Showing 90001 words to 93000 words out of 217237 words

Chapter 31 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

199

ce kawai a hannuna ba har sai da Salma ta miko min ta ta wayar.

“Gashi ki yi magana”

Da na karbi wayar sai na rike na rasa yadda zan yi da ita.

“Ya dauka fa”

Sai nai saurin karawa a kunne.

“Hello....”

“Wake magana”

Muryar Suwaiba ce da alama wayar tana hannunta ne.

“Ni ce Halima ce Ina Abdallah”

Ta dade bata ce min komai ba har sai da nai zaton wayar ta tsinke.

“Hello”

“Bachi yake”

“Ki taimaka min dan Allah ki tashe shi, ina cikin matsala yarinyar da..... ”

Ban gama fadar abunda zan fada ba ta tari numfashina da masifa.

“Haba Halima ya kamata ki gane Abdallah fa kanen mijinki ne, duk da ya rabu da ke be kamata wata alaka na shiga tsakaninku ba, ki shafa matsa lafiya dan Allah”

“Yanzu ma in cikin matsala ne shiyasa na kira shi...”

Na fada domin kawai ta fahimci akwai dalilin kiran ba hakan nan kawai nake kiransa ba.

“To bachi yake”

Ta tsinke wayar. Kwallar idona ta hanani ganin komai, hayaniyar mutanen da suke emergency sai na ji kamar ina wata duniyar, tabbas ina jin bakina yana motsi amman ban san me nake fada ba, Salma ta karbi wayarta ko na bata ko jefarwa nai duk ban sani ba, sai kuma na ji wani na tambayar ina yayen yarinyar nan, wata kila da mu yake wata kila kuma ba da mu yake ba duk ba zan iya ganewa a yanzu wani hudu ne ya rufe min ido ga idon a bude amman na kasa ganin komai.

“Anty.....”

Can cikin a na ji muryar Salma ta kirani kamar tana wata uwa duniyar. Tassssss na ji saukar wani azababben mari a gefen kumatuna, marin da ba a taba min irinsa ba tun da uwata ta haife ni a duniya, wani zafi na ji ya mamaye min ilahirin fuskata kamar wuta, a take kafafuwana suka kasa daukata.

“Ku rike ta....”

Shine abunda na iya jiyowa shi ma kamar daga can wata uwa duniyar, ji jai na buga hannuna a wani abun mai kamar karfi sai dai ko kadan ban ji zafin ba har numfashin da ke jikina yai gaba abunsa...
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


3️⃣0️⃣

AHMAD POV.

Aikin yake ta yi zuciyarsa na gurin yarsa, hakan nan kawai yake jin cewar baby Namra is not safe, yana ta ganin kamar matar nan zata mata kallon banza ko ta fada mata magana marar dadi saboda shi, and he can't take it anymore ko akansa balle akan yarsa da yake ji da ita, zuciyarsa na ta raya masa abubuwa, he feels like ba zai sake barinta taje gidan ba zai dauke mata hankali da wani abun.

“Daga ganin matar nan bata da mutumci ko na five naira”

Ya furta zuciyarsa na kara raya masa cewar macen auren mai mutumci ba zata iya tsayawa ta fada masa magana marar dadi kamar yadda Halimatu tai ba. Sai yanzu ma yake jin shi be yarda fa tarbiyar gidansu ba kar su lalata masa ya. Mikewa yai tsaye yana kallon agogo hannunsa da ya nuna masa karfe biyar da yan mintuna. Takardunsa ya kwashe ya dauko laptop dinsa ya nufi part dinsa ya aje su a can sannan ya fito harabar gidan ya kira almu direba, Almu ya zo da gudunsa.

“Kaje ka dauko Baby inda ka kaita dazun”

“To Alhaji”

Direct bangaren Hajiya ya nufa, sai ya same ta a falonta mai mata mopping na matsa mata kafafuwanta. A one seater ya zauna yana kallon fuskar Hajiya da ke cike da far'a, wanda yake kyautata zaton nasabar farincikinta da zuwan matar nan ta dazun.

“Ka ci abinci kuwa?”

