Showing 78001 words to 81000 words out of 217237 words
fice daga dakin, dan yasan halin Hajiyarsa yanzu sai ta sauya ma zancensa ma'ana shi ko ba dagon zance yake so ba. Part dinsa ya nufo har lokacin hannayensa a aljihu yana takawa a hankali kamar mai jin wuyar cira kafar. Be yi mamakin ganin kofar falonsa a bude ba tun da ya san mai masa haka a duk lokacin da aljanun nata suka tashi. Yana shiga ta zo da gudu ta rumgume shi tana dariya.
“Yes Daddy Oyoyo, Daddy na gyara maka dakinka na goge komai na sa turare”
Kanta ya shafa cike da kaunarta, yana murmushi.
“Good girl Allah yai miki albarka”
“Ameen Daddy za ka kai ni gidansu kawata Namra ko?”
Iskar bakinsa ya busar ya rika hannunta suka nufi kujera ya zauna, ya zaunar da ita saman cinyarsa sannan ya soma mata magana a hankali.
“Baby ke kullum kina zuwa gidansu kawarki nan amman ita ba kasafai take zuwa nan ba”
“Daddy ai su gidansu ba su da mota, shiyasa bata yawan zuwa, ni dai ina son zuwa gidan Daddy pls... ”
“And Baby na yi m maman kawarki fada”
Ya fada yana shafa kanta har yanzu jin yake be kyauta ba. Ta zaro ido tana rufe baki.
“No Daddy how?”
“Laifin tai min nai mata fada, so ko kinje gidansu ba zata miki yar fuska”
“Daddy tana aiki a karkashinka ne?”
“No”
“Then why kai mata fada?”
“Wani abun tai min wanda ya bani haushi”
Baby Namra ta yi masa wani kallo.
“Daddy waye be da gaskiya tsakanin kai da ita?”
“Ni ne”
Ya amsa kai tsaye sai ta sauka daga saman kafafuwansa.
“You should apologize to her”
Sakin baki yai be ce mata komai ba.
“For the sake of me Daddy bana son na bata da kawata Namra ina sonta, idan muje gidan ina jindadi akwai mutane da yawa a gidan kuma duka suna suna kuma Daddy scul din mu daya, Mommynta ta shafa kaina tace Allah ya min albarka Daddy why za ka yi fada da ita?”
Kokarin fashewa da kuka take, domin har cikin zuciyarta take son zuwa gidan su kawarta Namra and tana jindadin yadda yan gidan suke mu'amalantarta.
Hannayenta ya kama
“Zan kaiki gidan amman ba zan bata hakuri ba, ni nake da gaskiya ai”
“Amman yanzu ka ce kai ne da laifi fa”
“I mean na yi fadan da yawa amman dai ni ne mai gaskiya”
“Daddy.... ”
“Baby.... ”
Shi ma ya marairaice fuska kamar yadda tai yana kokarin rarrashinta Hajiya ta shigo falon.
“Gwarzo”
“Na'am Hajiya”
“Taso ka kaita gida”
“Bata wuce ba?”
“Eh kai zaka kaita gida, kuma ka tsaya ka kalleta da kyau”
“Tooo....”
Ya fada da dan mamaki, sannan ya saki hannun Baby Namra.
“Baby zan je na dawo sai na kaiki gidan ki bata hakuri a madadina kinji?”
Ta gyada masa kai tana share kwalla, Hajiya na gani hankalinta ya tashi.
“Baby ya akai? Me kike yi ma kuka?”
“Daddy ne ya tsokani momyn kawata Namra”
“Garin ya? Shi ne kika kuka kuma?”
Ta gyadawa Hajiya kai, shi kuma ya fice yana ta sake sake a ransa. Falon Hajiya ya shigo sai ya samu yarinyar a zaune ta natsu sosai guri daya tana wasa da yatsun hannunta.
“Hajiya ta ce zan kai ki gida”
“Okay tau”
Ta mike tsaye tana daukar katuwar ledar da Hajiya ta bata tana unkurin tafiya sai ga Hajiyar ta shigo rike da hannun Baby Namra tana fadin.
