Showing 21001 words to 24000 words out of 217237 words
ma Sadi kazafi ba haka nan kawai”
“Kazafi ne mana, ai kin dade kina son raba kan gidan nan, kin rasa abunda za ki yi shine kika fake da wannan waya sani ko can gurin aikin naki kika kai yarinya aka lalata sai kuma ki zo ki fake da Sadi, wai ko baki san cewar ni na haifi Sadi ba? Kuma ni din mahaifiyar Aminu ce uba daya ya haife su nono daya suka sha”
“Ko tagwaye ne su Hajiya be dame ni ba, yayanki kike tsaye a nan kina karewa ni kuma na san zafin haihuwa kuma na san zafin keta haddi saboda ni ma mace ce”
Zakiya ta matso kusa da ni tana min tsawa.
“Halima karki ce zaki ma Hajiya rashin kunya Wallahi na ci mutuncin ki”
Ni kuma na mike tsaye ina nuna ga da yatsa a fusace.
“Ke Zakiya iskanci ya tsaya a kanki, karki sake saka min baki a magana ke kanwar mijina ce ba yarsa ba, idan baki da tarbiya Wallahi zan gyara miki zama”
Ta nuna kanta
“Ni din? Ai kece marar tarbiya mai son hada yan'uwa bawan Allah yana can yana nema muku abunda za ku ci kina nan kina tada mishi hankali da yan'uwasa, ko da ya kira har kuka yake yace yana gurin aikin Kaduna amman kin daga masa hankali da maganar fyade”
“Karya dan uwanki yake miki, ba aiki yaje yi ba hutu ya samu ya dauki karuwarsa suka je can gurin hutu, abunda yake ne yaja akai wa Namra kuma aka rasa wanda zai mata sai dan'uwansa”
Hajiya ta nuna ni da yatsanta.
“Ke marar kunya, fitsararki ta tsaya kanki karki ce zaki min iskanci, ni danaba mazina ce bane, daman can baki da aiki sai kawo kararsa kullum cikin kawo kararsa kike baki taba gode abunda yake miki ba, ke da kike aiki ba ace miki mazinaciya ba sai shi? Tirrr Wallahi mugun abun ki ya biki, kuma Wallahi ki hada kayanki ki bar gidanan ko ke kadai ce mace a duniya ya gama aurenki, ki koma can cikin agolayen gidanku,kuma Yaya sai an kaiwa Sadi shi zai rikasu sai dai ki mutu, wannan zumuncin baki isa ki raba shi ba”
“Zan bar gidan nan Hajiya, amman idan Aminu ya damka min takardar sakina, ba zanje gidanmu na zauna da igiyar auren danki a kaina ba, kuma Wallahi ko ina za'aje sai na je sai na kwatowa yata hakkinta, ban san yayanki haka suke ba Hajiya da ban auri Aminu ba da Sadi be ganni ya ci zarafin yata ba, hakuri na ya kare indai aurena da Aminu na kare ko da kuwa hakan na nufin karshen rayuwata ne, tirr da ɗa irin na ki dan da za a cewa an yi ma yarsa fyade ya karyata ba tare da bincikar komai ba, ke kuma ki sako kafa ki zo ci mun mutunci ko? Kin zo ki shigarwa yayanki to Namra ma ƴa ce idan Aminu be san darajar ta da kimarta ba ni na sani kuma ba zan bar wannan maganar ba, kotu zata kwatar mana hakkinmu”
Tun da na fara maganar babu wanda ya sake cewa uffan ba kanensa kadai ba har Hajiya tsaye tana kallona, ni kaina na san na yi mata abunda ban taba ba, ko kusanyar magana bana iyawa da ita balle kuma har nai sa'insa da ita. A yadda nakr jin kaina a yau ko marina tai zan iya ramawa, domin ina jin babu wata sauran alaka tsakanina da dangin Aminu yanzu. Har Laweeza ta bude baki zatai magana sai Hajiya ta hana ta ta hanyar daga mata hannu sannan ta saka su gaba suka fice daga falon.