“No kin san ai idan ina aikin nan bana iya tsayawa cin komai”

“Larai tashi ki dauko kulolin na zuba masa”

“No zan ci after magrib”

Ya fada zuciyarsa na ta yi masa sake sake akan farincikin Hajiya, baya son ya tambaya tai masa maganar Ikilima ko abunda ya shafeta so he decided ya kyaleta kawai idan ma maganar da ya kamata ace ta ji ce yana zaunesa za tai masa maganar. Hannu Hajiya ta kai ta dauko wayarta ta kira direban Baby Namra bugu daya ya dauka.

“Hello Almu kaje ka dauko Baby Namra”

“Ga ni a hanya Hajiya Alhaji ya fada min ai”

“Okay”

Ta aje wayar sannan ta kalli Ahmad tana murmushi.

“Ko dan Baby ai ya kamata ka auri yarinyar nan, dan nasan yadda Baby take da rigima kamar kai ita kadai zata iya zama da ku, Wallahi dazun da mahaifiyarta na ba ni labarin irin hakurin zaman auren da tai sai ta kara burge ni”

Shiru yai kamar ba zai ce komai ba, sai kuma ya kalli Larai ya ce.

“Za ki iya ba mu guri Larai”

Da sauri Larai ta mike tsaye sai Hajiya ta ce.

“Why?”

“We need privacy Hajiya, idan muka maganar Family be kamata wani ya ji ba”

“Aiko dai ina jindadin matsa min kafafuwan nan da take”

Tashi yai ya tare a gaban Hajiya kasan carpet yaja kafarta daya ya soma matsawa.

“Hajiya ki ce matar nan ta zo miki tallar yarta kawai, ai kamata yai ace ta bari wasu su fada, kuma ni babu abunda za ku fada min da zai saka na aureta, na fada miki bana son auren matar wani Hajiya you know it”

“Wallahi wannan yar albarka ce, irin wannan mai hakuri ba har tausa sai ta min ba”

Kansa ya daga ya kalli Hajiya, ya san suna da arzikin da za su iya yin duk yadda suke so, after masu mata girki da shara da wanke wanke da gyara harabar gida da mai bawa fulawa ruwa everyday, now sukukarta take son ta rika matsa mata kafafuwanta, he just don't know why Hajiya take son mulkar sukukanta da hana su yancinsu, be isa ya siyawa matarsa abu ba ba da sanin Hajiya ba ko da ko anko ne, balle kayan sallah komai sai ta zaba ake musu.

“Hajiya.....”

Sai kuma yai shiru ya busar da iskar bakinsa, ya san mahaifiyarsa so tana da right ta yi duk yadda take so da shi ko da iyalinsa, but this time around maganin kar ayi kar a fara ba zai yarda yai auren a yanzu ba, idan ma zai yi ba bazawara ba kamar yadda take so, domin shi dai a rayuwarsa yana kyamar ragin wani, ya fi son shi ya rage maka as long as mace ta auri wani ta fito ba zai iya aurenta ba ko wacece ita a duniyar nan and no matter how much he loves her.

“Ka amince kenan?”

Da sauri ya amsa.

“No Hajiya ba zan iya auren yarinyar nan ba, I Wallahi ko hannun macen da wani namijin ya aura bana jin zan iya rikewa balle kuma har na aureta”

“Wai wannan wace irin bakar akida ce?”

Hajiya ta fada a fusace tana janye kafarta.

“Wallahi Haka Allah yai ni Hajiya, ina da masifar kishi ina da kishin bala'i ni kadai na san abunda na ke ji”

“To Allah ya raba mu da bala'i.... ”

Kamin ya amsa da Amin Almu ya shigo jikinsa na rawa cikin falon har yana kokarin faduwa, ko sallama be yi ba abunda be taba tun da yazo gidan ba Hajiya ba ko Ahmad sai da ya firgita da yanayinsa.

“Alhaji....Hajiya... An jefa Baby...Na ji ana fadin Baby ta fada rigiya”

“Na shiga uku ban lalace ba”

Hajiya ta fada Ahmad kuma ya mike tsaye da sauri yana kallon Almu.

“Wace Baby?”