“Ka biya da ita asibiti kanta ke ciwo, na bata magani ta sha tace min be daina ba”
Da okay ya amsa can kasan zuciyarsa kuma ya raya cewar lallai da gani hajiya na ji da bakuwar nan. Har gurin mota ta rakosu sai da ta shiga sannan tace..
“Ikilima ki ce ina gaishe da Hajiya na gode sosai sai na zo”
“In-Sha-Allah zan fada mata na gode Hajiya Allah ya saka da alheri”
“Ba komai Wallahi a sauka lafiya”
Sai da ya tashi motar aka bude musu gate sannan ta koma ciki. Tafiya kadan sukai Ahmad ya rage gudun da yake ba tare da ya kalleta ba ya ce.
“Ke ni ban san asibitin da zan kaiki ba, duk asibitin da zamu je yanzu sai mun bata lokaci kuma company mu yau basa aiki balle na kai ki chemist din dake ce, ku ba ku da likita ne da yake duba ku ko kika saba zuwa gurinsa?”
“Akwai wani likita da ke dubani, amman yanzu na sa ya tashi asibiti yana chemist dinsa”
“Ina chemist din take?”
“Tana can gurin tudun wada locos”
“Za ki gane gurin?”
“Eh na san gurin”
Be sake ce mata komai ya canja hanyar tafiyarsa zuwa gurin da ta fada masa, ita tai ta fada masa gurin har suka iso.
“Ki shiga ki ganshi zan jiraki a mota, duk yadda akai sai ki fada min zan ji da komai”
Ba musu ta bude motar ta fita shi kuma ya ciro wayarsa ya soma latsawa tare da kwantar da kujerar motar. Kamar hadin baki sai ga sakon karta kwana ta line Hajiya ya shigo.
_Ka samu wani abu ka bata, ko ka siya mata wani abun_
“To duk dai”
Ya furta yana murmushi, kamar wanda aka cewa dago, yana dago kansa yana hago Halima ta fito daga chemist din rike da leda baka. Bude motar yai ya fito, sai ya fito sai ya fara tambayar kansa me zai ce mata sorry? No ai ya girmi wannan yana jin idan yace mata haka ya kayardar girmansa. Amman ai ya kamata ya bata hakuri ko dan Namra, kuma tabbasa ya san be kyauta mata ba. zagaya yai ta inda take tafiyar dayan hannunsa a aljihu dayan kuma rike da waya ya sunkuyar da kansa kamar da gaske hankalinsa yana kan wayar ne.
“Ya akai lafiya? ”
Ta tambaya ganin kamar zai tare mata hanya. Dagowa yai ya kalleta sai kuma yaji nauyi bude baki yai mata magana.
“Ko nan din ma hanyarta ne? Ko kuma tsabar rainon wayo ne kawai da wulakanci irin na ka, ko na maka kama da yar tasha ne, domin yanzu na fahimci babu komai a tare da kai sai wulakanci kawai, a duk lokacin da na hadu da kai sai ka wulankanta ni ko kasa a wulakanta ni, kai na fahimci sam ba mutumen kirki ba ne, sai wani jijji da kai, kana jin kai wani ne kuma kai ba kowan kowa ba, abun kai min dazun na kyale ka ne kawai saboda ina ganin kamar ni ce bana da gaskiya but then i realized na fi ka gaskiya, kai sam baka da kirki sai wani son nuna isa kamar mai garin Gusau, to bari na fada maka karka sake cewa zaka min wani rainon wayo Wallahi zan mugun wulakantaka, dan na gane ku mazan nan ba ku da mutumci, by the way ina da miji ina da aure ina da yaya karka sake ka ce zaka min magana Mtscheeeessss.....”
tun da ta fara maganar yake kallonta har ta gama taja masa tsaki ta kara gaba ta bar shi a gurin da mamaki.
“I just....”
