Showing 126001 words to 129000 words out of 217237 words
goma sha daya, wasu suka aje biron kamar yadda ha fada wasu littafi wasu kuma sun rufe kyautarsu da irin ledar nan mai kyali.
“Ku yi hakuri is like kamar na yi force dinku, tun jiya ya kamata na fada muku amman ba samu dama ba yau din ma sai da na dub status dinta sannan na tuna”
Duk muka shiga nuna masa cewar babu komai ai kyautatawa, duk wanda ya aje juyawa yake ya fita, har ya zama ni ce ta karshe, hannu na saka na cire agogon hannun duk kuwa da kasancewar na mata ne na aje a saka tare da chewing gum daya sannan na juya na fita ina aynnawa a raina cewar wata kila zubdasu zai yi.
Har na dawo na fara aikina ban daina jin kafata da kaina suna min ciwo ba, hakan yasa na nemi izini na fita daga ward din mu da zimnar na kai kaina titi gurin mai chemist din nan na siyo magani.
Ina kawowa reception nai arba da Ahmad ana nuna masa abu a katuwar plasma dake gurin, wani irin mugu faduwa gabana yai domin na san yadda ya tsane ni balle ace yau ya gano ina aiki karkashinsa.
Da kallo ya bini har na kusan ficewa sai na ji an daga min tsawa da wani irin karfi.
“Keeeeeeeeeeee!”
Ba ni kadai ce mace a gurin ba, amman ina jin muryarsa na san da ni yake, hakan yasa na juyo na kalleshi.
“Me kike anan?”
Shiru nai na kasa cewa komai har sai da mutumen da ke kusa da shi ya amsa da.
“A nan take aiki tana cikin sabobin ma'aikatan da aka dauka, zo nan”
Mutanen ya karasa yana min alama dana karaso gurin da hannu. Ba musu na karaso gurin.
“Ku sallameta”
Da sauri na daga kai na kalleshi idona cike da hawaye, tabbas yau da ace Ahmad shi ke da kamfanin nan da sai na yi masa wankin babban bargo, amman ba wannan damar.
“Ka taimaka min dan Allah ina da bukatar aikin nan....”
Na roka ba dan komai b sai dan na san idan har wannan aikin ya subuce min kamin na sake samun wani aiki ne a gareni.
“Ranka ya dade tana da takardunta fa, duka ma'aikatan da aka dauka suna da takardu”
“Ku aje ta reception....”
Shine kawai abunda ya fada har ya juya sai kuma ya juyo yana kallona
“Karki shigo min kamfani da kwaliya, ba dandali ba ne nan”
Kai na gyada masa alamar okay ina share hawayena sannan ya juya ya wuce ya bar a gurin tsaye mutanen da ke gurin na ta kallona. Ji nai ba zan iya zuwa siyen maganin ba saboda kunya da kukan da ya rufe ni na wulakancin da Ahmad yai min a yau. Sai na koma ward din aikinmu na zauna, tsakanin shigowata da zamana be kai minti goma ba wani ya shigo ya canja min gurin aiki zuwa reception.
AHMAD POV.
A hanyarsa ta karasawa gida ne ya kade Halimatu at first ya fito da fada a cikin motar sai dai ganin ita dince yasa shi jan tsaki ya koma cikin motarsa duk kuwa da irin bakaken maganganun da take fada masa, ya kyaleta ne kawai saboda ita din macece baya fada mata yana daukar namiji mai fada da mata ragon namiji, balle kuma ita da ba shi da lokacinta.
Gida ya koma ya karya sannan ya dawo kamfanin, a reception ya tararda ma'aikatansa a gaban katon plasma dake gurin suna kallon harin da aka kai barno, sai dai ganinsa ya saka kowa ya kama gabansa, ban da Rilwal dake labarta masa abunda ke faruwa. Uffan be cewa Rirwal ba, yana kokarin kama hanyar office dinsa sai ga Halimatu ta fito daga wani bangare na kamfani abunda ya bashi mugun mamaki, kararsa ta kawo? Ko kuma wani nata ne a ciki? Ko wani abun ta zo yi? Da kallo mamaki ya bita har sai da ta kusa ficewa daga gurin sannan ya daka mata tsawa, ta juyo jikin a sanyaye.
“Mi kike a nan?”
Ya tambaya co's idan ma zuwa take kamar yadda ya ganta a wacan karon yai mata warning kar ta sake zuwa masa kamfani yo his surprise sai rirwal yai masa bayanin aiki take a gurin, a take ya bada umarnin a koreta. Sai dai yadda ta marairaice fuska tana hawaye tana rokonshi, yasa shi canja mata position a maimaikon korar gaba daya.
