Showing 12001 words to 15000 words out of 217237 words

Chapter 5 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

163

ni, Momy dan Allah ki yi hakuri”

Ta fada cikin kuka tana yarfar da hannu. Mikewa nai tsaye fuska a hade na ce mata.

“Kin san idan kika min laifi dukanki na ke ko? To yau yankaki zan yi kamar rago na soya namanki na zubar a bola”

Ina fadar hakan na juya ya fice daga bandakin na sauko kasa gabana sai dukan shida-shida yake tsabanin uku-uku da na kowa ke yi. Kitchen na nufa na dauko wuka na hawo saman na shiga dakin sai an samu ta fito daga bandakin ta labe gefen gado tana ta rusa ihu.

“Momy dan Allah ki yi hakuri karki kashe ni bana son na mutu dan Allah ki yi hakuri”

“To fada min mi ya same ni a nan”

“Idan na fada shi ma Baba Sadi yanka ni zai yi, wayyo na shiga uku Abbah..... ”

Kasa magana nai jin abunda ta fada gaba daya sai jikina ya kara yin sanyi, ga wani uban kuka da take kamar zata shude. Aje wukar nai na mika mata hannuna.

“Taso zo nan”

Sai ta girgiza min kai.

“Aa yanka ni za ki yi Momy ba zan zo ba”

“Ba zan yanka ki ba ni mahaifiyarki ce ba zan iya yankaki ba, idan kin fada min abunda Baba Sadi yake miki ba zan miki komai ba”

“Idan kuma na fada shi ma yanka ni zai yi wayyo Allah na”

“Ba zan bari na yanka ki ba, kuma ba zan fada masa cewar kin fada min ba, wannan sirrin mu ne ai ba zan fadawa kowa ba”

Na fada ina karasawa kusa da ita a hankali, sannan na kai hannu na rika ya dawo da ita saman jikina na rumgume har lokacin kuka take jikinta na ta rawa sosai. Kyale ta nai sai da ta ci kukan ta a jikina sannan na dago ta na share mata hawayenta ina mata murmushi ta yadda hankalinta zai kwanta ta yarda da ni.

“Yata Namra fada min mi Baba Sadi yake miki?”

“Ba zaki min komai ba?”

“Eh kuma ba za su fada masa ba ai wannan sirrin mu ne mu kadai ko Abbah ba zan fadawa ba”

“Yace idan na fada sai ya yanka ni kuma na kone gawata kuma yace idan an mutu can zan samu wuta tai ta kona ni ciki kasa”

“Karya ne kawai yakr baki tsoro ne, fada min zan siya miki duk abunda kike so”

Shiru tai na wani lokaci sannan ta sake daga kanta ta kalleni.

“Momy ni bana son na mutu”

“Ba zaki mutu ba idan kika fada min”

“A nan yake saka min abu”

Ta nuna gabanta tana kallon fuskata, sai nai mata murmushi ina nuna gurin.

“A nan?”

“Eh da kuma abaki yake saka min wannan abun”

“Shine wani abun tsoro? Ai ba wani abun ba ne, da har zaki ji tsoro”

“Amman shi yace karna fada”

“Shikenan abunda yake miki?”

Na tambaya ina jin kamar kuka sai kubuce min, su kan hawaye tuni na fara yinsu.

“Eh da hannu yake saka min sai jiya da wacan monday ya sska min abun fitsarinsa a nan, kuma da zafi sosai idan nai kuka sai ya ce ba zai ba ni chocolate ba, kuma idan na fada zai ya ka ni?”

“Da yaushe da yaushe yake miki haka?”