Ya fada yana daga hannunsa tare da bin bayanta da kallo, sai kuma ya ksa cewa komai ya jimke hannun.
“Am... Baya nan wai be shigo ba yau”
Ikilima ta fada shi kam har ya manta tare da wata suka zo, sai a lokacin ya soma lura da ba su kadai ba ne a gurin. Kasa kasa yake satar kallon mutane be taba jin tozarci irin wannan ba. Matsawa yai kusa da Ikilima.
“Mutane suna ganinmu lokacin da take min fada?”
“Yes da karfi fa take yi dole kowa ya kalleku ai”
Wani abu na ji kamar ya netse a kasa, saboda ya san people would think ko ya mata wani maganar banza ne. And she's right be kamata yai magana da matar aure ba, dan idan shi ne wani nai magana da matarsa zai iya masa komai ma, but shi ya manta da maganar aurenta ma.
Oh does she think sonta yake yi? Ko kuma ta maida shi wani banza ne take fada masa haka, har ya shiga motar be daina sake sake ba.
“She got lucky bana fada da mata, amman wallahi da namiji ne yai min haka sai an dauki gawarsa a nan i hate nonsense”
Ya fada yana fisgar motar kamar zai tashi sama, after few minutes ya bugu sitiyarin motar da karfi.
“Matar nan ba tai ba, i hate her so much, da ganinta mahaukaciya ce”
Ikilima dai bata ce masa komai ba bayan kallonsa da tai, tsoro dai ya gama kamata dan ta lura ransa ya bace sosai.
“Ai duk laifinki ne da kika kawo ni gurin nan, da ta isa tai min kallon banza ma, amman ji irin maganar da ta fada min son ranta, sai yanzu ai na gane bakar magana ta fada min”
Nan da nan jikin Ikilima ya fara rawa domin ta lura har fuskarsa ta canja sa gumi yake kamar marar gaskiya duk kuwa da irin ac da ke cikin motar.
“Har da wani wai kana jin kai wani ne, ai ni wani din ne ke ba kowa ba.... Mtchhhh”
Yaja tsaki yana jin kamar a gabanta ne ya rama, domin a duniyar nan yafi tsanar tsaki fiye da komai, da ka yi masa tsaki ko ka tofar masa da yawu kara ka mare shi ko ka zage shi.....
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣7️⃣
Na isa gida cikin bacin rai, ban taba jin na tsane wata halitta kamar yadda na tsani wannan mutumen ba, a yadda na fahimci rayuwata ina ta faduwa da mazaje marasa mutunci, maso sun su taka ni yadda ransu yake so, wanda ni kuma nake ganin ba zan dauki hakan a yanzu ba, na gama indai kuka ne akan wani namiji ko shiga damuwa akan wani namijin ba zan sake bari wani ya saka ni damuwa ba.
I can live without aure indai har zan iya tsare kaina da mutumcin na tarbiyantar da yayana, zan iya shiga aljanna, haka zuciyata ke raya min i feel like idan har Abdulhamid ya sake ni ba zan sake wani auren ba, zan cigaba da aikina ina kula da yayana, zan nemi ya sake ni bana bukatar sake zama da shi ji nai na tsani duk wani namiji a duniyar har na rika jin na matsu ya dawo gidan, kamar ance min da ya dawo zai rubuta takardarta ya ba ni.
Maganin da na siyo dan na sha na samu bachi ne ammn sai bachin rai ya hana ni sha. Wani irin kuzari da karfin hali nake jin yana ratsa ni, i feel like ko da duniyar nan za su taru su tsane ni i can live, even for the sake of my children right? Yes this is right time da zan nunawa duniya wacece ni, wannan lokacin ne ya kamata na amsa suna, i don't know what the future bring ban ce ba zan sake facing wani challenge ba, but zan iya jurewa zan iya daurewa daga lokacin na fara rayawa kaina cewar gobena mai kyau ce. Na yi kuka a lokacin da na ke fuskantar wulakanci a gidan Aminu, na yi kuka a lokacin da akai ma Namra fyade, na yi kuka a lokacin da Aminu ya sake ni, na yi kuka a lokacin da akai min fyade, amman hakan yana nufi sai na zauna nai ta kuka akan komai akai min na bar damuwa a raina? No be kamata na karaya ba, be kamata na lauyewa kaina hakkina dan ina mace ba! I have to say it out loud, i have to fight for my right.
