Showing 24001 words to 27000 words out of 217237 words

Chapter 9 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

170

kuma yadda nake ji a yanzu da nake tare da kanenki, a kullum ina cikin fargaba da tsoron kar wani abun ya same su kar wani ya lalata musu rayuwa, ko daga nan zuwa gidanki suka fita hankalina a tashe yake har sai sun dawo sannan na ke samun natsuwa, shiyasa a kullum bana da burin da ya wuce ko wacce na ganta a dakinta, Halimatu kina jin abunda na ke ji a matsayina na uwa, ke ma uwa ce”

Dan murmushi nai kadan sannan na nufi dakinta na kwanta a kusa da Amal ina ta kallon fuskarta, kamin na sake tashi na nufi inda handbag dina take na dauko na danna number Abdallah sai na jita a rufe wata kila ya rufeta ne saboda ya san zan kira ko kuma ya saba rufe idan zai kwanta ne oho.
A wani abun mamaki a daren sai na kasa runtsawa har safe, bachi ya kauracewa idona ba dan kuma ina tunanin komai ba, domin ban ji tunanin kowa ya zo min rai ba a wannan daren sai Allah ya saka min saukin abun har na ke jin kamar bana da damuwa a tare da ni.
Misalin hudu saura na asuba na tashi na shiga bandakin domin yin alwala nai nafila kamin ayi assalatu, ina tsugunawa gurin fitsari sai jini ya fara min zuba a madadin fitsarin, sai da ya zubo min da dan yawa har da sare sannan nai fitsarin na wanke na tashi sai na ji abun be tsaya min ba.
A dole na nufi dakin kanena na tashi Marwa ta bani pad na saka sannan na dawo na zauna na dauki carbi Mama ina ta ja, marata na dan murda min kadan-kadan.

Haka nai ta dauri har kusan takwas da yan mintuna na safe, ina bawa Amal koko wayar Abdallah ta shigo.

“Hello Assalamu Alaikum”

“Wa'alaikissalam Momy ina kwana?”

“Lafiya kalau Namra an tashi lafiya?”

“Lafiya Kalau”

Ta amsa min da muryarta radau har tana yar dariya.

“Momy ga maman su Nabeela”

Ta mikawa matar Abdallah wayar muka gaisa, sannan ta bawa su Adnan da Aiman, daga bisani ya karba ba tare da ya min magana ba ya kashe wayar. Number Hajara na kira na labarta mata abunda yake faruwa sai ta saka salati da sallami tana fadin sai ta zo. Bayan na gama da matsalar Amal na aika yaro aka siyo min pad da pants a shago na shiga nai wanka na fito na saka tufafin jiya, sannan a shiga dakin Baba na gaishe shi tare yi masa ya jiki.

“Al-hamdulillah, na yi waya da Almu direba, zai zo anjima kadan sai aje kwaso miki kayanki, makulin gidan yana gurin Aminu ne?”

“Eh dayan yana can daya yana gurina”

“To za aje tare da ke saboda kar a hado da na shi, ki kwaso yana yaranki da na ki sai a kawo a nan,kamin na dawo ma ya tarar an kwashe komai na ki”

“To Baba na gode”

“Babu komai Allah ya bamu hakurin zama, kin san shi zaman gida sai da hakuri musamman ma gida nai kanne da yawa haka, sai kin yi hakuri d yan'uwanko kamin Allah ya kawo miki wani na gari”

“In-Sha-Allah Baba”

