Showing 102001 words to 105000 words out of 217237 words
iya aikatawa, kuma idan har bata aikata ba miyasa suke jin tsoro ita da iyayen?”
“Da zaka ji labarin matar nan da ka tausaya mata, kaddara ce ta fada mata kuma mahaifiyarta tai min rantsuwa....”
Saurin saukowa yai daga saman kujerar yana hade wani bakin abu daya tsaya masa a makoshi.
“Hajiya dan Allah? Bana son na ji duk wani abu da ya shafe ta, ba ina kokarin kai kararta ba ne saboda na danne mata hakki no hakki yata nake kokarin kwatowa?”
“Wace hujja kake da ita wacce ta nuna maka cewar matar nan ita ce ta kashe Baby? Haba Gwarzo ya kake neman zautuwa akan mutuwar da ba yau ta saba bakuntarka ba?”
Sakin baki yai da mamaki yana kallon Hajiya miyasa tai saurin canja har take kokarin hana shi bayan ita ma a da tana goyon bayan karar?
Siyama ce ta tashi zaune ta tana kallon Hajiya da mamaki.
“Hajiya be kamata a kyale wannan maganar ba, taya zata kashe Baby kuma a barta?”
Hajiya ta daka mata matsawa.
“Kar na sake jin bakinki ba ki san komai akan rayuwa ba, kuma idan manya suna magana karki sake tsoma bakinki”
“Amman gaskiya ta fada Hajiya indai suna da gaskiya kotu zata ba su gaskiyarsu mu kuma ta ba mu rashin gaskiyar”
Kallonsa Hajiya tai da kyau
“Mutuwar nan ta dauke mahaifinka ta dauke matarka, yanzu kuma ta dauke yarka, wata rana ni zata dauke kuma ta dauke kanwarka kamin ta dauke ka, wata rana zata zo da zaka rasa wanda zai hana ka aikata ba daidai ba balle ya fada maka kuskurenka....”
“Bana tunanin idan wannan ranar ta zo zan iya rayuwa Hajiya, na rasa babana na rayu na rasa matata yes na rayu yanzu kuma na rasa yata still zan rayu amman bana tunanin idan na rasa ki zan rayu, ku kadai kuka rage min a yanzu daga ke sai Siyama ku kadai nake da ku a yanzu, Allah ya min kyautar mata ya karbe, ya ba ni ya ya karbe, mahaifina ma ya karbi abunsa, ba ni da kowa a yanzu daga ke sai yar'uwata sai dangi”
Ya fada hawaye na sauko masa, sannan ya taso daga inda yake zaune ya nufa inda take ya rumgumeta.
“Na bar maganar nan har bada Hajiya, Wallahi na barta”
Hajiya ta lumshe idonuwanta dake cike da hawaye zuciyarta cike da tausayin danta.
“We're three mu kadai muka rage, babu Baby babu Daddy”
Cewar Siyama tana fashewa da kuka tare da rumgume Hajiya.
“Allah ya musu albarka”
Hajiya ta fada da muryar kuka, hakan yasa Gwarzo tashi ya bar falon yana share hawaye wasu na sauko masa.
HALIMATU POV.