Kai tsaye ya nufi office dinsa ya bar a gurin tsaye tana hawaye da suka saka shi jin babu dadi, yana tura kofar office din farko mutane da ke office din ya mike tsaye yana gaisheshi, haka ma na biyu sannan ya shiga office dinsa.
Sam ya manta da zancen da Siyama tai masa cewar tasa ayi kowa ya bashi gift sai da yaga taren abubuwan da ba zai iya tsayawa ya tantace ko kiye da miye ne a gurin ba. Gaban teburisa ya karasa ya zauna, hannu ta kai ya danna telephone dinsa.
“Zo”
Shine kawai abunda ya fada ya sannan ya mike tsaye ya cire rigar dake jikinsa ya dorata a bayan kujera. Mutane da ke office na biyu ne ya shigo da sauri sai Ahmad ya nuna masa kayan dake kasan tebur din.
“Kwashen abun nan ka san inda zaka kai su... ”
Ya fada yana masa nuna da baki idonsa na kaiwa akan wani agogo da chewing gum kwara daya dake gefe agogon. He don't know why he find it so intereste to touch.
“Mi komin wannan agogon”
Mutumen ya dauko ya miko masa, sai ya karba yana dubawa agogo chewing gum diary na daya daga cikin abubuwan da his late wife Halima take bashi as a gift a idan yai birthday, tun kamin ta aureshi har bayan aurensu. Ji yai ba dadi tunawa da matarsa da yai, da kansa ya duka ya dauko cingon da wani karamin diary dake can gefe ya nufi kujera ya zauna.
“Kasan wa ya min kyautar agogon nan da diary nan da chewing gum din nan?”
“Wallahi ban sani ba ranka ya dade, su da yawa suka shigo kuma ban san waye ba cikinsu dan ba gabana suka aje ba”
“Okay take the rest”
Dorowarsa ya bude ya saka diary da agogon a ciki sannan ya bude chewing gum ya kai bakinsa. He can't remember when last na ci chewing gum sai yau hakan yasa ya ji ya masa tauri, or maybe saboda wannan karami ne ba irin mai tsada da ya saba ci ba. Haka nan kawai Halima ta fado masa a rai, did she deserved to work a kamfaninsa? Bayan dazu dazun nan ma ta gama zaginsa, ashe kuma ta san a kamfaninsa take aiko amman ta ci masa mutunci? Ko da yake shi ya kadeta kuma be tsaya ya dubata ba yai tafiyarsa, amman duk da haka ai be kamata tai masa rashin mutumci ba. Laptop dinsa ya janyo ya bude ya fara duba wasu abubuwan.
After like 40 minutes Yunus ya shigo masa da wasu takardu, after ya gama masa bayani yake tambayarsa.
“So ka biye shiriritar Siyama kasa am bata min office da gift ko?”
Yunus yayi dariya.
At least ai an saka ka farinciki, tunda birthday ka ne, ban saka kowa yayi ba amman dai na saka sabbin ma'aikatan mu ne su baka abunda ya samu”
“Nope ka san ba komai ke burge ni ba”
Har ya dauke kai sai kuma ya juyo da sauri.
“Sabbin ma'aikata? Har da wannan farar mata tana nan ciki....”
“Wace farar mata?”
“Wacce na saka aka canjawa position dazun baka nan?”
“Yeah amman na samu labari, har da ita dukansu na saka ai ita ta aje maka chewing gum da agogo”
Jimmm Ahmad yai.
“O.... Okay....”
Ta fada yana daina tauna chewing gum tare da yatsuna fuska...
I feel like na karo wani page anjima da dare 😝😝😝 amman ga masu comments kadai 🙄🙌
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣1️⃣
HALIMATU POV.
Ba laifi sai na ji kamar inda aka dawo da ni a yanzu ya fi na farkon dadin zama, domin a can rubuce rubuce ne, a nan kuwa kula da masu shigowa ne kawai gashi sai fira muke tare da sauran ma'aikatan, daya mace ce wacce ta kasance kabila ce sai ni ta biyi sai maza uku, ni kadai ce ba ni da uniform a cikinsu, domin ni tufafin gida ne a jikina.