“Idan muna part dinsa sai na kore su Adnan da su Safwan yace su tafi ni kadai na tsaya wai suna masa yahaniya ni ce kawai bana masa ihu sai su tafi idan suka tafi sai ya saka min hannu a nan ko kuma ya bani yace na sha, kuma ya ce idan ban hade wannan majinar ba sai doke ni, ko kuma ya saka bakinsa a nan ya yi min yadda nake masa, wata rana kuma idan mun tafi wani gurin sai ya fita da ni ya siya min abun dadi yai min haka nan ko yace nai masa, ko ranar da muka tafi yawo sai ya aje su Safwan da Aiman a gurin wasan yara ni ya tafi da ni a mota ya saka ni na sha masa tsanar sa, tsana haka yake cewa”

Ban iya komai ba a lokacin bayan fashewa da kuka mai tsanani. Babu mace da zata labarta yadda wata macen take ji har sai ta taba kasancewa a cikin halin da wacan macen da ta taba kasancewa. Daga ni sai ire-irena mu ke iya bayyana yadda mace ta ke ji idan aka keta haddin yarta ko kuma ita kanta! Ina ma ace yau haddina ni Halimatu aka keta ba na yata ba?

“Namra miyasa baki fada min ba tuntuni?”

“Ai yace idan na fada zai yanka ni kuma na fada miki bana son zuwa can ke kuma sai ki ce sai mun tafi kamin ki dawo daga aiki”

Rasa nai abunda zan yi ko na ce mata sai kawai na sauke ta daga jikina na aje ta saman gadon na taso na baro mata dakin na dawo falo na zauna na safe kaina ina jin zuciyata kamar zata fashe. Kuka nai sosai ba na wasa ba ji nake kamar na hade zuciya na mutu na hutu gaba daya. Kamar wacce aka tsikara na tashi da sauri na koma sama na dauki Hijab dina na saka na dauki jakata da wayata na nufo dakinsu na dauke ta da kayan bachinta muka fito ko rufe gidan ban tsaya yi ba na nufi titi ina samun napep muka nufi asibiti. Har cikin asibitin hawaye nake ina sharewa gashi na yi rashin sa'a na tarar har an gama daukar suna, a karon na farko bayan na yi blocking din number Abdallah yau da kaina ba daga waya na kira shi. Bugu biyu ya dauka.

“Ko dai kin kira ki min bakar magana ko kuma ki zage ni, domin na san ina da farinjinin da ba zaki kirani ki min magana kamar yar'uwa ba”

Fashewa nai da kuka.

“Dan Allah Abdallah ka taimaka min na zo an gama daukar suna na kawo Namra ne”

“Kina ina?”

“Ina bangaren yara bakin kofar shiga”

“To zan zo na same ki a nan”

Tsakanin kashe wayarsa da zuwansa be wuce minti biyar ba, da alama yana kusa da gurin kuma ya karasa inda na ke da sauri har yana hadawa da gudu. Ganin yadda hawaye ke min zuba yasa shi tsayawa yana kallona.

“Halima lafiya?”

Kasa magana nai sai yaja hannun Namra yana dubata.

“Mi ya same ta wai? Lafiya kike?”

Hankalinsa ya tashi sosai ganin ina kuka.

“Lafiyarta nake son a abinci ka min”

Na fada ina hawaye kamar ba gobe bakina na rawa.

“Lafiyarta kuma?”

Kasa amsa masa nai sai na juya da zimmar tafiya.

“Halima?”

Na juyo.

“Lafiyar ki kuwa?”

“Ban sani ba, ina jin kamar bana da damuwa kuma ina jin kamar akwai abunda yake damuna, gida nake son naje”

“Wane gida?”

“Gida gurin Mama da Baba na fada musu”

Magana nake ni kaina ina jin kamar a mafarki nake maganar ba a zahiri ba. Tallabar Namra yai ya dorata a kafadarsa ni kuma ya rika hannuna.

“Zo muje”

Ya nufi hanyar da ya fito da ni, ni kuma ina ta binsa ba tare da nasan inda zai kai ni ba, mutumen da na ke ciwa mutunci ina zaginsa yau yana jaye da hannuna na kyaleshi.