Na ga abubuwa daya a cikin dogon bachi na, abubuwa mabanbanta, masu rikitarwa wadanda ba zan iya fassawaba, tabbas bachi da na dade ina yi a yau yana daure da mafarka kalakala. Ina ji a jikina kamar ban taba bachi mai nauyi irin wannan ba, domin ba jikina kadai ya mutu ba har fatar idona ji nake kamar ba zan iya budewa ba, numfashin ma idan ya fita daker ya ke dawowa, a duk lokacin daya dawo sai na ji wani bari da ban gama tantancewa daga ina yake fitowa ba, sai dai na sa tabbas ba na muhallina ba ne. A zuciyarta nake ta amboton mahallincina hakan ba karamin taimaka min yai har na samu karfin buden idon ba, sai kuma nai saurin maidawa na rufe sakamakon hasken da na ji yai min yawa idon har wani yaji na ji suna min. Cikin karfin hali na kai hannuna na murza idon sannan na sake budewa ina karewa dakin kallo sai a yanzu nake gane ko warin asibiti ne nake ji, amman miya kawo ni asibiti? Shi nake kokarin tunawa, a take kaina ya tsara na nemi duka tunani na rasa sai na sake rufe idon ina jin bakina da daci. Tuna abunda ya faru yasa ni saurin bude idon a nan abun neman ya samu hawaye suka fara aikinsu, unkurin tashi nai zaune amman na kasa saboda rashin kuzari. Hakan na cilasta min cigaba da karewa dakin kallo, ina haka aka turo kofar dakin wani ya leko ni sai kuma ya rufe dakin, da alama wani yake nema domin haka wasu suke idan suna neman wani sai su rika bibiyar daki suna lekawa. Har na lumshe idona sai kuma na sake jin an bude kofar a karo na biyu sai dai wannan karon na ji alamar shigowa duk kuwa da kasancewar idon nawa a rufe suke. Wani irin fitinannane kamshi turare na ji ya maye gurbin warin asibitin da nake ji hakan yasa ni saurin bude idon karaf nai arba da wani kyakkyawan farin mutum wanda ba zan iya kiransa da saurayin ba ba kuma zan ce masa mai aure ba tunda ban san gaibu ba, yana da manyan idanuwa ga dogon hanci, bakar rigar dake jikinsa ta haska fuskarsa gwanin daukar hankali. Matsowa yake ta yi kusa da ni yana kallon fuska kamar mai son tantance wani abu, van yarda a zahiri nake kallonsa ba har sai da na runtse ido na sake budewa, sai a yanzu na fahimci mutumen dazun ne da ya leko ni ya sake shigowa.
“Sannu.... ”
Ya furta min yana cigaba da kallona.
“Yauwa”
Na amsa daker, sai ya kalli kofa ya sake kallona.
“Ya jikin?”
“Al-hamdulillah kai likita ne?”
Jimm yai kamin ya bani amsa, hakan yasa ni tsaye na kare masa kallo da kyau, kusan a kuskure nai arba da sarkar cross din dake wuyansa wacce nake kyautata zaton ta zinari ce, kamar yadda hannunsa yake dauke da agogo da awarwaro na zinari haka ma zoben hannunsa, ba rigar jikinsa kadai ba har jean da ke jikinsa kana kallonsa kasan mai tsada ne.
“Yes ni Doctor ne how are you feeling now?”
Yana fadar hakan ya nufi gurin files dina ya bude yana dubawa sai dai babu alamar natsuwa a tare da shi in each seconds sai ya kalli kofa kamar mai tsoron shigowar wani. Ba zan iya karyata cewar shi din ba likita ba ne domin ban san a wace asibitin nakr ba, ba kuma zan iya gasgata cewar shi din likita ne ba domin ban ga alamun hakan a shigarsa da natsuwarsa ba, ko da yake likitoci ma sun fi saka kananan kaya.
“Ina mijinki?”
Ya tambaya yana kai hannunsa ya taba jikina.
“Miya faru?”
“Akwai maganar da nake son yi da shi”
Ya fada babu alamar wasa a tare da shi.
“Idan wani abun ne ka fada min likita ba ni da aure a yanzu zaman kaina ke”
Shiru yai yana kallon na dan wani lokaci kamin ya kai duka hannayensa ya rika ni ya tashe ni zaune, sai dai har lokacin ba shi da natsuwa.
“Haihuwarki nawa?”
“Hudu na samu miscarriage daya”
“When last kika samu miscarriage?”
“Ba a dade ba be wuce wata biyu zuwa uku ba”
“Mi kikai aka kawo ki asibiti mi yasa kike kuka?”
Hannu na kai na taba fuskata sai na ji sanyin hawayen dazun da ba su bushe ba.
“Wata yarinya ta fada rijiya kuma ta mutu shine abun ya firgita ni”
“Shiyasa kika samu kanki unconscious?”
Kallon rashin fahimta nai masa.
“Miyasa kake ta min wadannan tambayoyin?”
“Sun shafi lafiyarki ne, na duba files dinki na ga komai after that kina fama da cutar damuwa, kin sha maganinki yau?”
“Ban san an kawo ni asibitin ba sai yau”
Saurin tashi yai tsaye sai ya kai hannunsa a karo na uku ya taba fuska, sai kuma ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayar da ban taba irinta ba ya miko min.