Ban yi awa daya a gurin ba aka kawo min wando da riga na kamfanin, irin na sauran ma'aikatan da suke gurin mai dauke da sunan kamfanin, tare da wani dan abu da ake sakawa a wuya wanda ke dauke da sunana sai kuma gurin saka hoto, har ga Allah bana son saka kananan kaya abu ga mai dan jiki balle ni da Allah ya horewa abun duk yadda zan so boyewaba boyuwa zai yi ba, na saka skirt ma suka bayyana balle kuma wando, na dade rike da tufafin ina da tunaninsa sakawa ko akasin hakan, sai dai na san idan har na ce ba zan saka ba zasu iya korata. Ba ni da wani zabi da ya wuce na saka din ai idan ina a reception din babu mai ganina tunda katon tebur din ya tare ni sai dai idan zan tashi kuma idan zan tashi zan iya canja tufafi ko kuma na saka mayafi. Bandakin kamfani na nufa na canja tufafi sannan na saka hijab dina na fito reception din a lokacin da na tsaya a inda ba a ganina sai na cire Hijab din na cigaba da aikina hankalina a kwance. Wani abun burgewa ashe na wadanda suke reception din har da abincin ake kawo musu da ruwa tsabanin da da sai dai yunwa da kashe ni.
Mu uku muka je cin abincin tare da blessed da Walid, muna cikin cin abincin yake dauko mana labarin sabon kamfanin da za ake tunanin budewa a wata jihar sai dai suna tantamar garin da za a bude, mun dade muna tattaunawar har nake bayarda shawarar da ace za su yarda da sun bude a Kano domin can ne cijiyar Kasuwanci, ko kuma Jos duba da yanayin garin Walid kuma yace Abuja, a haka dai muka gama cin abincin muka tashi muka koma gurin aikinmu su biyun da basu ci ba suka koma ciki dan cin abincin.
Ina tsaye a gurin sai ga wasu fararen mutune sun shigo, da fari dai na dauka turawa ne, a take hankalina ya koma gurinsu tun kan su karaso nake ta kallonsu cike da burge domin kusan sai nace ban taba ganin turawa a zahiri ba sai yau, sai dai na lura sauran abokan aikina ba kamar ni suke ba, wata kila sun saba ganin turawa ba kamar ni ba da na zama bakwaya har murmushi nake musu kamin su karaso.
Ko miye abun burge a farar fatar ma oho sai kace ni din ba fara bace ko da yke nawa farin mai kyau ne, domin na su ba shi da kyau kallo farin yayi yawa har wani kashe ido yake.
Suna isowa sa abokin aikinki ya tarebe su da yaren turanci su kuma suka masa magana da faransanci hakan yasa na fahimci cewar faransawa ne ba turawa ba kamar yadda nake zato. Hakan yasa na yi kaudin yin musu harbun da tambayar abunda suke bukata a dan abunda na iya na yaren faransanci. A take suka mayarda min da amsa, aiko nan dade ya kusa kashe ni wai ni na magana da wanda ba yare ba kuma ba yan kasa ta ba. Da suka fada min wanda suke bukatar gani wato shugaban kamfanin sai na fadawa Walid shi kuma ya nuna min yadda zan yi na kira na sanar idan bukatar irin haka ta taso, kamin na danna number wanda yace min shi ake fara kira a sanarwa, sai ga Yunus din ya fito daga cikin kamfanin ya tare su da far'arsa har ya basu hannu suka gaisa, sai dai shima na lura be iya faransanci ba kamar dai sauran abokan aikina. Godiya suka min da yarensu na mayar musu da godiyar nima sannan suka bi Yunus zuwa ciki. After like 15 minutes ya fito yana tambayar wai na iya faransanci ne sosai.
“Gaskiya ba sosai ba gaisuwa kawai na iya sai dan abunda ba a rasa ba, ban iya sosai ba”
“Amman za ki iya kula da su kamin mai fassara mana ya iso?”
“Yes”
“Good zo muje”
Sai da na dauki gyalena na yafa sannan na bi bayanshi, sai dai a yanayin yadda yake tafiya ne yasa nai saurin cin masa duk kuwa da kasancewar ina tafe ina dingishi ne sai muka jera a tare muna tafiya a tare, ba laifi yana da sakin fuska da son magana ba kamar mugun gogan ba, a nan yake tambayar inda na iya yaren faransanci, na fada masa tun a secondary school na yaren yaren sosai lokacin da muna can sai dai shiga FUG yasa na manta da wani abu, ga kuma abubuwa na rayuwa sai na watsar da abun. Sai a lokacin da zamu shiga cikin office din ya bukaci na cire mayafin nawa, hakan yasa ni jin babu dadi wanda har ya bayyana a fuskata.
