Showing 96001 words to 99000 words out of 217237 words
ta daka masa.
“Bata ba ni ba...! Bana kaunar yarinyar nan Husaini, ita kadai tasan bakin nufin da ke zuciyarta shiyasa take haduwa da abubuwa, da gangan ta taki soyayyarka ta auri dan'uwaka, ta barka kana ta wakenta, shi kuma yana can zuciya cike da kuncinta, ai ko dan hallacin da kake mata be kamata tai maka haka ba, ta san kana son ta kuma yar ta yarda ta auri dan'uwanka bayab kuma ta san ba da zuciya daya zata zauna da shi ba, ko da ma zaman ya yiyu da wane ido zata kalleka? Ina da tabbacin Halimatu taja Hassan a jikinta ne ta nuna masa zata aureshi saboda ta musguna maka, ashe ba kai kadai tai niyar ciwa mutunci ba duka ku biyun ne, ina da tabbacin Hassan ba zai taba yafe maka ba idan har ya gano ka taba sonta kuma ka bari ya aureta, taya zan so yarinyar Husaini ka fada min, ku yan biyu ne a mahaifa daya kuka rayu, ciki daya kuka fito a rana daya ta sani kuma ta aikata wannan abun? Ba yanzu ba, gaba na ke hange tsabanin da mahaifinku yake gudun kar ku samu kuna daf da rusgawa a wannan ramen matukar baka cire kanka daga dramar wannan matar ba”
Ya girgiza mata kai.
“A'a Hajiya, kaddarar ce a haka, ina da tabbacin da ni ta aura da ta samu jindadin da ta rasa har ma da doriya, amman wahala da bakinciki be kare mata ba shiyasa ta auri Abdulhamid sai waenan abubuwa suka faru da ita”
Wannan karon kallon tsoro Hajiya tai masa.
“Na bonu wannan wane irin abu ne Husaini? Wani irin so kake mata haka?”
Hajiya na masa tambayar ya lumshe ido ya dora kansa saman kafarta ta dama yana sauke ajiyar zuciya.
‘Wani irin so ne, wanda hannu be isa ya rubuta ba, ba ki ba zai iya furtawa ba, zuciya ta cika da kaunar Halimatu, rai na ta aikin begenta ta mamaye illahirin jiki da tausayinta, babu gurbin ganin laifinta, balle kiyayya ta samu muhalli...’
A zuciyarsa yake wannan maganar a fili kuma sai ya bude idon ya dago kansa ya kalli Hajiya ya ce.
“Tausayinta kawai na ke”
“Ka fara bani tsoro, duk yadda na ke tunanin abun nan ya wuce nan, sai dai ina gargadinka kar ka kuskura ka bar dan'uwanka ya san cewar wata alaka ta taba shiga tsakaninku”
Shiru yai na few minutes.
“Hajiya kin san miyasa na zo yanzu? So nake ki saka Abdulhamid ya maida aurensa da Halimatu”
Kallonsa Hajiya ta tsaya yi kamin ta mike tsaye.
“ Ada dai ina maka kallon mai hankali da tunani, to yanzu na gano baka da shi, Halimatu ta dauke ta tafi da shi, ai zamanta a gidan dan'uwanka ma hatsari gareku sai yanzu na gano, kuma Al-hamdulillah da ya saketa Allah ya hada kowa da rabonsa”
“Wallahi Hajiya tana bukatar Abdulhamid a kusa da ita, dazun ma da ya rasa tunaninta maganarsa take min, hannunwanta ta nuna min ce min take na kalla na ga yadda Abdulhamid ya rabu da ita, ya kasa yadda da ita ya kasa riketa....”
Tabe baki Hajiya tai.
“Wani makircin sai mata, kai miya kai ka gurinta?”
Be boye mata komai ba, ciki har da marin da Ahmad yai mata.
“To Allah ya kyauta yai mafita”
Shine abunda Hajiya ta fada ta shige dakinta, ta kasa samun muhallin da zata sake kaunar Halimatu a ranta, ada kam tana kaunarta sosai amman ban da yanzu da take ganin kamar Halimatu na son tarwatsa mata kan yaya ne. Sai 10 ya bar gidan bayan ya yanke shawarar tunkarar Abdulhamid kai tsaye da maganar.