“Baby Namra Wallahi yanzu na ji ana fadar hakan ina tsaye kofar gidan na aika yaro ya kirata sai yaron ya shigo gida da gudu yan..... ”

“Almu Enough...!”

Be gama ba Ahmad ya daka matsa wata mahaukaciyar tsawar da ko Hajiya sai ta ta ji zuciyarta kamar zata fado, balle shi Almu da Ahmad yake kallo kamar idonsa zai ciro. Hannunsa ya saka aljihu ya ji babu keys juyawa yai da wani irin gudu da ya manta when last yai irinsa ya shiga part dinsa ga keys din a inda ya saba aje su amman ya kasa ganinsu sai da ya rumtse idonsa.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Ya furta gabansa na kara faduwa, bude idon yai ya kai hannunsa ya dauki keys din ya fito da sauri ya nufi gurin motarsa, a yanayin yadda ya bar gidan da yadda ya hau titi duk wanda ya kalleshi ya san ba tukin hankali yake ba, ko dai ace yayi shaye-shaye ko kuma ba shi da hankali ko so yake ya kashe kansa. Cikin kankanen lokaci ya isa unguwarsu Halimatu, sau biyu kawai ya taba zuwa kawo Namra da kuma daukarta, ya san inda kofar gidan take amman be taba takawa ba sai yau, haka ya fita be ko kashe motar ba ya shiga cikin gidan su Halimatu kamar ba gidan matan aure ba.

“Ina yata take?”

Ita ce sallamarsa, sai aka rasa mai bashi amsa kowa yai cirkocirko.

“Ta fada rigiya Momy taje da ita Asibiti”

Adnan ya amsa masa.

“Wace asibitin?”

“Na ji tace fmc a napep suka je”

A nan ma Adnan ne ya bashi amsa, juyawa yai da sauri ya koma cikin motar, da wani irin karfi ya fizgeta sai da kura ta mamaye gurin. Yana shiga fmc ka tsaye ya wuce emergency ko'ina dubawa yake har ya hango Halimatu tsaye tare da kanenta biyu. Tun ka ya karasa ya rika ganinta kamar wani bakin maciji, yana isa gurin tana juyowa a take ya kifa mata mari, tangal-tangal tai tana kokarin faduwa sai mutane suka fara fadin a riketa Salma ta riko ta amman ina tuni ta kai kasa, hannunta ya daki wheelchair dake gurin.

Haba malam, haba bawan Allah Subhanallahi, sune abubuwan da suke fitowa a bakunan mutanen da ke gurin.

“Ina yata”

Ya tambayi likitan.

“Mahaifinta ne kai?”

Runtse ido yai kamar ba zai amsa masa ba, sai kuma ya gyada masa gudun bata lokaci.

“Muna bukatar jini”

“Ina take?”

Ya tambaya numfashinsa na fita kamar wanda yai wani aiki ya gaji. Da hannun likitan ya nuna masa kofar dakin.

“Tana ciki”

Da sauri ya shiga gurin, katon guri ne da ake aje mutane wasu kasa wasu saman gado ana shiga da su wani dakin likita na dubasu. Tsaye yai yana kallon yarsa kama da matacciya take masa domin bata motsi kuma babu alamar rai a tare da ita.

“Baby.... ”

Ya furta cikin tashin hankali.

“Tana da rai jini likitan ya ce a kawo sai a duba ta, sun tafi su dauko gado... ”

Be ko tsaya kallon mai matsa bayanin ba ya nufi yarsa yasa hannu biyu ya dauke ta cike da kuzari jin cewar tana da rai. Kamar wani mahaukaci haka ya fito da ita mutane sai kallonsa suke, ya sakata a mota sannan ya zagayo ya shiga mazauninsa da gudun tsiya ya bar cikin asibitin SJT hospital ya nufa da ita kasancewar ita ce asibitinsu kuma asibitin masu kudi wacce za a baka kulawa a take. Kamin ya karasa ya saka hannunsa aljihu ya lalaba wayarsa sai ya ji wayam babu komai sam ya manta da cewar a gida ya bar wayar sai yanzu da yake bukatar kiran family Doctor su.