“Saka min Number ki a nan zan, akwai bayanin da zan miki akan ciwonki yanzu sauri nake yi”
Tsakanin wayar da fuskarsa sai idanuwa suka kasa tsayawa kallon abu daya, fuskarsa ko kuma wayar ko tambayar da ta cika min zuciya? Mi zai saka likita ya tambayi number wayata? Wane irin bayani ne da ba zai iya yi min ba?
“Wane irin likita ne kai? Wane bayani ne da ba zaka iya yi min ba? Ni ban gane ba? Waye kai? Ka bar ni na ji da abunda yake damuna dan Allah”
“I'm sorry”
Ya fada sannan ya nufi kofar fita kamin ya fice ya sake waigo ya kalleni.
“i'm sorry”
Sannan ya fice, ni kuma na lumshe idona ina maida numfashi a hankali, tsakanin fitar Mutumen da ban san wanene da sake turo kofar dakin a shigo be wuce minti biyar da yan dakiku ba. Da sauri na sake bude idon a zato na shine ya sake dawowa sai ni arba da Abdallah ido cikin ido wani irin faduwar gaba na ji wanda ban taba jin irinsa ba, sai na ji yayi min wani irin kwarjini kimarsa ta cika ido, hakan yasa ni kawarda kaina daga barin kallonsa har ya karaso kusa da ni, yawo ya rika min da hannunsa a fuskata kamin ya kai hannunsa ya taba ni.
“Halimatu....”
“Na'am”
Na amsa ba tare da na kalleshi ba, ina iya jiyo sautin fitar iskar bakinsa kamin ya kai hannunsa ya daga idona.
“Sannu yaushe kika tashi?”
“Ban dade sosai ba”
“Okay”
Da kanshi ya shiga ba ni kulawa kamin ya fita ya hado min tea ya dawo. Ya mika min tea na saka hannu na karba idonaa na kaina, yana ta kallona kamar be taba ganina ba, har na gama shan tea na aje kofin be dauke idonsa daga gareni ba. Dagowa nai na kalleshi a zatona zai kawarda idonsa ne amman kamar jiran yake mu hada sai ya cigaba da kallona ido cikin ido, hakan yasa sai duk na ji na tsargu.
“Yan gidan mu basa nan?”
Sai ya gyada min kai still idonshi na kaina.
“Kwananki tara a nan sai yau kika farka”
Kwana tara? Kenan ba bachi nayi ba kamar yadda nake tunani suma nai? Na tambayi kaina kamin na sake kallonsa na ce.
“Da gaske Baby Namra ta rasu?”
Nan ma kan ya gyada min yana cigaba da yi min kallon da ban san na minene ba, shigowar wani likitan ne yasa shi saurin mikewa tsaye ya saka hannayensa aljihu yana yi Doc maraba.
“Ya jikin nata?”
“Da sauki.... ”
Haka Abdallah yai ta ba ni kulawa fiye da yadda na cancanta, sai dai hakan ba karamin taba ni yai ba, miyasa Abdallah zai yi ta bani kulawa bayan na zabi auren dan'uwansa sama da shi? Bayan na yi masa zargin shi yai fyade? Anya na cancanci girmamawa da kulawa daga gareshi?
Duka yan gidansu yan'uwa na kusa da kawaye na sun zo ganina ciki kuwa har da mahaifiyar Aminu, ban da mahaifiyata, ko baba da bashi da wadacacciyar lafiya sai da ya zo ganina amman ban ga mahaifiyata ba, idan na tambaya sai ace min tana gida tana miko min gaisuwa hankalina be kwanta ba sai da nai waya da ita muka gaisa sai dai a yanayin da na jita kamar ba lafiya ba. Aisha da Hafiza ne suka labarta min yadda Mama da Baba sukai da mahaifin Baby Namra da kuma zirga zirgar gaisuwar da suka rika zuwa yi.