AHMAD POV.
Ya kasa barin kowa yai jinyar yarsa ciki kuwa har da mahaifiyarsa, zuciyarsa ta cika da rauni har yake ganin idan ya daga kusa da Baby Namra zai iya rasata, mutuwar mahafiyarta yake tunawa and think he's not ready to bear the pain.
After yayi losing mahaifiyarta ace yanzu ita ma ya rasa ta? The pain was almost more than he could bear.
Tun da aka shigo da ita ICU bata motsa ba, yana ganin numfashinta yana tafiya yasan yarsa tana da rai, amman ba shi da tabbacin za ta tashi.
Iskar bakinsa ya busar yana neman ta inda iska zai shiga hancinsa ya huda zuciyarsa ya zauna ko ya samu sassauci. Be taba jin ya tsani wata hallita ba kamar yadda ruhinsa ya cika da tsanar Halimatu. Abubuwa mabanbanta zuciya take raya masa, wata kila wulakanta masa Y'a akai har ta kai ta je waje ta fada rijiya, wata kila ma tsawa tai mata shiyasa ta ji haushi ta fada rijiya, ko kuma ta koreta daga gidan ita kuma taje gurin rijiyar, what if yarta ce ta jefata? Ya mai akai ta fada rijiya?
“Ki yi addu'a kawai yata ta rayu, ya rabb pls save me”
Ya furta yana maida numfashi da karfi, sannan ya kalli tafin hannunsa, wanda tun a lokacin da ya mare Halimatu hannunsa yai sanyi har yanzu, maybe because be taba marin mace ba sai yanzu kusan shi a rayuwarsa ma be taba dukan kowa ba sai ita. Ji yake ya zama wani irin mugun mutum idan ya tuna ta, yadda zai sarrafa rayuwarta idan yarsa ta mutu kawai yake tunani, kamin ya kai hannun nasa ya rike hannun yarsa..........
Runtse ido yai be bude ba sai da Hajiya ta shigo tare da likitan da suka fita dazun.
“Gwarzo ya kamata kaje gida ka huta fa, 12 ta yi”
“Hajiya ina son na maida ita Abuja a akwai wata asibiti a can wata kila za ta fi samun kula fiye da nan”
Likitan ya matsa kusa da Namra da sauri ya taba ta, babu alamun numfashi a tare da ita, a take hankalinsa ya tashi ya fara bata taimakon gaggawa amman mai kira yayi kira wanda ya bada aro ya karbi kayansa, fita yai ya shigo da wasu likiton abunda ya kara tadawa Ahmad hankalin kenan, ta yadda ya ga fuskar ko wannensu da yadda suka ja zanen asibitin suka rufe ita sai ya zuba hannayensa aljihu ya daga kansa sama ya rumtse ido.
“Na yi imani da kai Allah, kai kake kashewa ka raya, La'ilaha illallahu..... ”
Ya furta yana jin kamar babu komai a zuciyarsa, duk kuwa da ya kasa gasgata yarsa ta tafi ta bar shi da gaske. hajiya kam fashewa tai da kuka tana ta salati har ta kasa tsayi sai da aka fito da ita daga dakin.
Dafa shi da Doc Nura yai ne yasa shi bude ido ya kalleshi.
“I'm sorry Gwarzo take heart”
“Da gaske ta rasu?”
Ya gyada masa kai sai ya runtse ido, ya bude yana murmushi.
“Subhanallah”
Ya juya ya kalli gawar Baby Namra, sannan ya sake kallon Doc Nura.
“Dan Allah ka taimaka ka kaini gida i don't think zan iya driving”
Har zuwa lokacin da ya fadawa Doc Nura haka, be ji komai a ransa game da mutuwar yarsa ba, ya yarda ta mutu amman be ji zafi ko jin kewa ko tausayi a ransa ba, be kuma san da dalilin hakan ba. Wani yanayi yake jin kansa ba damuwa ba bakinciki.