Yana isa suka karbata a take suka fara bata kulawa, jini ne abunda suka bukata bayan sun shiga da ita ICU, kamin ya kai gurin da za a dibi jinin nasa jikinsa har rawa yake. A ana cikin dibar jinin sai ga family Doc su ya shigo gurin hankalinsa a tashe.

“Subhanallahi Gwarzo, yanzu ta kira tace na duba mata ko ka zo nan, na shiga emergency Doc Nura ke fada min an shiga da Baby ICU kai kuma kana nan, garin ya hakan ya faru...?”

Kai kawai Ahmad ya daga ya kalleshi, shi da kansa ya karancin irin tashin hankalin da Gwarzo yake ciki ya fi gaban kwatance. After an gama dibar jinin Ahmad ya riko rigar Doc Nura da idanuwansa da suka gama rikedewa ya ce.

“Dan Allah ka yi duk yadda za ka yi ka ceto rayuwar Baby, dan girman Allah”

Ba Doc Nura kadai ba duk mutanen da ke gurin sai da ta ji tausayin Ahmad, gashi dai ba kuka yake ba amman idanuwansa da jikinsa da fuskarsa sun nuna damuwarsa karara, even the way da yake numfashin kasan yana cikin tashin hankali. Doc Nura ya gyada masa kai.

“Karka damu In-Sha-Allah zata tashi”

Sai a lokacin ya sake shi, ya dafe kansa ji yake kamar ace yana da wani abun da zai yi yarsa ta dawo normal. Mikewa yai tsaye ya bi bayansa a bakin kofar dakin da aka shiga da ita ya tsaya ya jingina jikin bangon dakin ya Runtse ido, yana jin muryar Hajiya amman ja kasa daga kansa sai kokuwa yake da numfashinsa.


ABDALLAH POV.

Daure da tawul ya fito daga bathroom dan karamin tawul a kafadarsa yana goge ruwan da ke kansa.

“Waya kara ni”

Ya tambayi Suwaiba da ke zaune bakin gadonsa.

“Babu kowa”

“Amman na ji wayata ta yi ringing kuma na ji kin yi picking sai kuma kika fita”

“Ni ce na gwada kiran ina son na gane idan wayata tana aiki ne”

The way da tai masa magana sai ya ji be gamsu da abunda ta fada ba, if gaskiya ne then why da tai picking ya bar dakin? Be sake ce mata komai ba, ya zauna gaban madubi ya soma shafa mai, jin bata zo ta taya shi ba yasa ya juyo ya kalleta.

“Ba za ki taya ni ba?”

Bata bashi amsa ba, sai dai irin kallon kunar zuciya da take masa ya karantar da shi damuwarta.

“It seems like kamar akwai abunda yake damunki”

“Yes alakarka da Halimatun nan ne ya ishe ni”

Juyowa yai gaba daya ya fuskance ta.

“I thought we talk about this issue kuma kin fahimce ni”

“No i didn't,and i won't”

Kai tsaye ta amsa masa da kamar fada, mikewa yai tsaye ya dauki wayarsa ya cire password din ya shiga call list ya duba mai kiran, bakuwar number ya gani a take ya aikawa Number kira, sai da tai ringing har ta katse ba a dauka sannan ya sake kiran layin aka daga cikin muryar kuka Salma take magana.

“Hello.. Ya Abdallah”

“Miya faru?”

Ya tambaya ba dan ya san mai maganar ba, sai dai ita Salma tana da number sa.

“Anty Halima ce sume”

Gabansa ya fadi.

“Ta suma kamar ya?”

“Dazun ba Anty Halima ta kira ka ba? daman muna asibiti wannan Namra ce ta fada rijiya shine babanta yanzu ya mari Anty Halima ta suma”

“Kuna ina?”

“Muna asibitin Fmc”

Be saka cewa komai ba ya katse kiran, zuciyarsa bata bashi kowa ba sai Namra ta ya akai ta fada rijiya ita tambayar da ta fado masa a rai, and why Aminu zai saka hannu ya daki Halimatu bayan ita take dawainiya da yarta, saboda kawai ya mayarda ita wata banza shine yake ta yi mata yadda ya ga dama.