Faduwa nai zaune a gurin ina wani irin fuci kamar zakayan.
“Momy ni ce naja fada ko?”
Namra ta tambaya tana kallona tare da fashewa da kuka. Kallonta kawai nai sai na kasa cewa komai na mike tsaye tare da maganin da nake bata na nufi dakina, ina shiga na fada saman gadon a ruf da ciki, wani irin soya nake jin zuciyata na min bana jin kuma ba kuma za a kawo zancen dariya ko farinciki a tare da ni a yanzu ba, gaba daya bana jindadin komai ciki kuwa har da rayuwata. Ina yi awa daya a gurin sannan na mike tsaye na nufi bandaki amai nai bayan na gama na wanke bakina na fito ina shafa cikin da ke jikina, abunda be isa shigowa duniya ba na ke tausayawa wani abu na hade mai nauyi sannan na fito na nufo falo. Wani abun mamaki sai an samu Namra tana ta kuka har da shisshika kamar ranta zai fita, haka ne na nuna alamar ta ci kuka ta kenan sosai har ta gaji. Adnan da Aiman kuma suna zaune a guri daya kusa da ita sun rakube kasa kamar wasu marayu, Amal ce kawai ke ta sha'aninta da wayata da ke hannunta.
“Adnan kuje ku kwanta kunsan gobe akwai scul”
“To Momy”
Suka tashi a tare suka nufi dakinsu a natse kamar ba su ba, yaran da sai na yi da gaske suke zuwa su kwanta ko kuma su yi bachi a duk inda ransu ya so sai na dauke su na kai dakinsu. Kusa da Namra na zauna ya dago ta idonta har yayi ja tsababen kuka.
“Yar Kirki mi akai miki?”
Bata ce min komai ba sai na kwantar da kanta jikina ina ta shafa kanta a hankali. Amal na gani ta rugo a guje tana kuka, daman haka take bata kaunar wani ya taba min jiki ko ya kwanta a jikina sai dai ita kadai. Dagata nai na ajeta a gefena na rumgume ta sannan na karbi wayata. Ganin sako a saman wayar yasa na shiga messages box sunan Abban Namra ne a saman kamar yadda nai saving number. Wani irin fargaba da tsoron bude sakon ne ya kamani a lokacin. Saurin sauke Namra da Amal dake jikina nai na mike tsaye na nufi gaban windows falon rike da wayar ba tare da na bude sakon ba. Na hade yawu ya fi a kirga numfashi na ma har gargada yake zuciyata na raya min saki na Aminu yai. Cikin karfin hali na kai hannu na bude sakon.
_Ni Aminu Idrees na saki mata ta Halimatu Ibrahim saki daya a yau 4 ga watan 3, ya zama saki uku kenan babu gwara a tsakaninmu_
Ina gama karantawa na ji kamar ba a duniyar nan nake ba, ba dan bana bukatar sakin ba, sai dan saki abu ne mai kirma wanda ko baka kaunar mutum idan aka sake ka dole ne sai ka ji wani abun marar dadi ya ratsaka.
_Karki kara minti daya a cikin gidana! Karki yarda na dawo gobe na same ki a cikin gidana, kuma karki daukar min yara_
Shine sako na biyu bayan na farkon, ban san ta inda hawaye suka taru a idona har suka zubo min ba, sai jika screen din wayata suke.
“Zaki iya wannan Halimatu, wasu uwa da uba suka rasa balle ke da igiyar aure ce kawai kike rasa kuma auren mutumen da be san darajarki ba, akan yaranki ne right? Zaki iya yin komai akan yaranki, wannan be isa ya karya miki guiwa ba, be kamata ma hawaye ya ziyarci idonki ba saboda kin rabu da mugun mutum right?”