Kwana na biyu asibitin aka ba ni takardar sallama, a ranar da aka sallame ni a ranar Aminu ya kawo min ziyara, ba karamin mamaki ya kamani ba da nai arba da fuskarsa, domin a yanzu bayan Mahaifin Baby Namra babu wanda na tsana kamar shi, su biyun nan bana kaunarsu a rayuwata. Be zo min hannu biyu ba yayi min siyayya mai yawa, bayan mun gaisa be sake ce min komai ba kamar mai kunyata sai wani sunsun da kai yake baya son kallona. Nima ta bangarena ban da kallon tsana babu abunda nake masa, ko ya jikin da ya ce min kasa amsawa nai sai Husna ce ta amsa masa shi kuma ya rike hannun Adnan yana ta wasa da shi gwanin kunya. Muna haka Abdallah ya shigo wani tsaya yai cak ya kalleni ya kalli Aminu.
“Waye wannan?”
“Mahaifinsu Namra ne?”
Aisha ta amsa masa.
“Daman Namra tana da uba? Miya kawo shi nan? Naga dai ba Namra ce bata da lafiya ba mi ka zo yi?”
Dagowa Aminu yai ya kalleshi.
“Na zo duba jikinta?”
“Sai yanzu kake damuwa da jikinta? Lokacin da take gidanka ka kula da ita ne? Dan Allah mana tashi ka fice ko na saka a wulakantaka yanzu nan”
“Akwai alaka a tsakanin mu ba ka isa ka raba wannan ba, so ko ka so ko ka ki dole ne alaka ta cigaba da tafiya har a bada saboda akwai yaya a tsakaninmu”
Aminu ya fada yana mikewa tsaye
“Yayan da baka damu da su ba? Yaran da kanenka ya lalata yarka ka kasa yin komai? Malam zo ka wuce”
A fusace Aminu ya fice daga dakin, aiko Abdallah kamar jira yake sai yai kaina da masifa kamar zai cinye ni.
“Tsakanin ke da shi ban san waya fi wani hauka ba, taya mutumen daya aureki ya raba ki da danginki ya kuma can ya wulakanta ki ya ci zafinki ke da yar ki yanzu zai zo dubaki har ki saurareshi? Wace irin mahaukaciya ce ke? Ko sonshi kike ne? Son shi kike?”
Yana ta maimaita min tambayar son sa na ke yafi a kirga be yi shiru ba har sai da na amsa masa a fusace hawaye na sauko min zuciyarta cike da wani irin bacin rai da bakinciki marar misaltuwa.
“Eh son shi nake shikenan?”
Yawo yake da idonsa a fuskata kamin ya gyada min kai.
“Yes shikenan....!”
Ya fice ya bar a ni a dakin ni da Aisha ban san lokacin dana fashe da kuka ba.
ABDULHAMID POV.
A natse ya shigo ya falon ya zauna bayan sun gaisa da Hajiyarsa sai shiru ya biyo baya alamar akwai damuwa a tare da shi, sai dai Hajiya bata lura da hakan sai aikin motsa furarta take.
“Hajiya mi yasa baki taba fada min cewar Abdallah yana son Halimatu ba?”
Da sauri Hajiya ta juyo ta kalleshi.
“Wace irin magana ce wannan? Taya Hussein zai so matarka? Wacce ka rabu da ita”
“Wallahi Hajiya zan iya dafa miki al'qurane cewar Abdallah yana son Halimatu, sai dai abunda ban gane ba kamin na aure ta yake son ta ko kuma bayan na aureta? Ko kuma bayan rabuwarmu?”
Hajiya ta aje kofin furar tana dan murmushi tace.
“Ba haka ba ne Husaini yana tausayinta ne kuma.... ”
“Abunda yake mata ya wuce tausayi Hajiya, ni ba mahaukaci ba ne na fahimci komai yanzu, kuma na san ke ma kin sani”
“Ni ban san komai ba kuma Husaini ba son Halimatu yake ba, hasalima duk wani taimako ita ce take neman yai mata”
Hajiya na rufe baki Abdallah na shigowa dakin fuska babu annuri ya kwaso fushinsa na asibiti ya shigo gidanta da shi. Har ya zauna be cewa kowa uffan ba, kamar ya san zancen a ake, sai dai a badini kalaman Halimatu ne suka taba masa zuciya. Hajiya ta watsa mata wata uwar harara kamin ta rufe shi da fada.