_______________________

Tsakanin Namra da Halima wa yafi zama abun tausayi? Namra da aka lalatawa rayuwa ko kuma Halima da take mahaifiyarta kuma take rayuwa da mugun miji? 😭

Allah kasa mu dace 🙏😪
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy


6️⃣

Office dinsa ya shiga da ni, sai ya saki hannuna ya sauke Namra daga saman kafadarsa ya zaunar da ita a saman kujerarsa sannan ya rufe kofar office din ya sake rika hannuna ya zaunar da ni a dayar kujerar dake kusa da kofar, sai ya zauna shi ma yana ta kallona ya kasa cewa komai, ni ma shi nake kallo amman ba kallo na ainahin kyausa ko wani abun daya shafi jikinsa ko fuskarsa ba, kallonsa nake a zahiri amman a badini zuciyata tana can gurin tunanin yau da kuma GOBENA, har yanzu na kasa yarda ba mafarki na ke ba, har yanzu hawayen ba su daina sauko min ba, har yanzu ban daina jin sautin muryar Namra na maimaita kanta a kwakwalwata ba, ji nake kamar yanzu take ba ni labarin nan, rumtse ido nai na kulle gam ina jin kamar idan na bude zan ga komai be faru ba, ji na ke kamar ace idan na bude idon zan farka daga mummunan mafarkin da nai yi ne.

“Halima”

Can cikin kaina na ji kiran Abdallah da sauri na bude idon ina kallonsa har nunfashina na rawa kamar wacce ta farka daga bachi, da gaske ji nake kamar ace mafarki ne ba gaske ba.

“Miya samu Namra?”

Ya tambaya fuskarsa na nuna tsantsar damuwa da ganin hawayen. Nuna masa Namra din nai na kasa cewa komai, bakina nai nauyi sosai kamar an saka min dutse a ciki, wata kila kalaman da zan furta a duniya sun kare ne, domin ina jin idan har bakina zai bude da sunan magana a yanzu to kuka ne kawai zai fito amman ba magana irin wacce ko wane lafiyayen mutum yake ba. Kai nake ta daga masa alamar ita din ce ita dince kamar wanda ya sake tambaya, shi kuma ya tattara hankalinsa ya maida akaina sai yawo yake da idonsa a fuskata.

“Bana son zubar hawayen nan na ki Halima, ki bude baki yi min magana maybe i can help”

Ya fada yana dauke kansa daga barin kallona ya dafe da hannunsa yana sauke numfashin da karfi, can kuma ya mike tsaye ya nufi gurin windows din ya tsaya yana kallon waje kamin ya buga hannunsa da karfi jikin ginin gurin.

“Matsalarki duk ba zata wuce ta shegen mijin nan na ki ba, can you pls talk”

Ya fada yana juyowa ya kalleni, yunkurin bude baki nai da zimmar magana da gaske sai na kasa maganar har kuma lokacin ban daina hawaye ba kamar an rubuto min ranar kawai domin kuka. Teburinsa ya nufa ya dauko takardarda biro ya aje min a gabana.

“Rubuta idan ba zaki iya min magana ba”

_So na ke a duba min Namra fyade akai mata_

Haka na rubuta a takardar na mika masa, yana karantawa ya zaro ido ya kalli Namra da sauri sannan ya kalle ni.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, garin ya?”

Nan ma kasa magana nai sai dai na bude bakina ba kamar dazun ba da dantse har da hakorana. Barin gurin da nake yai ya nufi gurin Namra.

“Namra wa yai miki haka? Fada min ya akai hakan ya faru?”