Ni kadai nake magana da kaina kamar wata tabbabiya da sauri na share hawayena, na nufi Namra dake kallona.
“Tashi muje gida”
Na fada ina daukar Amal, dakin su Adnan na shiga har sun fara bachi na taso su na saka Hijab dina na dauki jakata domin bana jin iya tsayawa daukar komai a yanzu, waje muka fito gaba daya na rufe kofar falon sannan na saka yarana gaba muka fita gate din.
Misalin tara da rabi muka isa unguwarmu wato family house dinmu, tun a waje na san Abdallah na cikin gidan sakamakon ganin motarsa da nai a waje, bayan an sallame mai Napep di na ji kamar ba zan iya shiga cikin gidan ba saboda Abdallah. Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na saka kafata a cikin gidan, babu kwalla ko kadan a tare da ni a lokacin da na shiga cikin gidan sai dai ina shiga falon nai arba da Mama da kanena biyu da kuma Abdallah sai na ji kuka ya zo min marar misaltuwa.
“Lafiya dai Halimatu”
Mama ta tambaya tana kallona da yara hankalinta a tashe.
“Mama Aminu ya sake ni.....”
Na fada ina fashewa da kuka, kanwata Salma dake kwance kan kujera ta yi saurin tashi zaune tana zaro ido, Mama kuma ta dafe kai ita da Ummi.
“Wow..... ”
Shine abunda Abdallah ya fada yana mika dukan kallonsa a gareni fuskarsa da murmushi kamar ya manta a inda yake.
________________
Saki mace mai ƴaƴa huɗu saboda son zuciya 💔😪
Anya akwai imani a zuciyar Aminu kuwa?
A matsayinki na mace ya kike auna abun nan ya kike ji a ranki?😪
Abdallah me yake yi ma murmushi? 🙄
Idan tawayensa Abdulhamid yaji ya zai yi 🤔
Anya Aminu zai barwa Halimatu yaranta kuwa?
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: https://chat.whatsapp.com/Kd8IIfbBTC824Lw3DOeKra
*GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
9️⃣
“Wannan kaddararen aure yau Allah ya kawo karshensa, ni ban ga abun kuka ba ma balle wata damuwa”
Shine abunda ya fito daga bakin Abdallah, Mama kam kasa cewa komai tai har lokacin tana dafe da kanta nima na kasa daina hawaye zuciyata tana min wani mugun zafi.
“Ummi rikata ki shiga da ita daki mana”
Cewar Abdallah yana kallona kamar ya taso da kansa din ya rikani. Salma ta taso ta zo ta rika daga tsayen da nake muka nufin dakin Mama tana rike da ni kamar yadda Abdallah ya bukata, muna shiga dakin na zauna bakin gado sai ta zauna kusa da ni tana kallona idonta taf da hawaye.
“Ki yi hakuri Anty Halima haka Allah ya so, ki dauka wannan ma yana rubuce a cikin abunda Allah ya rubuto zai same ki”
Na gyada mata kai ina ta kokarin taushe kukan da ke cina, Amal ce ta shigo ta zauna saman kafafuwana ya lafe kamar zatai kuka sai kace wacce ta san abunda ke faruwa. Salma kuma ta tashi ta fita ta barni a dakin daga ni sai Amal a nan na samu damar yin kukana iya yadda raina yake son, ina cikin kukan Mama ta shigo ta zauna bakin gado na yi zaton zata fara tambayar abunda ya faru ne ko kum ta tausaya min ko ta karfafa min kuiwa akan abunda ya faru, amman sai na ji wani abu dabam na fitowa daga bakin.
“Ai ga irin ta nan kin kashe aure tun ba a aje ko'ina ba kin fara kuka, ina amfanin wannan abun? Kin saka kanki da yayanki a cikin matsala bayan kuma kin san saki daya ya rage ba wani gyara a tsakaninku? Halima rayuwa zatai yi? Yanzu duk maganar da muka miki muka ce ki rufe abun nan sai da kika tona shi?”