Kamin dare yai Abdulhamid ya shigo duk na matsu sosai, saboda irin abunda na kudirewa zuciyata, ban girka komai ba har dare, can bayan sallah isha'i sai gashi ya shigo gida kamar yadda ya saba, da ada ne ko be yi sallama ba ya shigo zan masa sannu da zuwa amman a yau sai na ji ba zan iya yi masa hakan ba. Ga duka alamu yau da yunwa ya dawo, domin yana dawowa ko dankinsa be shiga ba ya nufi dinning rike da wasu takardu a hannunsa. Ganin babu abincin a dinning din yasa ya juyo ya kalleni.
“Ina abinci?”
“Ban girka ba”
Daga inda nake zaune saman kujerana bashi amsa kai tsaye. Be sake cewa komai ba ya tashi ya nufi hanyar dakinsa yana shiga na rufe masa baya, sai na same shi yana kokarin cire rigar shaddar da ke jikinsa, hango shigowata ta madubi da yai ne yasa ya tsayar da cire rigar ya juyo ya kalleni
“Kina son wani abu ne?”
“Ina son sanin result din gwajin da nai nake son sani”
Juyowa yai da kyau yana kallona for like ten seconds sai kuma ha dauke idonsa daga kallon da yake min ya kalli wani gurin dabam.
“Positive....”
“Al-hamdulillah.... Abu na biyu kuma ina son ka san cewar komai yana da lokaci kuma yana da iyaka, a lokacin da na aureka babu wanda ya cilasta ni ra'ayin kaina ne, and now mun gaji we need some space”
Sake kallona yai a karo na biyu kamar wanda be fahimci yarena ba, wata kila kuma yana mamakin furucina ne.
“Saki na ke bukata...!”
I say it..
“Are you sure? Ba ki bukatar sake shawara ko tunani”
Shine abunda ya fito daga bakinsa, sai kuma ya matsa kusa da ni ya kai hannunsa biyu zai dafa kafadata, ni kuma nai saurin matsawa.
“Bana bukatar ko daya”
Sai da ya hade yawun bakinsa sannan ya furta.
“Shikenan zan ga abunda zan iya yi akai”
Yana fadar hakan ya juya ya cigaba da cire rigarsa ni kuma na fice na bar masa dakin. Ko kadan ban ji kuka a tare da ni ba kamar yadda na saba yin kukan a duk lokacin da wani abun bacin rai ya same ni, but i feel bad ina jin na yi abunda be dace ba, miyasa ba zan jira har zuwa lokacin da shi din zai bukaci sakina ba? Why? Bana da wata hanyar ne sai wannan idan har zan jira to zan cigaba da kashe kaina ne da rai na. Can bayan na yi sallah isha'i ina kokarin kwanciya ya shigo dakina ya aje min takeway ya fice.
AHMAD POV.
Hajiya na kallonsa ta san danta yana cikin bacin rai, sai dai ta yi shiru ne saboda ta saba masa haka a duk lokacin da yake cikin damuwa idan har taji bata ji yace mata komai ba sai ta tambaya.
“Hajiya yau ko?... No first of all ita wannan yarinyar da kika saka na kai gida wacece ita?”
“Sai ka fara fada min damuwar”
“Wallahi wata bad luck na hadu da ita yau, ban taba jin na tsani mace kamar yadda na tsani matar nan ba, i hate her... ”
“Me tai?”
Kadan ya gutsurawa Hajiya labarinta yana ta tsaki.