“Miyasa bata kira wani ba a family sai kai? Bata fi kusa da Abdulhamid ba shi da ya aureta ya saketa cikin mutunci? Ji yadda kake zanzana kamar.... ”

Kan ta karasa ya daga mata hannu.

“Please....”

Sai kuma ya juyo daga jikin wardrobe da yake tsaye ya kalleta yana gyara hannun rigarsa.

“Alaka ta da Halimatu ba ta yankewa matukar ina da rai, saboda haka ki sakawa zuciyarki salama, idan za ki iya yarda da mijikin fine, idan kuma aka samu akasin haka za ki wahalar da rayuwarki ne kawai, na fada miki kuma a yanzu zan sake maimaita miki hakan, for now on ba saboda na auri Halimatu nake wannan abun ba i just want to make her happy....”

Yana kawai nan ya nufi gurin da kananan abubuwansa suke ya dauka ya saka aljihu ya fice daga dakin cikin sauri. Kamin ya isa asibitin zuciyarsa ta cika, ransa ya bace sosai from now on zai rika defending Halimatu as her brother, taya wani can wai shi tsohon mijinta zai saka hannu ya daketa saboda kawai yarta ta fada rijiya.

“Ji wani irin zalimci”

Ya furta yana jin wani irin bacin rai an taba masa Halimatu, a take wani bangare na zuciyarsa ya aika masa tambayar da ya rasa amsar ta.

“Miyasa na damu har haka? What if mutane suka zargi wani abu? Miyasa nake ta zurfafa lamarinta a raina har yanzu....?”

Yayi farkin motarsa gurin da kowa yake fakin sannan ya fito ya nufi cikin asibitin yana kokarin sake kiran Salma dan sanin inda suke a cikin asibitin.



HALIMATU POV.

Ashe suma na tana da dadi kamar dai shan maganin bachi, ta kan mantar da kai duniyar da kake ciki da kuma duniyar kuncinka balle kuma wata damuwa da fargaba ko kuka da tsoro. Indai har haka itama mutuwar take to ni kam ina maraba da ita daga yanzu har zuwa lokacin da zata sallamomin.
Sannu sannu Halimatu.

Muryoyi biyu na ji wadanda ba zan iya tantancewa ba kamar na Inna da Mama kuma kamar ba na su ba, iyakar unkurin da nai na bude idanuwa ne sai na ji sun min nauyi sosai, a cikin kaina kuma kamar babu komai ina jinsa kamar fanko. Ban ankaro ba na ji numfashina yai nauyi gurin fita daga kirjina haka ma gurin shiga sai na yi da karfi yake wucewa. Da wani irin karfi na umkuro na tashi zaune tare da bude idanuwa har sai da Inna da rike ni. Tabbas Inna ce ga fuskarta nan ina gani kamar a mafarki bakina na motsi amman ban san mi nake cewa ba, kai na daga sama gaba daya komai kamar ba gaske ba nake ganinsa. Kamar a min shokin sai na ji na farko daga mafarkin da nake. A zahirin ma ga Inna nan rike da ni Sai Salma da Aisha da Fati tsaye a kaina, Salma ta rufe bakina tana kuka tana kallona kamar yadda Inna ma take kuka ita da Fati.

“Anty Halima...”

Aisha ta kira sunana tana kallona kamar a firgice.

“Na'am”

Na amsa mata ina kokarin tuna abunda yasa aka kawo ni a nan. Na tuna Namra ta fada rijiya muka kawota ko? Sai aka mare ni? Amman waya mareni? Miyasa aka mareni?

“Ina Namra take?”

“Babanta ya dauke ta”

Salma ta amsa tana share hawayenta. Daga lokacin ban sake sanin inda nake ba, sai na ji kamar wata tsotsa tana min yawo akai. A lokacin da hankalina ya dawo sai na ga Abdallah da wasu likitocin uku tsaye a kaina suna kallona. Wannan karon Salma hannu ta dora saman kai tana hawaye, Aisha ma kuka take.

“Wai miya faru? Namra ta mutu ne?”

“Bata mutu ba... ”

Abdallah ne ya amsa min yana saka hannunsa a aljihu.

“Ina son na ganta”

Ina kokarin sauka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login