Daga kaina nai na kalleta, ban san abunda take hango min ba na kokarin hanani yin komai akan abunda akaiwa Namra, na san tana gudun zaman gida a gurina kuma tana jin kwatankwacin zafin da nake ji na baro yayana a wani gidan, amman har yanzu na kasa gane dalilin na son boye maganar, indai na janyo ma yayana tsanena ina ganin kamar ba hujja ba ce.
“Ko wace Uwa Mama tana goyon bayan abunda yayanta suke aikatawa ko da kuwa abun nan marar kyau ne, na kasa ganin kuskure abunda nake son aikatawa, na san kina min tunanin mutuwar aurena ne, amman tabbas aurena mutu ko da ta wannan dalilin ba, duk yadda kike jin zafi idan wani abun ya same ni haka nake jin zafi idan ya samu Namra, saboda nima uwa ce, kin taba fada mana cewar saboda mu kika zauna da Abbah a cikin lalurar da yake ciki ta rashin lafiya, mama ya dan Allah ki fahimta nima saboda Namra ne, kuma ba dan bana son aurena ba sai dan ganin kamar mutuwar auren a yanzu zata fi sauki sama da idan yayana suka girma, Mama Aminu ya sake ni akan be yarda da abunda na fada ba, ba wai ma ya roki na boye sirrin ba ko kuma ya roki kar na kai kotu ba, mahaifiyarsa har ikirarin cewa tai sai an kaiwa Sadi Namra ya rikata sai dai na mutu, Mama ina kuke son na saka kaina na ji sanyi? Me kuka son nai a duniyar nan?”
Wannan karon hawayene yake zuba a idon Mahaifiyata, na sani kalamaina sun ratsata matuka kuma ta fahimci inda na dosa.
“Kwatarwa yarki hakki abu ne mai kyau Halimatu, amman kwatar hakki a inda kwatar yafi rashin kwatar alheri to barin shi ya fi, idan kika kai maganar nan kotu kin sani Sadi da yan'uwansa ba yarda za su yi ba, kuma za su yi komai dan su wanke shi ciki har da mijinki tunda kin ce be yarda da abun ba, daga haka maganar zata tashi sama kanki ankaro an fara buga ku a jaridu ana fira da ku, kamin a kwato miki hakkin ki sai kin sha wahala, idab kikai nasa a hukunta na shekara daya ko watanin kadan me akai kenan? Idan kuma ba ki yi sa'a ba sai a kori kararku bayan na gama fadar kin batawa yarinya suna, irin wannan abun Halimatu rufewa ake saboda rayuwar yar ki a nan gaba wa zata aura? Wa zai aureta? Mi zata je ta tarar? Ina hango miki abunda zai zame miki matsala ne nan da wadansu shekaru masu zuwa wanda ke ba zaki gani ba a yanzu, zaki batawa yarki sunane kawai a cikin kawayenta yan'uwanta da kuma wandanda zata hadu da su nan gaba, ke da Hafiza da Doc Abdallah kun kasa fahimtar abunda nake nufi ne kawai wata kila sai nan gaba, shi ma abunda ya zo yana min magana akai kenan? Wa be kamata a kyale wannan maganar ba, ni kuma na fada masa indai da yawuna za aje kotu da wannan maganar a matsayina na mahaifiyarki ban yarda ba!”
Kamar wacce aka saka da mashi haka magana Mama ta ratsa kirjina ta shiga har cikin kaina, tsakanin maganar fyaden da sakin da Aminu yai min da kuma maganar Mama sai na rasa wane yafi yi min zafi a kirji.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Na fada ina jin kirjina kamar zai fashe zuciyata ta fito waje, muna haka Baba ya shigo dakin yana turo wheelchair dinsa Inna na bayansa tana hawaye shu kuma fuskarsa na nuna tsantsar damuwar da ke tattare da shi. Ina kallonsu sai ya tuna min da wacan lokacin na baya lokacin da aka dura aurena da Aminu, lokacin da ko wace fuska take dauke da murmushi da annashuwa da jindadi.