“Daga ina kake?”
“Asibiti”
Ya fada yana dan sakin fuskarsa shi sai yanzu ma ya ankara da ya shigo babu sallama kuma be gaishe da Hajiya ba.
“Abunda kake yi wa Halimatu yayi yawa Husaini gashi nan har dan'uwanka ya fara zarginka.... ”
Abdulhamid yai saurin tarar numfashinnta.
“Ba zargi nake ba Hajiya zahiri na gani, kawai abunda na masa ganewa, shin kamin na aureta ne yake sonta ko kuma bayan na aureta ne?”
Abdallah ya kalli Abdulhamid with confused.
“Saboda kawai ina taimakonta sai ya zama ina sonta?”
A take Abdulhamid ya daka matsa tsawa abunda be taba ba.
“Sonta kake Abdallah, ni ba mahaukaci ba ne abunda kake mata ya wuce taimako, kuma abun kunya ne ace na saki mata ka koma kana bibiyarta”
Tabe baki Abdallah yai.
“Daga kai har Aminu ba ku dace da zama mata kamar Halimatu ba gaba daya ba ku da hali ba ku da tunani... Kuma ba ku da tausayi... ”
“Eh sai kai gwani, je kai yi campaign ta aure ka”
Abdallah ya mike tsaye a fusace.
“Wai miye damuwarka da taimakon da nake yi ma mata ne? Ka riga ka ji baka bukatar zama da ita ka sake ta, to miye damuwarka da ni ko ita? Baka san cewa ina taimakon Halimatu tun kamin ka aureta ba?”
Abdulhamid ma ta mike tsaye.
“That's mean kana sonta tun kamin na aureta kenan? Miyasa ka bari na aureta bayan ka san kana sonta?”
“Wai minene matsalar ka Abdulhamid? Abdulhamid?”
“Kai ne matsala Abdallah? Taya taya taya zan saki mata twins brother naya rika bibiyarta?”
Abdulhamid ya fada cikin daga murya.
“Haram nai ko kuma taimakon da nake mata ne ba dace ba?”
“Ana barin halak ko dan kunya, kuma ko dan gudun zagin mutane, kuma ni cin fuska ne a gareni kuma abun kunya a gareka”
“Bana gudun zagin mutane, kuma wata halak din take baruwa Abdulhamid, wata halak din...!”
“Husaini......! ”
Tsawar da Hajiya dakawa Abdallah ne yasa Abdulhamid ficewa daga falon a fusace.
“Enough is enough, so ba hauka ba ne kana ta wahala akan yarinyar da ta kasa daga kai ta kalli soyayyarta a idonka, da gangan ta take soyayyarka ta auri dan'uwaka, ba ka da hankali ne kai? Yanzu hakan da ran dan'uwanka ya bace ya maka dadi kenan? Baka da magana sai ta Halimatu baka da time sai na Halimatu, baku taba fada da junanku ba sai akan yarinyar, to ya isa haka an kai karshe”
Ta karasa hawaye na sauko mata, Abdallah dai be ce komai ba all what he try to do ya saukar da fushinsa ya samu natsuwa.
“Daga yau sai yau, ban yafe ka sake shiga safgar Halimatu ba, ban yafe ka sake taimakonta da komai ba”
A rikice ya girgiza mata kai da sauri sai ta daga masa hannu.
“Fita ka ba ni guri”
Hannunsa ya saka ya dafe kansa kamin ya juya da sauri ya fice daga gidan gaba daya....
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣4️⃣
“Kai ma wani irin ka zama ne Aminu? Kamar ba kai ba? Har ka tsaya wani katon banza ya ci maka mutunci akan matarka ka kasa ramawa sai yanzu zaka zo nan kana wani huce haushi kana fada min? Haka yarinyar ta saka gaba wai ba zaka maida yaranka a gidanka ba kuma ka saka mata ido ya biye mata sai kace ba kai kake aurenta duk ka bi ka zama wani irin mutun”
Uffan be ce ba har Hajiya ta gama yi masa fadan, shi kansa a yanzu ya san ba kamar da ba ne, duk wani kuzari da kazarkazar irin nasa yanzu babu shi a tare da shi, tun da ya auri murja komai