Na jidadin yadda ya nuna min kulawa sosai, tara da yan mintuna direban ya zo da babbar motarsa irin wannan ta kwasar kaya, tare da ni da kanena uku aka je muka kwaso komai sai da mu kai wa gidan tas da kayan sannan muka dawo, a unguwa kuwa kowa sai kallon yake ganin an kwaso kayan wanda be san da maganar ba ma yanzu ya sani. A dayan dakin da ake zuba kaya aka zuba gado na da kujeru da sauran tarkashe kayan sakawata kuma na kai su dakin su Marwa domin shi ne ke da girma sosai har ma na samu gurin shimfida katifa ta, na raba yan tsoman karana gefe. Tabbas na ji babu dadi a wannan lokacin domin bbu wanda zai so baro wadatacen gidansa ya dawo wani guri ya raba. Bayan mun gama na sanja wasu tufafin na bar Amal a gida na nufi gurin aikina. Kowa yayi mamakin ganina a wannan lokacin dmin ban saba zuwa da aiki a late ba ko ma naje late ba kamar haka ba, domin sha daya saura. Mun gaisa da Kabeer da Emanuel kamar yadda muka saba da halshen turanci kamin Kabir ya koma yana magana da ni da hausa daga can inda yake zaune ni kuma ina zaune a teburina.

“Ya jikin na ki?”

Shiru nai wata kila na fada masa bana jindadi ko? Oho na dai manta.

“Al-hamdulillah”

“Kin karya kuwa?”

Nan ma shiru nai kamin na bashi amsa, na manta when last wani ya tambaye ni ko ya damu da na ci abinci.

“Eh na karya”

“Baki karya ba Haima na sani”

Na fada yana dariya sannan ya mike tsaye yana fadin.

“Bari na sauka kasa naje restaurant na siyo miki wani abun”

“Aa Kabir na karya ban bukatar komai...”

Be saurareni ba ya fice yana ciro wayarsa daga aljihu, dafe kaina nai kamin na dauki takadun da na tarar a gurin an shiga da su office din Oga Dahiru, da sallama na shiga na mika nasa gaisuwa sai ya amsa min yana kallona.

“Kwana biyu ba ki zo office ba”

“Bana jindadi”

Na fada ina mika masa files din hannuna.

“Kin ga likita?”

“Eh malaria ce”

Wani kallo yai min kamar be yarda ba, sai kuma ya karbi file din yana murmushi.

“Halimatu kenan, Thank you you can go”

Na juyo na fito daga office din ina ta mamakin kallon da yai min da kuma murmushin da ke fuskarsa. Ina kokarin zama a kujera ta gabana ya fadi na rashin dalili har sai da na kira Allah sannan na samu natsuwa, aikina na cigaba da yi har na tsawon minti talatin sannan Hafsat ya shigo office din mu hankalinta a tashe tana fadin.

“Ku kuna nan zaune ba ku san an kade Kabir ba”

Na riga Emanuel mikewa tsaye domin da hausa tai furucin kamin ta sake fada da turanci, sai naji abu kamar daga sama.

“Taya?”

Na tambaya hankalina a tashe.

“Gashi can waje ban san yadda akai ba amman har kafarshi ta cire gashi can ana saka shi a mota za a kai shi asibiti... ”
Ban san lokacin da na rufe bakina na watsa da gudu zuwa sakan ma'aikatar ba, tsakanin ni da Emanuel sai aka rasa wanda yafi wani saurin saka ya ganshi, sai dai dukan mu mun yi rashin sa'a domin tuni an saka shi a mota an nufi asibiti da shi, babu komai a tsakan titi sai shimkafa da ya siyo min da kuma jini, ban san lokacin da na fashe da kuka ba har sai da Raliya abokiyar aikina ta rikoni muka dawo cikin ma'aikata, a lokacin kasa yin komai nai kuma ban yi tunanin binsa zuwa asibitin ba a wannan lokacin sai sauraren marata dake murdawa na ke, kamin na dauki jakata na fito na tari napep na koma gida.
Ina isa na tarar su ma sun gama na su fadan da Familyn Aminu akan yayana, wai sai an basu yara Baba kuma yace idan suna son yara su tafi kotu, sun labarta min abunda ya faru sai dai sun lura nawa hankalin ba a gurin nan yake ba a yanzu, gani sai wani duke duke nake saboda ciwon marar da nake ji.