Tana kallonsa sai ta fashe da kuka daman tun da muka shigo take alamar kukan ganin nima kukan na ke yi. Sauko tai daga kan kujera ta rugo a guje inda nake zaune ta rumgume ni tana wani irin kuka mai taba zuba zuciya, ni ma fashewa nai da kukan mai sauti na rumgume yata kankan a jikina ita kuka ni kuma, sai a lokacin na fara tambayar kaina ina tunanin abunda nai wa Sadi da zai yi ma yata haka? A kullum burina da mafarkina na tsare mutuncin kaina da na mijina da na yayana, amman yau wani a cikin familyn mijina ya keta yadda yata, ya rusa min komai.

“Miyasa zai min haka? Mi masa a duniyar nan? Me zai ji a jikin karamar yarinya kamar Namra? Kuma yar dan'uwansa? Mi yasa zai saka mu a wannan halin ni da ita?”

Magana na ke ina kallon Abdallah kamar shi zai ba ni amsar duka tambayoyina. Mikewa nai tsaye rumgume da Namra na fara zagaye dakin.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”

Haka nai ta maimaita ina jin zuciyata kamar zata rabe gida biyu, numfashina kuma yana ta kokuwa da jikina, sai na yi da gaske yake fita ya shiga. Abdallah ne ya miko hannu ya karbe ta.

“Zan kula da ita zan yi mata duk abunda ya dace ke ki zauna a nan”

Daga haka ya juya ya fice, ni kuma na nufi kujerar da sauri na zauna saboda kafafuwana da na ke jin kamar ba za su dauke ni ba, ga wani sanyi da nake jin na taso min har hakorana na son haduwa da juna. Babu wanda ya fado min a rai yanzu sai Abban Namra shi ya kamata ace yana tsaye a tare da ni muna wannan jimamin a tare ya kamata ace ya san halin da yarsa take ciki, da sauri na bude jakata na fiddo wayata na kira numbersa haka tai ringing har ta katse be daga ba, na sake gwadawa nan ma be daga ba, sai da na jira masa miss calls har hudu a na biyar ya daga a fusace.

“Wai ya akai? Ina aiki kina ta damuna da kira”

Kasa ce masa komai nai sai sauke numfashi nake, har ya gaji ya kashe wayar, wani irin abu marar misaltuwa na ji ya ratsa zuciyata ya tsaya min a makoshi, mutumen da ya fita be tambaya lafiyar yarsa ba bayan ya sa bata da lafiya yanzu kuma na kira shi yace min aiki yake ina damunsa, wane irin aiki ne wanda ya fi iyalinsa muhimmanci, wane aiki ma mutumen da yace min tafiya zai yi? A yanzu shi na ya kamata ace yana tsaye a bayana yana jimamin wannan lamarin tare da ni, shi ne ya kamata ace ya tsare min komai da ban nemi yin aiki ba da yanzu ina tare da yayana ba sai na kai su gidan wani ba, wata kila da be yi da yar wani ba da yanzu ba ayi da tasa ba. Jikina ne ya fara rawa har wayar da ke hannuna ta fadi ina ta jin wani abu na juya min a ciki kai kamar kwaro, ban san lokacin da Abdallah ya shigo ba sai muryarsa na ji.

“Halima karki jawa kan ki depression”

Kallonsa nai.

“Kwanta”

Ya fada sai na kwanta kamar daman can umarninsa nake jira. Sai ya cire rigar likitoci dake jikinsa ya rufa min.

“Abunda na ke jiye miki kenan, shiyasa tun kamin ki haifi yaran nan nai ta nuna miki cewar ki rabu da mijinki, ki kashe aurenki amman kika ji, daman namijin da be iya komai ba sai neman mata ai dole shi ma a dana yarsa, yanzu ai sai yaji idan da dadi, wani abun bakinciki ma wai kanensa ne zai masa haka? Hakan na nufin familynsu gaba daya lalatacci ne kenan! Wai ya ma san abunda ya faru kuwa? Ko kuma yana can gurin bakin neme nemen matansa?”

