“I will take the pain,.... take it away....”

Hannu na saka na share hawayena na nufi inda na fito da sauri na barshi a gurin zaune.





#Team Gwarzo
#Team Aminu
#Team Abdallah
#Team Abdulhamid
#Team Kabir
#Khadeeja Candy
#GOBENA
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


3️⃣7️⃣

ABDALLAH POV.

After ya bar gidansu Halimatu ya koma office, sai dai ya kasa natsuwa da abunda Hajiya ta saka shi ya aikata kuma yana ganin be kyautawa Halimatu ba, yanzu dawainiya za tai mata yawa. Haka dai yai aikin da tunaninta a ransa kamar kullum bayan ya tashi office yai sallah masallacin asibitin sannan ya nufi gidan Hajiyarsa.
  A yau harabar gidan ya tararda ita ta shinfida katuwar tabarma ita da yar aikinta suna ta fira. Kusa da inda suke zaune yai parking sannan ya fito daga cikin motar fuskarsa na nuna alamar akwai damuwa a tare da shi, tun kan ya karaso mai aiki ta miko masa gaisuwa sannan ta tashi ta koma cikin gidan.

“Hajiya sannu da hutawa”

“Yauwa”

Ta amsawa tana kokarin kawarda fuskarta daga damuwarsa, shi kuma ya zauna kusa da ita sosai ya soma mata magana a hankali.

“Hajiya da dai zaki duba maganar”

“Maganar Halimatu ko? Ko gaisawa ba mu gama yi ba za ka dauko min zancenta”

“Wallahi Hajiya tun daga lokacin da kika shaya mana katanga a tsakani sai na shiga cikin damuwa, ba aurenta zan yi ai Hajiya, bayan soyayya akwai tausayinta a zuciyata wanda shine makasodin karuwar soyayyarta a raina, hanani taimakonta da kika yi sai ya jefani cikin damuwa”

“Indai kana neman albarka ka bi umarnina ka huta”

“Amman Hajiya harda yaranta?”

“Har da su....”

Ta amsa masa da karfi alamar ta fusata sosai. Sai yai kasa da kansa, na wani lokacin kamin ya tashi ya saka takalminsa.

“Hajiya zanje gida na huta, a tashi lafiya”

Shine last word dinsa da ita sannan ya nufi motarsa ya shiga, a maimakon ya nufi gidan kamar yadda ya fada sai ya juyarda motarsa zuwa gidan iyayen Halimatu, hakuri yake son ya bata akan abunda ya faru dazun, if ba zai iya taimakonta a yanzu then ba shi da yancin fada mata bakar ji yake kamar yai mata wani aibi, daya bayan daya yake ta tunanin maganganun da yai da ita dazun a lokacin da yaje kai mata takardar transfer dinsu Namra, even if be fada mata bakar magana ya kamata yai mata wata maganar da hankalinta zai kwanta ba wai ya barta a cikin duhu ba za tai ta zarge zarge akansa hakan kuma ba karamin jefata zai yi magana damuwa ba.
  Yana isa ya fita daga motar cike da gwarin guiwa ya nufi cikin gidan, sai da gaisa da kanenta sannan ya nufi dakin Mama.

“Mama bata nan Halimatu ma bata nan sun tafi asibiti”

Ya juyo yana kallon Ramla wacce ke masa maganar.

“Waye ba lafiya?”

“Amal ce aka ce ta samu accident on their way back to school”

“Subhanallahi suna wace asibitin?”

“Royal”

Da sauri ya fice daga gidan be ko tsaya gaisawa da Inna ba, hankalinsa ya tashi sosai a take tausayin Halimatu ya kara kamashi.

“Oh Allah.... ”

Ya furta yana hannunsa na hagu saman kai. Tunanin halin da Halimatu take ciki yake gashi ba shi da halin taimaka mata a yanzu. Ya busar da iskar bakinsa yana girgiza kai.
  Sai ya shiga cikin asibitin sannan ya ciro wayarsa ya kira Halimatu domin sanin a inda suke, a maimakon ya ji muryar Halimatu sai muryar Aisha ta daki dodon kunnensa, itace ta kwantanta masa inda suke ya karasa gurin da kuzarinsa, sai dai yana bude kofar dakin ya shiga idonsa sukai arba da Aminu sai wani rashin jindadi da walwala ya mamaye masa zuciya. Da Mama kawai ya gaisa sai Aisha da ta miko masa da gaisu, ko da wasa be kalli inda Aminu yake ba balle mahaifiyar Aminu da ke binsa da kallo.

“Mama garin haka ya faru?”

“Wallahi suna kokarin tsallaka titi ne wani mai achaba ya kade ta”

“Subhanallahi”

Ya karasa kusa da Amal yana dubata, sai Aiman ya zo ya kama hannunsa yana kiran Uncle. Dan murmushi kadan Abdallah yai masa domin yau babu walwala da far'a a tare da shi, hannu ya kai zai shafa kansa sai Aminu ya kai nasa hannun ya fisgo Aiman yana jin wani irin kishi da kiyayyar Abdallah na taso masa. Da gangan Abdallah yai masa wani shegen kallo na uku saura kwata, kamar zai yi masa dariyar abunda yai sai kuma ya dauke kai ya kalli Mama.