“Lafiya Halimatu”

“Mama marata ke masifar ciwo”

Ta yi saurin janyo kujera ta ba ni.

“Zauna sannu”

Na zauna ina jin kamar ba zan iya zaman ba, domin ko ciwon nakuda be kai wannan ciwon da nake ji a yanzu zafi ba. Wayata dake cikin jaka tai ringing sai dai ban kula wayar ba saboda ba ta wayar nake a yanzu ba.

“Salma je ki taro Napep muje asibiti”

Mama ta fada cikin tashin hankali ganin yadda nake cizon baki saboda azaba domin ta san ni da juriya. Kamin a taro napep din mu shiga zuwa asibiti sai na ji kamar zan mutu har da kuka hannuna akan marata sai murjawa nake. Mun yi sa'ar ganin likitar nai mata bayanin abunda nake ji a take ta saka a bani gado sannan ya rubuta min magani ta kuma fada min cewar abunda ke cikina ne yake kokarin zubewa za a min wanki mara.






___________

Kwana biyu nan ina busy shiyasa bana post kullum amman da zarar komai ya zama normal zan cigaba kamar yadda aka saba In-Sha-Allah.
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy


🔟

Ba mu dawo gida ba sai 6pm na yamma, domin bayan mace ta min wankin mara sai da likita ya bani damar hutawa na awa biyu da rabi zuwa uku sannan muka dawo gida.
  Da dare Hajara ta kawo min ziyara ta nuna min damuwarta da kulawa sosai kamin addu'arta ta biyo baya, mun dade muna fira da ita sai goma na dare mijinta ya zo ya dauketa. Bayan tafiyarsu da kamar mintuna talatin Abdallah ya kirani a waya har na yi kamar ba zan daga ba sai dai tunawa da bana da aure a yanzu ya yake min hanzarin kin daukar da nake yi a baya, wata kila ma Namra ce take son magana da ni ko Aiman.
Da nai picking ban ce masa komai ba, ko sallama da hello da ake idan an kira mutum ko kuma shi ya kira wannan karon bance ba, sai kawai nai shiruna ina jiran ya fara min magana. Shi kuma ya gagara cewa komai kamar wanda ya kira domin kawai yaji saukar numfashina, jin hakan yasa na kashe wayar na mike tsaye na nufi dakina ko kuma nace dakinmu ni da kannena. Tufafin jikina na canja na saka marar nauyi saboda yanayin garin da nake gani da kamar akwai hadari saboda zafin da yai yawa. Amal kuma na saka mata nata kayan bachi na kwantar da ita ina lallaba tai bachi sai ta fara min kukanta na banza daya saba yi wani lokacin idan za tai bachi.

“Ai da an sani a bawa Ya Abdallah ya hada da ke ya tafi mu huta”

Cewar Kanwata Haulat tana hararar Amal daman can basa shan inuwa daya da juna. Ni kuma nai murmushi na mika hannu na dago Amal na rumgumeta ina rarrashinta.

“Ya Abdallah yazo dazun lokacin kina asibiti”

“Ya kawo su Namra ne?”

Na tambaya ina kallonta.

“A a ba da su ya zo ba, shi kadai ya zo yana tambayarki sai Inna ta fada masa kina asibiti za a miki wanki mara”