Haka yai ta magangunsa cikin bacin rai har yai ya gama ya fita bance masa uffan ba, daman can ba son aurena da Aminu yake ba, babu ranar da zan hadu da shi ba zai labarta min cewar ya ga Aminu tare da wata ba, kullum cikin bibiyar rayuwar Aminu yake saboda kawai ya ga aibunsa ya fada min, hakan yasa nai blocking dinsa a fb whatsapp da ma kiransa, shi kadai ne mutummen da bana jituwa da shi a cikin familynmu saboda sukar Aminu da yake min, a duk lokacin da ya fadi min cewar Aminu yana neman mata nakan karyata kuma na hana zuciyata aminta da hakan saboda kar na sakawa kaina rudani kar na saka shakku a zaman aurena da mijina. Na sha jin Aminu yana waya da mata ko na ga chat dinsu amman ina kokarin ganin ban zarge shi ba sai na dora abun akan ruwan dare da zamanin nan da wasu mazan aure suke na chat da mata a waje, duk kuwa da irin dadewar da yake a waje, sai dai kamashi da condom da jin zai yi tafiya wani garin da mace yafi komai karya min guiwa, ga kuma fyaden da akai wa Namra a yanzu, na san akwai kaddara wacce ki giftawa bawa, amman ina jin a jikina wata kila da Aminu be yi ba da ayi ma yarsa ba, domin ni dai na san ko zinar ido ban taba aikatawa ba, amman yau an yi ma yata.

Tashi nai zaune na share hawayen idona, ina jin ba Baba Sadi ba, ko Aminu ne ya keta ma Namra haddi a yau ba zan kyale shi ba, rigar Abdallah da ke jikina na aje na mike tsaye na dauki jakata da wayata da ke kasa na nufi kofa kamin na kai hannu na bude sai Abdallah ya turo kofa ya shigo tsayawa yai kallona.

“Ina zaki je?”

“Gida, ina Namra?”

“Zaki iya tafiya, idan na gama zan kawo ta”

Tsayawa nai a gurin kamar an dasa ni, sai na ji kamar ba zan iya tafiya na bar shi da yata ba.

“You can trust me, tana gurin blood test ma yanzu”

“Thank you”

Na fada sannan na ratsa ta gefensa zan wuce.

“Ke kanki rayuwarki tana cikin hadari Halima, abunda zai fi miki kwanciyar hankali is ki raba kanki da wannan mutum, gashi yanzu dan'uwansa ya maida miki Namra babbar mace!”

Wani banza kallo na watsa masa.

“Kana tunanin akwai hikima abunda kake fada min a yanzu? Kana ji a ranka ya dace kai min wannan maganar a yanzu? Na kashe aurena na fito na bar yarana a can? Shine kwanciyar hankali da kake fada min? Ko kuma na zuba masa magani ya mutu shine zai nisanta ni da shi? Kullum burinka ka fada min wata bakar magana akan Aminu, kana tunanin dadi na ke ji? Ko kuma kana tunanin hakan zai saka na so ka ne? Hakan be kara min komai ba sai tsanarka Abdallah, ba yau na nake yiwa tanadi ba GOBENA, duk abunda nake ina yi ne saboda yayana da kuma GOBENA....”

Cikin fushi na fada mishi hakan sannan na fice ba tare da sake ce min komai ba. Tun daga yanayin tafiyata za ka gane cewa ina cikin fusata, wannan karon ba kuka ne a zuciyata ba, kuzari ne irin na neman hakki ga wanda aka dannewa shi, ina jin a raina zan iya kwatarwa yata hakkinta, ko da hakan zai zama silar mutuwar aurena. Mai napep na tara na shiga be tsaya da ni ko ina ba sai kofar gida, dari biyu na ciro na bashi ban ko tsaya karbar canji ba na shiga cikin gidan.
Yan matan gidan mu basa nan kasancewar ranar akwai scul masu zuwa aiki sun tafi masu makaranta ma sun tafi kuma a isa dawowo ba, Mama ta kawai na tarar tsakar gidan Inna na can dakinta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login