“Allah ya saukewa Mama, ya kamata a saka ido sosai akan yaran nan, a samu wanda zai rika kaisu ya dauko su zai fi....”

“Ba sai ka fada mana ba, can baya da ake kula da su kai kake kula da su ne? Ba yara ba ne mu da zaka fada mana abunda za mu yi”

Aminu ya fada cikin fusata da daga murya. Ko da wasa Abdallah be kalli inda yake ba sai yai kamar be ji abunda yake fada ba, har sai da ya duba agogon hannunsa sannan yai masa wani kallon wulakanci, cikin wata irin isa da jin kai ya zuba hannayensa aljihu yana fadin.

“Magana kake Malam Aminu... Ai ban lura da kai bane Aminu... Ashe kana gurin...”

Maganar Abdallah bata karawa Aminu komai ba sai fusata da kawo zuci kusa har launin idonsa ya canja.

“Ya za ayi ka lura da ni ka shigo hankalinka sama”

Dariya Abdallah yai kamar ba komai sai kuma ya juya ya kalli Hajiya.

“Ikon Allah ashe har da mahaifiyarka ma, Na shigo hankalina yana gurin Amal ne, ka san ni Allah ya saka min son yaya musamnan na Halimatu, to sannu Hajiya”

Ya karasa yana da risinawa kamar da gatse, sannan ya kalli Mama still with murmushi a fuskarsa ya ce.

“Mama zan fita sai na sake dawowo”

Har Aminu ya bude baki ya sake fadar wani abun sai Hajiya tai masa hani da ido, hakan yasa shi hade maganar tare da bacin ransa. Abdallah ya nufi kofar fita yana kallon Aminu fuskarsa da murmushi mugunta.






HALIMATU POV.

Har na yi nisa sai kuma ya juyo na dawo gurin da yake da sauri, ban same shi a gurin ba hakan yasa na daga kaina na fara waige waige a gurin, kamar yasan shi nake nema sai ya dago min hannu daga can inda yake tsaye jikin wata kotuwar mota mai ruwan toka, kamar kar na karasa a inda yake, sai dai kuma akwai tarin tambayoyin da shi kadai zai amsa min ba, akwai abubuwan da nake son a banbance min, ina son ko wane launi da zanen kaddarata ya fito min a kalarsa, fari yai fari fes bakin yai baki wulik ta yadda zai fuskanci alkibila ta, ina son sanin wanene shi, a yau ina son nai ninkaya a duniyar tarihinsa, ina son na bazama a duniyar mafarkinsa a kaina na wanzu da burinsa da dalilin bibiyata da yake.

“For the last time waye kai?”

Ita ce tambayar da na fara aika masa tun kamim na isa daf da shi, ina ta yawo da idanuwa a fuskarsa.

“Kina da bukatar hutu, ya kamata ki huta daga baya sai mu yi maganar”

“Hutu? Hutu a duniyar macen da ta zo bauta? Hutu a rayuwar matar da manta da jindadi a rayuwarta? Fada min waye kai...!”

Na fada da iyakar karfina har sai da ya soma tsorata ta yanayi na.

“Sunana Abraham zauna a ciki sai mu yi magana”

Ya fada yana bude min motarsa.

“Sunanka baya min dadi ka daina maimaita min abunda na riga na haddace, kasan me nake nufi ka bani amsa kawai”

“Idan na baki amsa ba zaki guje ni ba? Idan na fada miki waye ni ba zaki kyamace ni ba? Ki min alkawari cewar fada miki waye ni ba zai kawo kiyayya a tsakaninmu ba”

Kallon mamaki nake masa.

“No wait.... Why all this?”

“Saboda na taba cutar da ke.... ”

Har lokacin da yake maganar ban kawo komai a raina har sai da ya fadi kalmarsa ta karshe, zuciyarta ta fara raya min wani abun da ban taba mafarkin faruwarsa, lalabe na fara yi a duniyar tunani na, sautin wacan muryar nake hada da wannan, ina ta kokarin siffanta surar wacan da wannan, farat daya na nemi duniyar tunanin nawa na rasa, abubuwan da nake kokarin hadawa duk suka watse, sai na ji kan nawa kamar babu komai a ciki. Tafiya nai bayabaya kamar zan fadi sai yai saurin kai hannunsa zai kamani.

“Dan.... Allah... Kar.. Ka... Taba... Ni... ”

Na fada a wahale, wasu zafafan hawaye na sauko min, kamar yadda shi ma idanuwansa suka fara fitar da hawayen.