“Halimatu ya akai hakan ta faru?”
Ban boye masa komai ba ciki har da ikirarin da Hajiya tai na kaiwa Sadi Namra ya rika.
“Wannan maganar banza ce! Taya zai sake ki ba tare da sauraren gaskiya ba kuma be yi bincike ba sannan ya ce zai dauki yaya ya kai wa kanensa? Babu wanda ya isa ya rabaki da yayanki a nan za su zauna tare da ke idan kuma yayi musu kotu zata rabu mu da shi, domin yanzu babu sauran mutunci a tsakaninmu da shi, duk abunda yake takama da shi sai na gani!”
Baba ya fada cikin fushi da daga murya kana kallonsa kasan ransa ya bace sosai, wanda ban yi zaton haka ba domin yana da wahala ka ji bakinsa maganar zamana da Aminu bayan ki yi hakuri aure sai da hakuri, na ji sanyi sosai kuma ina jin na samu kwarin guiwar rike yayana da kyau domin na samu mai goya min baya.
Sun dade suna da maganar aurena da Aminu tun daga kan haihuwa ta ta fari har zuwa yau abubuwan da sukai ta faru da kuma abubuwan da suke gani ko ji, ni dai ban ce uffan ba domin har lokacin da kennana suka shigo suka saka baki ana yi da su ban ji ina furta ko da sunan Aminu ba a zance balle kuma har nai wata firar abunda ya shafeshi, sannan suna yi an saboda su nuna min kar na damu akan abunda ya faru.
Sai kuma sha biyu sannan kowa ya nemi gurin kwanciya, a lokacin Amal ta dade da bachi a kirjina, sai da na kwantar da ita a kasa saboda fitsarin da take sannan na fito falon Mama neman su Adnan.
“Ai tun dazun Abdallah ya tafi ta su gidansa, yace can za su kwana”
Mama ta fada.
“Har da Namra?”
“Eh har da ita”
“Akan me zai tafi da ita bana son tana rabar kowa a yanzu bari na kira shi...”
Ina juyawa Hafiza ta kirani.
“Anty Halima dan Allah karki kira shi yanzu, kin san dai indan kowa zai lalata miki yara ban da Yaya Abdallah, kuma saboda yana tausayin yaran yai so karki bashi kunya a yanzu”
“Bana iya yarda da kowa akan yarana yanzu, indai har kannen mahaifinsu zai iya yin wani abu na lalata da Namra, to kowa ma zai iya lalata da ita, rayuwar ya mace a yanzu tafi ko yaushe bukatar tattali, idan na nesa be lalata maka ita ba, na kusa zai iya samu damar hakan, idon kowa ya rufe a yanzu Hafiza, ba zaki taba gane abunda nake nufi ba har sai kin yi aure kin haihu sannan za ki gane tarbiya da tsare yaya abu ne mai wahala, ban son na sake aikata kuskuren da na aikata na barin Sadi da yarana har ya samu damar yi min tabon da ba zai gogu ba har na koma ga mahallincina, da na san cewar zuwa na gurin aiki zai haifar da haka da ban yi aikin ba, da na zauna da yayana a ko wane irin hali, a ko da yaushe ina aina yadda Namra zata ji idan ta girma ta samu irin wannan labarin, ida na kuma na sake bari wani ya sake faruwa? Laifin akan wa zan dora shi?daman tun farko be kamata na yarda da kowa akan yayana ba”
Na karasa tare da saka hannuna na share hawayen idona, sannan na kai dubana gurin mahaifiyata wacce ke kallona fuskarta da murmushi.
“Kinji kwatankwacin abunda nake ji a lokacin da kike budurwa ke da yan'uwanki da