“Kai ma ai be kamata kai haka ba, ko dan yarta na abota da yarka, sannan matar aure ce akan me zaka tare ta a hanya da sunan ba ta hakuri? Kai yanzu yadda kake da kishin tsiyar nan wani ya isa ko kallon matar ka yai?”
Kallon Hajiya yake da mamaki he thought zata bashi gaskiya ta bawa wacan rashin gaskiya ne.
“Okay....”
Sai yai shiru, kamin ya sake tambayarta.
“Ita wannan yarinyar fa?”
“Yarinyar nan da ka gani bazawara ce”
“What....?”
Ya tambaya da mugun mamaki domin a tunaninsa budurwa ce, a yadda ya ganta yarinya karama.
“Yes ta yi aure bata dace ba mijinta har dukanta yake kuma ta hakura ta zauna har sai da yan uwanta suka kashe aure, sannan gidansu mahaifiyarta ita ce ta hudu, so ta san halin rayuwa tun da ta taso a gidan yawa kuma duk mace da zata yi hakurin zama da miji mai duka zata iya hakurin zaman aure a ko'ina, shiyasa na ke son idan ta maka ka aureta”
“Aure yanzu Hajiya? Hajiya ba tai min ba, abu kamar ta tsinke ni bana son mace ramanmiya irin wannan, and kin san abunda ba zai taba yiyuwa ba ne na auri matar wani Allah ya sauwake, ba zan taba auren bazawara ba, ba zan iya auren matar da wani namijin ya aureta ya sake ta ba, ko kuma mijinta ya mutu har a bada, Hajiya ke ma kin san wannan”
“To wai miye a zaurawan nan ne? Haba Gwarzo, na aje wannan akidar dan Allah ni fa yan matan nan na yanzu ba yarda zan yi da su ba, kara wacce tai aure ta dandana dacin auren zata fi iya zaman aure a gidan nan”
“Ba dai bazawara ba Hajiya”
Ya sake nanatawa sannan ya tashi ya fice daga falon, part dinsa ya nufo har yanzu zuciyarsa cike da take da bacin rai abunda ya faru.
“Imagine wai ni matar nan ta tsaya ta fada wa maganar banza wai... Wani ni Ahmad hmmm”
Yayi kwafa sannan ya tura kofar falonsa ya shiga gumi na karyo masa, daman can haka yake da ransa ya bace sai ya fara gumi jikinsa yai zafi sosai kamar marar lafiya, idonsa ma a take suke canja, zuciyarsa kuma tai ta wani zillo kamar ta fito, shi kansa idan ransa ya bace baya iya controlling kansa, that's why yake taka tsantsan yana gujewa duk wani abu da zai kawo masa bacin rai.
AMINU POV.
Hajiya ba ta yarda ba har sai da ta saka aka yi mata na ta bincike, a gurin malamanta da kuma malaman kawayenta, sai dai duk inda take abu daya ake fada mata cewar arzikin danta hana tare da matar da ya rabu da ita, wasu ma har kara rura wutar abun suke ana fada mata cewar da ace be sake ta ba da yana daf da samun wani abun. Sai dai hakan be gamsar da ita ba har sai da ta sake saka kawarta Hajiya Mairo a gaba suka tafi gurin wani malamin. Ba su tsaya bin layi ba abun ka da masu kudi, sai aka bi da su ta wata hanyar suka shiga cikin dakin malamin. After sun gaisa ya dauko kasa ya fara bincike domin shi haka yake ba ya bari mutum ya fada masa dalilin zuwansa, sai dai shi ya fada maka abunda ya kawo ka. Yayi kusan minti ashirin yana duba kasar sannan ya dago ya kalli Hajiya Mairo.
“Waye Aminu? Gashi nan yau sun nuna min da Maganarsa kuka zo”
“Tabbas hakika maganar Aminu ta kawo mu, yaron abokiyata ne kuma aminiyata”
Ya gyada kai sannan ya kalli Hajiyar Zuwaira wato mahaifiyar Aminu ya ce.
“Sun fada min komai, dan ki na fama da gurguncewar cigaban rayuwa haka ne?”
Tai