A motar asibiti aka saka baby Namra, shi kuma ya shiga Motar Doc Nura Hajiya da darebanta kuma suka shiga nasu motar, aka baro motar Ahmad asibiti har sai da direban ya dawo ya dauka. Hajiya ce da kanwarsa suka kira familynsu suka sanar musu mutuwar Baby Namra. Hajiya na aikin hawaye yarta na rusa kuka wato kanwar Ahmad wacce ta shaku da Baby kamar wata kawarta,
Ahmad kam part dinsa ya shiga ya kwanta saman gadonsa rairaim ya lumshe idonsa yana maida numfashi a hankali. Wayoyinsa na ta ringing amman ya kasa ko da motsawa balle ya dauka....
AMINU POV.
Zaune yake Sa'adatu na kwance saman jikinsa hannunsa a cikin rigarta yana ta wasa da kirjinta, sam baya jin komai ba ya jin cewar abunda yake aikata akwai zunubi duk kuwa da kasancewar yasan sakamakon mu'amala da matan banza balle mace mai aure kuma kawar matarsa.
Haka yake a bangarenta bata jin cewar cin amanar mijinta take, ta dauki alhakin Allah da na mijinta ga kuma na yayanta hakan be taba damunta ba, taba taba jin ko ras a ranta zuciyarta tana nishadantuwa da alfasha kamar yadda shi ma yake ji.
“Wallahi na rasa kwarin guiwar da zan fada mata cewar zan dauko yayana”
“Wai kai wani irin tsoro kake mata ne? Tana matarka amman ko magana zaka mata sai ka rikice”
“Wallahi nima ban sani mugun tsoronta nake kamar mutuwa”
Ta tabe baki sannan ta tashi zaune.
“Ni dai dan Allah ka yi duk yadda za ka yi ka dawo da Halimatu, ta zauna cikin yayanta, daman can ban jidadin rabuwarku ba domin bana son naga ana raba mace da yayanta, dan tsabani kadan daga tambaya fita unguwa sai ka saketa”
Iskar bakinsa ya bursar domin yasan shi ya fada mata haka cewar ya saketa saboda ta fita unguwa ba da izininsa ba. Amman yanzu yana son ya dawo da ita ko dan arzikinsa ba yana jin kamar yafo samun natsuwa yayi yadda yake so a lokacin da yake auren Halimatu ba kamar yanzu ba, uwa uba kuma ga arzikinsa ance yana tare da ita. Wayarsa ya dauka ya soma lasawa yana fadin.
“Zan dawo da ita dole ma ne na dawo da ita, amman yaran zan fara karbewa tukuna yadda take da shegen son yara dole ta biyo su”
Bayan ya fadi haka ya kara wayar a kunne.
“Babyna ya kike”
“Lafiya kalau Baby kana ina?”
“Ina gurin aiki amman yanzu zan iso gida”
“Sai ka iso love you”
“Love you too”
Ya aje wayar yana tuna lokacin da yake auren Halimatu, at any time zai iya shiga gidansa kuma sai a time din da ya so dawowa zai dawo ba kamar yanzu ba, da wannan ta saka masa ka'idar indai zai dawo gida ya rika kiranta yana sanar mata, and be isa ya dawo pass 9 ba, a yanzu gida yake sallah isha'i wani lokacin har da magariba ma, be isa ya shirya tafiyar karya ba, balle har ya dauki wata macw su je tare, shi yake batawa Halimatu rai amman tai ta bashi hakuri, ba kamar wannan ba da ita zata bata masa ran kuma ya bata hakuri wani lokacin har da kukansa, gaba daya rayuwa ta masa juyin masa jindadi yai masa upside down. Shi kansa yanzu ya kasa gane kansa ga tsoronta ya cika masa zuciya ko magana zai mata fargaba yake.
Mikewa yai tsaye yana sauke ajiyar zuciya.
“Ya kamata na je gida yanzu, idan kin gama ki rufe dakin ki basu makullinsu”
“Okay”
Ta fada yana gyara rigarta.