“I can't hide it anymore yanzu, ba zan iya cewa ba da gangan na aikata ba, i rape you amman ban tsammanci zan dawo gareki ba, and on that very night da kika fada min kin samu cikina ban iya bachi ba a ranar saboda tunani da farinciki jin haka, daga lokacin na samu kaina da kaunar ki da kuma son rayuwa da ke, because my only hope and pray is na samu haihu kamin na mutu, na san zan iya mutu at any moment, but i want to make my parents proud, and ina son ko na mutu na bar carbon copy na....”

Ya karasa muryarsa a dakishe saboda kuka. Risinawa nai gabansa na hade hannayena kamar neman gafara.

“Why do you rape me? Mi mai maka?”

Sai shi ma ya risino saitin fuskata yana share hawayensa.

“I don't know why, na san dai mijinki na je nema a wannan daren.... ”

Be gama maganar ba na mike tsaye na juyo tafiya na fara yi kamar mai ciwon kafafuwa, ko wace dagawa da takawa tana min nauyi, ga nauyin zuciya da ya danne min kirji har yana neman numfashina, ina tafe wasu hawaye masu zafi suna sauko min yawun bakin gaba daya ya canja gumi na ta karyo min har kasan marata murdawa yake, ina ta girgiza kai alamar a'a a'a ban daina ba har sai da na hango Abdallah ya fito daga cikin emergency sanye da shadda hannayensa duka biyu zube a aljihu... Tsayawa nai cak ina kallonsa, a yau ji nai kamar an halittoni ne kawai domin kallonsa, kaunarsa da tausayin kazafin da nai masa wanda har ya kai ni ga furta masa. Babu kamar kai Abdallah Wallahi babu irinka, mutumen da ya kasa nuna min kyama balle yayana, mutumen da ke bani taimako da kowace hanya, mutumen da idan nai gudu naje gunsa da bukatuna da damuwata zai tara hannayensa biyu ya karbe ni, na yi kuskure tabbas na aikata kuskure na barin mutune da ya dace da zama abokin rayuwata....

“Kullum cikin kuka kike please smile....”

Maganarsa ce ta dawo da ni daga duniyar tunanin da nake, ashe ya karaso kusa da ni ya ban sani ba, fuskarsa da murmushi yana min alama da nai murmushi da yatsan hannunsa biyu kamar yadda murmushin yake a fuskarsa.
Ban tana jin kaunarsa Abdallah sai yau ban taba jin kimar Abdallah ba sai yau ba, ban taba jinjina abunda yake min ba sai yau. Murmushin nai ina hawaye.

“That's my girl....”

Ya furta sannan ya maida hannun aljihu yai gaba abunsa, kamshin turarensa ya daki hancina har sai da ma lumshe idanuwana....
Na samu dakika biyar a haka kamin na juya ina kallon tafiyarsa cike da kaunarsa, wata kila jikinsa ne ya bashi cewa ina kallonsa sai ya juyo ya kalleni tare da aiko min da kyakkyawan murmushin wanda ya sanyaya min zuciya ji nai kamar na ruga na rumgume shi na fada masa cewar yau Ni Halimatu ina kaunarsa.....






___________

Ana wata ga wata, ina masu team Abraham ashe abun na ku.....🤐😥
Team Abdallah
Team Gwarzo
Za mu ga team din da yafi yawa 💃💃
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


3️⃣8️⃣

Ban koma cikin dakin ba, a harabar da amsu jinya suke zama na samu butar wata matar nai alwala ta bani carpet nai sallah nai addu'a sannan na tashi na nufi wani bangare na asibiti gurin da aka kawata da furanni da kuma hasken fitulun kasancewar hudu ya fara. Tsaye nai a gurin ina ta kallon sama wata iska mai dadi na kadawa hawayen idona na ta aikinsu, babu abunda nake tunani sai Abdallah babu wanda nake hangowa a tare da ni sai a yanzu nake ganin dacewar tarairaya ta da Abdallah.

“Uhmm na san na bata miki akan maganar da nai dazun amman iya gaskiyata nake fada, kina da damar da za ki ji haushi na ki tsaneni kuma zan jira har zuwa lokacin da zaki warke daga raunin da nai miki.... ”

Juyowa nai a hankali na kalli Aminu wanda ke min maganar, sai a yanzu nake kallonsa da kyau ya rame sosai ya dan yi duhu. Dan murmushi nai na nufi wata karamar balcony na zauna sai shi ma ya tako ya zo ya zauna kusa da ni. Magana na fara yi ba tare da na kalle shi ba


“A lokacin da nake budurwa idan mai ma mahaifiyata ko mahaifina wani aiki ko abunda ya faranta musu rai, sukan ce min Allah yai miki albarka ya baki miji na gari, ni kaina ina yawan addu'ar a sallah ta, a lokacin da ka zo kace kana so na ka aureni sai na ji cewar Allah ya amsa addu'o'inmu, bayan na yi haihuwar farko ka juya min baya, sai na fara addu'a ina ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login