“No ba wani dadewa za ki yi ba, za ki yi tambaye abunda suke bukata ne kawai sai kuma fara gabatar musu da abunda zan nuna miki kamin mai aikinmu ya iso”
“Ba fa komai na iya a faransanci ba, ba zan iya wani dogon bayani sosai ba”
“I know saboda kar mu barsu shiru ne, tun mun zama kurame mu da su”
Ban musa ba na cire Hijab din kamar yadda ya bukata, daman can dankwalin atamfa ne a kai, ga farar riga da bakin wando na kamfani sai ya bada wani kala na dabam, na yi zaton su kadai ne a dakin taron, sai na tarar har da Angry Bird din ya wani shakimce a saman kujera yana ganina ya wani hade rai. Ni kuma na tsaya bakin kofa har sai da Yunus din yai min iso.
Na shiga ciki na tambaye su abunda suke bukata na sha suka bukaci ruwa kawai, shi ma kuma da aka kawo ba su sha ba, abunka da marar yarda, haka nan dai cikin rashin iyawa na rika dan nuna musu abubuwan da Yunus ya nuna min, wanda suke a katon wani abu mai kamar tv kuma shi ba tv ba, da removed din hannuna na rika nuna musu kalolin zinarin da suke a ciki, domin ya fada min abun nan ja na jikin remote din kawai zan taba su za su rika canjawa da kansu.
Muna haka sai ga mai fassarar ya shigo, na yi zaton idan ya shigo umarni za a bani na fice sai gashi ya saka ni cigaba da danna remote din shi kuma yana musu bayani da halshen faransancin, ina jin wani abu wani abun kuma bana gane komai, wani abun zai fada ma Ahmad da Yunus abunda suka ce ne sannan ya cigaba da yi musu bayanin, har akai aka gama Ahmad be ce komai ba, sai aikin tsutsar minti yake, ni kuma ban ma sake kallon inda yake ba. Sai da suka gaisa da shi sannan suka fice tare da mai fassarar, hakan yasa na aje remote din ina jiran a bani umarnin ficewa, amman Yunus din sai karin bayani yake ma Ahmad din. Ni kuwa hankali gaba daya yana gida ga garin ya hada bakin hadari kamar yadda nake hange ta cikin gilashin da ke gafenmu.
“Ranka ya dade zan iya tafiya”
Na fada ina kallon Yunus din a tare suka kalleni daga Ahmad din har Yunus ne.
“Sorry yau mun baki aiki da ba naki ba”
“Babu komai”
Har na aje remote din ina kokarin juyawa sai yace.
“Ta ina za ki bi? Na sauke ki”
Kamin na bashi amsa Ahmad din ya tari numfashinsa sound so serious fuskarsa babu alamun wasa.
“Shi kuma wacan aikin wa zai yi?”
Nikam daman ba shiga motar zan yi ba, hakan yasa kamin ma Yunus din ya bashi amsa na ce wa Yunus din.
“Na gode ranka ya dade zan fi sakewa idan na hau napep”
Daga haka na juyo na fito daga office din ina mamakin irin kiyayyar da Ahmad ke min akan abunda har a gurin Allah bana da laifi domin ban aikata ba, wato yaji haushin da Yunus din yace zai rage min hanya ko waya fada masa ma shiga zan yi oho.
Da tunanin hadarin na fito hakan yasa ban wani tsaya canja tufafi ba yafa mayafina na dauki kayan na saka riga a handbag dina domin ita kadai zata iya shiga sauran kuma na rike a hannu na bi hanya domin tuni abokan aikina sun wuce har wasu sun karbi duty.
Ina tafiya aka fara yayyafi ban yi zaton zai yi karfi ba, hakan yasa na kara harama da zimmar kamin ruwan yai karfi na samu abun hawa, da ganin hadarin ba irin wanda idan an fara ruwan nan ba ne a daina, wata kila za a dade a na ruwan.
Ko da na fita gate babu masu Napep sai achaba su ma kuma kowa da goyonsa, sai gudu suke ni kuma na maida himma sai tafiya nake ina waige waige ko zan samu abun hawan, ban nisa sosai da kamfanin ba aka sako da wani ruwa mai mugun karfi, hakan yasa ni cira kafa har da dan guduna na nufi inda wata yar rufar kwano wacce ke kusa da inda Kabir yake. Babu kowa a gurin hakan yasa na shige rumfar da sauri na fake, domin tuni ruwan ya fara jikani. Sai dai wani abun mamaki duk ruwan nan da ake Kabir na zaune a inda ya saba zama ruwan na duka kansa, ban san lokacin da tausayinsa ya rufe ni, da sauri na aje kayana da jakar hannu a gurin na fita a ciki a rumfar na nufi inda yake cike da karfin hali domin a yanzu kafar ta fi min zafi fiye da dazun. Da fari magana na fara masa akan ya taso ya bar gurin sai na ga yana ta kallona kamar be gane ni ba, hakan yasa na kai hannnu zan riko shi, aiko kamar jira yake sai ya hayayyako min