****
Murja na aje wayar ta kalli Sadi tai saurin sauka ka gado.
“Gashi nan dawowa”
Shi ma zabura yai ya sauka daga kan gadon ya dauki rigar shaddarsa ya saka.
“Abunda muke fa nake tunanin wata rana asirinmu zai tonu, shiyasa na ce miki mu rika haduwa wani gurin kar wata be kira ba ya riske mu”
“Ni fa ba zan iya yawo boye boye ba sai a fara cewa ana ganina ina yawo, amman kai idan ka zo wa ya san abunda ya kawo ka gidan yayanka? Kai dai ko ka gaji da ni ne?”
Bakinsa ya kai yai mata kiss
“Ina zan gaji da ke Murja, tun kina waje ban gaji da ke ba balle yanzu da kike gidan yayana”
“To ka tafi dai kar ya tararda kai sai mun yi waya”
Ta fada tana turashi, ba musu ya dauki keys dinsa da wayarsa da ya saka a silent ya fice da sauri ita kuma ya nufi wardrobe ta dauko zane ta daura sannan ta bude karamar jakarta ta dauko kullin wani abu ta nufo kitchen da shi, kular miyar taushe ta bude ta kwance abun ta zuba kadan sannan ta saka spoon ta garwaye miyar ta fito da sauri ta maida maganin a muhallinsa ta shiga bandaki.
HALIMATU POV.
Me yake faruwa da ni? Da gaske hauka na ke a yanzu? Tsantsar damuwa ce ko kuma shaye-shaye da na fara ne ko kuma gamu nai? Har na shigo cikin gidan mu bana raba dayan biyu ba. Dare ne a lokacin amman a gidanky kamar rana, domin kowa yana farkewa cikin da har da yayana. Sannu kowa ke min suna ta min kallon tausayi, ni kuma na amsa na zauna q tabarmar da aka shimfida tsakar gidan.
“Momy...”
Muryar Namra ce da na kalleta sai ta kara boya bayan Aisha tana hawaye, can kuma ta leko.
“Momy dan Allah ki yi hakuri karki da ke ni, Wallahi ba ni na jefata rijiya ba, ita ce ta hau taba dirowa tana hawa shine murfin ya balle ta fada ciki Wallahi ba ni ba ce”
Ta fada cikin kuka kamin Inna ta karba mata.
“Dan Allah karki mata komai Halimatu, tun dazun take dakonki, ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce idan kika dawo yanka ta za ki yi, ki dauki abun nan a matsayin kaddara”
Idona ya cika da hawaye tausayin yata ya kama ni, sai na mika mata hannu alamar ta zo.
“Ba za ki min komai ba”
Na gyada mata kai sai ta tako ta zo gurin ta kama hannuna nawa ni kuma na jata jikina na rumgume, ni da ita muka fashe da kuka a tare. Ashe ba mu kadai ba, har sauran kanena da Inna sai da sukai hawaye ban lura sai da na tashi zan je dakin Mama.
Wani abum hamdallah a lokacin da na shiga dakin Mama sai na tararda ita a kwance magani a gafenta da ruwan zafi, daman can na san tana da hawan jini sai dai ba kasafai yake tashi ba sai idan wani abun ya faru ko ranta ya bace sosai, wannan karon na san tashin hawan jinin nata baya rasa nasaba da abunda ya faru. A gafen gadonta na na zauna kasa na dora kaina a saman gadon ina bachi ina kuka, Adnan ya shigo ya dora kansa saman cinyata sai kai hannu na dafa kansa.
“Bana da sa'ar komai a rayuwata, ko a lokacin da na haife ku mahaifinku ce min yai na tara masa yaya, zan tsofar da shi....”
Tuna ba ni kadai na ke ba yasa na yi saurin yin shiru sai dai hakan be hana Adnan fahimtar yarena ba.
“Kamar yaya Momy”
Hannu na kai na rufe bakina na hade yawu. Sai ya dago ya kalleni.
“Momy dan Allah ki daina kuka”
Ya fada yana kokarin fashewa da kukan. Hannu na kai na kama fuskarsa na rike.