Tana rufe baki kiran wayarsa na shigowa a wayata, nan ma sai dai nai kamar kar na dauka sai kuma wata zuciyar ta hana ni, picking nai na kara a kunne tare da sallama. Be amsa min ba kuma be ce min komai ba sai dai daga cikin wayar ina iya jiyo yadda yake ja da aje numfashi da karfi. Katse kiran nai na kwantar da Amal sannan nima na kwanta bayanta ina ta tunanin Kabir ko a wane hali yake ciki a yanzu inata auna zafin barin da na da kuma kafarsa da aka ce ta cire da gaske ma ta cire din ko kuwa dan karawa labarin magi dagishiri yasa tace haka? Number wayarsa na gwada kira da fari ta yi ringing har aka daga sai dai ina yin sallama sai aka kashe kiran na sake bugawa na ji wayar a rufe. Damuwa sosai ta shiga raina, ko ba komai ai mun yi zaman mutunci da Kabir idan na tsallake ko kuma na cire son tana jikin ko yi min maganar banza da Kabir yake kokarin yi ban san shi da wani hali na assha ba, tun ba jiya ba yana yawan damuwa na al'amurana, duk wani abun da ya dame ni zai nuna damuwarsa sosai a kaina, idan kuma akan wani laifin ne a gurin aiki to zai yi kokarin tare min ko ya wanke ki ko a gurin waye ne. Ko a kan wannan kadai ya kamata na damu da Kabir balle kuma saboda yaje siyo min abinci wannan abun ya same shi, ko da ciwon kai ne ya same shi ta dalilina dole na damu balle kuma hadari, abun sai ya hade min a guri daya har na rasa wanne zan fara tunani bayan damuwar da ke cina yanzu kuma wani abun ta samu Kabir ta dalilina.
Har garin Allah ya waye Kabir na cikin raina ban jidadin rashin zuwa ganinsa da ban samu yi ba, kusan rabin mafarkin da nai na Kabir ne sai dai ba zan iya fahimtar sakon mafarkin ba, kuma na alakanta hakan da kwanta da nai ina tunaninsa.
Duk da bana sallah haka ba be hana ni tashi da asuba da wuri ba kamar yadda na saba, ko bana sallah na kan yi addu'oina na safe idan ina lokacin period ne.


ABDALLAH POV.

Da gangan yake yai magana ya yi shiru yana ta sauraren yadda numfashinta ke fita fuskarsa na yalwantuwa da murmushin da shi kadai ya san sikarsa, bayan ta kashe wayar ya sake kira sallamar da tai masa ta saukar masa da natsuwa da kwnaciyar hankali daman can muryarta kawai yake son ji, domin ba shi da wani abun da zai ce mata, bayan son yai mata jajen ɓarin da tai ta waya, ɓarin kuma ba karamin dadi yai masa ba, domin ya kusanto masa da nesa kusa zuciyarsa na raya nasa a yanzu yana cikin ko wane mataki da zai iya nunawa Halimatu soyayyah, domin bata da auren a yanzu kuma ta cika idda indai har jinin ya tsaya mata. Kansa ya daga sama yana kallon tauraren da sukai ma sararin samaniya ado. Sannan ya maida wayar aljihunsa tare da zuba duk hanneyensa aljihun wandon, Halimatu ba zata so shi ba, ba zata taba amincewa da shi kai tsaye ba, domin yayi kuskuren nuna mata kauna a lokacin da take da igiya uku ta aure akanta har ta koma biyu har da zama daya, shi yake yawan fada mata mijinta yayi kaza ya yi kaza, yana yawan nuna mata Aminu ba irin mijin daya dace ta aura ba ne, ya dade yana jira zuwan wannan ranar ya dade yana addu'ar Allah ya raba auren Aminu da yar'uwarsa Halimatu saboda kawai shi ya aureta, yana ji a ransa kuma yana yawan rayawa a zuciyarsa cewar shi kadai ya dace ya zama mijin Halimatu, domin shi ne mutumen da zai iya nuna mata kauna zallarta ya kare mutuncinta ta martaba, and he know exactly how to lighten the candle of happiness in her life. Tun daga lokacin da ya dawo kasar nan tare da iyalinsa ya kyalle ido ya ga Halima sai Allah ya dauki sonta mai tsanani ya saka masa, har ya zama bashi da sukuni da walwala idan ban ganta ba ko be ji daga gareta ba, tun yana kokarin cire abun a zuciyarsa ya kawarda komai har ya gagareshi, har yake ji da ace ya san lokacin da take budurwa ko kuma yayi arba da ita tabbas da Halimatu bata da wani mijin bayan shi, domin tana da siffar da yake so a jikin mace komai na rayuwarta burge shi yake, the way she dressed, yadda take tafiyarda rayuwarta ga hakuri da kawaici ga magana ma so calmly, even simple makeup din da take burge shi yake.
Daga lokacin da ya gano kalar mijin da take aure kuma sai tausayinta ya samu muhalli a zuciyarsa, kuma ya samu makamin yaki da igiyar aurenta.