“Adnan kai na fara haihuwa Allah ya raya min kai, ya inganta rayuwarka yai maka albarka ba baka ikon kula da kanenka ko bana raye”
“Ameen”
Mama ta amsa daga kwance da take tana kallona. Saurin share hasayena nai.
“Ashe kin farka ya jiki?”
“Ya na ki jikin?”
Shiru nai na wani lokacin ina kallonta kamin na amsa.
“Na ji sauki”
Sai ta tashi zaune cikin rashin kwarin jiki ta shiga bandakin da ke cikin dakin.a zaune nai bachi duk yadda Mama ta so na kwanta sai na kasa ko na kwanta ma bachi baya daukata hakan yasa na tashi nai alwala na raya daren da nafila. Misalin hudu da rabi nai sallamar karshe a lokacin da na daga hannuna na yi kirari ga Ubangijina nai salati ga annabi na sai na rasa mi zan fara roko, lafiyata ko ta Baby Namra ko farinciki ko gushewar damuwa?
“Allah ka min mafita ka tsaya min, ka isar min a komai da komai ka zama gatana, ka yafe min laifukana, ka sadani da rahamarka”
Bayan na gama na sake rufewa da salatin Annabi, ban tashi daga gurin ba har aka kira sallah asuba, bayan na gama sallah na dauko qur'ane na soma karantawa har bakwai da yan mintuna sannan na tashi, ina jin kaina na juya kafafuwana kuma sun yi nauyi kamar yadda idanuwa sukai.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Baby Namra ta rasu gashi ana sanarwa a Zamfara redio”
Shine abunda ya dira a kunne na da muryar Salma. Sai ni ma na karba mata a Hankali daga cikin dakin da nake tsaye.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Sai nai bayabaya har na kai jikin ginin dakin na jingina, hawaye suka ce min salamu alaiki......
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣2️⃣
Barka da Sallah Allah ya maimaita mana 🙏❤
Hannu na kai na rufe bakina, wannan karon ba kuka ido da baki kawai nake ba har da zuciya da kwakwalwa da jikina amsa amo yake. Kuka nake ta ko'ina irin kukan da ban taba yi ba, irin kukan da ban taba sani yana tare da ni ba karkawar nake kamar wacce ta shekara a cikin kankara hakorana na hadewa da juna suna wata kara, wani kalar hayaki nake ji a cikin kaina.
“Ashe har yanzun kukan be kare ba Halimatu”
Mama ce tai maganar sai na dago na kalleta tsaye take jikin kofar dakin da nake ita ma kuka take kamar ni. Kai na gyada mata kamar wani abun arziki sai kuma na ji ana fisgata kafafuwana suka kasa daukata, wani farin haske ya baibaiye idona tashin hankali da nake ji a yanzu bana jin cewar ko daya daga cikin yayana ne ya mutu zan samu kaina a yadda na samu kaina a yanzu.
“Ki ce Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Mama ce take fada min abunda zan fada, ba dan ina ganin fuskarta ba, ba fuskarta kadai ba komai bana iya gani a yanzu sai dai ina jin hannunta a jikina tana rike da ni. Unkuri nai da zimmar na bude bakin na furta abunda ta umarce ni sai bakin yai min nauyi kamar ban taba magana da shi ba. Daga lokacin ban sake sanin inda nake ba sama nake kasa nake duniya nake ko a lahira ban sake sani ba, sai duniyar ta duburce min hankalin ya tafi numfashin ma yai min dogon zango....
AHMAD POV.
Tun bayan da aka kai Baby Namra a gidanta na gaskiya be sake zama a aje ba, duk wanda ya kira wayarsa ko ya zo gidan da sunan masa gaisuwa ba zai dauka ba ba kuma zai fito ba. Wani abu yake ji a tare da shi shi ba tsoro ba ba kuma fargaba ba, baya son ayi masa gaisuwar mutuwar yarsa, har yanzu kuma ya kasa saka komai a bakinsa bayan ruwa, ya kuma kasa jin komai a game da mutuwarta. Ita kanta Hajiya a yanzu tafi shiga tashin hankalin