Ba abu ne mai sauki Halimatu ta karba tayinsa a yanzu ba, shi kansa ya sani domin haka ba zai yi kuskure nuna mata haka a yanzu ba ko kuma furta mata kalma so ko aure a yanzu ba, duk kuwa da kasancewar ta dade da jin daga gareshi saboda ya fada mata ba daya ba ba biyu ba cewar yana sonta yana kaunarta a lokacij da take da igiyar auren a akanta har take masa kallon mahaukaci ko kuma marar tunani, wannan dalili ya saka Halimatu tsanarsa fiye da kowa a familynsa.
Ba irin wannan lokacin ya kamata ya nuna mata so ba, wata kila ma bata sha'awar auren a yanzu, sai dai ya shirya nuna mata kulawa da kwantar mata da hankali da kuma kaunar yaranta.

“Daddy ba zaka shigo ba?”

Juyowa yai yana kallon yarsa Suhaima fuskarsa dauke da murmushi, ya kai hannunsa ya daga sama.

“Eyyyy ba ki kwanta ba Mamana?”

“Yes mu na ta kallo da Aiman, amman kowa yayi bachi sai ni da kai da Aiman muka rage”

“Okay je ciki ina zuwa”

Ya fada yana sauketa kasa sai ta juya da gudunta ta koma ciki, shi kuma ya sake ciro wayarsa sai dai wannan karon ba Halimatu ya kira ba Hajiyarsa ya kira duk kuwa da bashi da tabbacin cewar zata dauka wata kila ma ta yi bachi. A mamakinsa sai tai picking call din da muryarta radau babu alamun bachi.

“Hajiyata ba ki kwanta ba?”

“Ban kwanta ba Husaini kai me kake a farke?”

Jimmm yai na wani lokacin sannan ya ce.

“To ni ma dai ba zan iya fada ba for now, amman dai na kira na fada miki cewar Halima ta yi miscarriage ya kamata ki dubata gobe inda hali, kin ga ko sakin da akai mata Hajiyata ba ki je kin mata jajaye ba”

Daga dayan bangaren Hajiya tai murmushi mai sauti sannan ta dora da.

“Zanje gobe In-Sha-Allah shikenan? Jikin nata dai da sauki ko?”

“Ban sani ba, amman naje dazun ban tararda ita ba wai tana asibiti ni kuma bana son su fara zargin wani abun ne shiyasa ban je ba, amman ni ma gobe zanje ma dubata”

“To sai ka biyo ka dauke mu mu tafi ai”

“Aa Hajiyata zuwanki dabam na Abdallah dabam”

Ya fada da murmushi a fuskarsa sannan yai mata sallama ya sauke wayar, fira da mahaifiyarsa ko yayansa na daya daga cikin abunda yake saka shi ciki nishadi da farinciki ko da kuwa yana cikin damuwa ne. Juyowa yai ya nufo balcony ya tura kofar falon ya shiga. To His surprise sai ya samu uwargidansa tsaye jikin window dakin tana kallon waje sai dai shigowarsa yasa ta juyo ta da dubanta gurinsa. Ya dan wara ido yana murmushi daya saba yi mata.

“Suhaima ta ce kina bachi”

Ta wani marairaice kamar karamar yarinya marar.

“Taya zan iya bachi Doc be kusa da ni, na yi na dan guntun lokaci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login