Showing 120001 words to 123000 words out of 217237 words

Chapter 41 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

167

fin ne shiyasa”

Ya fada yana daukar cup ya hadawa kansa tea.

“Zan tafi yanzu idan komai ya zama Ready a fada min na aiko direba ko kuma na dawo na ci”

“Okay Allah ya maka albarka”

“Amin”

Ya amsa da dan murmushi kadan a fuskarsa sannan ya fito cire da kofin tea ya nufi motarsa ya bude ya shiga, yana mata key mai gadin ya bude masa gate ya fice, da hannu daya yake driving dayan hannun kuma na rike da cup din yana kurbawa a hankali.
Yana kusan isa kamfaninsa ya rage gudun da yake yana ta kallon Halimatu ta cikin bakin gilashin motarsa, shi be san abunda take a nan ba kusan kullum indai yayi sammako sai ya ganta idan kuma zai tashi ma yana ganinta tana bawa mahaukacin nan abinci, ko miye alakarsu oho! Ko da yake ita din ma ai kallon mahaukaciya yake mata, shi ganinta da yake kusa da kamfaninsa ma bata masa rai yake domin bayan mutuwarsa babu wacce ya tsana irinta, sai dai duk haka idan ya ganta a gurin sai ya tsaya ya kalleta sai dai idan ya ganta ya rika jin haushinta yana jin haushin kansa, duk ranar da be ganta ba har jira yake ga ko zata zo ta bawa mahaukacin abinci.
To ko shine uban yayanta? Wata zuciyar ta tambaye shi. Oho mata ma ko wanene can ita ta sani Allah yasa ma wata rana ya makureta.... Ayyana a ransa sannan ya karasa kamfanin da kansa ya shiga cikin ana ta miko masa gaisuwa amman ko kallonsu be yi ba balle ya amsa sai wani sham kamshi yake.




HALIMATU POV.

6 MONTHS LATER.....

Al-hamdulillah Al-hamdulillah Al-hamdulillah, da sannu rayuwa ta soma sauya min ta inda ban zata ba, domin ko a mafarkina ban kawo cewar zan samu aiki a kamfanin nan ba, duba da irin mutanen da sukai applying sai dai komai na Allah ne cikin ikon da yarda ya amince aka dauke ni aiki a kamfani, aiki a gurin yamin dadi ba dan komai ba sai dan Kabir kusan ko wace Safiya ta Allah nakan siye abinci a hanya ko kuma na siyo na dafa naje masa da shi idan zanje aikin, haka ma idan na dawo indai akwai canji a jikina zan siya masa abinci na tsare shi sai an tabbatar ya ci ya koshi sannan na dawo gida, hakan kuma na karamin faranta min rai yake ba, har ta kai a yanzu idan ya gama cin abinci na tashi sai ya tashi ya bi har bakin gate din kamfanin sai idan security din sun hana shi shiga sannan ya zauna a gurin ko kuma ya koma can a inda ya saba zama ya zauna har sai na gama aikin ya fito na bashi abincin.

Wani irin dadi nake ji, a taimakon abincin da nake bashi a yanzu, ina jin cewar na bawa wani mai bukatar taimako taimako na, a kamfanin ma kowa yana mutunta ni kamar yadda nima nake bawa kowa girmansa, bana da matsala da kowa ga wasa da dariya sai kace daman can mun dade tare a aikin, bana fuskantar wata matsala a aikina sai dai fargabar abu daya, wato Mahaifin Baby Namra, tun daga lokacin da na fara aiki a kamfanin aka bani takardu da da magazine din kamfanin sai na gane cewar shine mai kamfani kamar yadda na lura da cewar shine mai makarantar da can da Abdallah ya cire su Namra domin a can mna ganshi kamar yadda na taba ganinsa a wannan kamfanin aau daya, domin hotonshi ne a jiki an rubuta masa shugaban kamfanin Ahmad Muhammad Gwarzo, sai dai ba kowa ya san haka ba kasancewar ba a saka hotonsa a kamfanin ba balle sunansa, kusan tun da na zo ban taba ganinsa ba, sai wacan ganin da nai masa a farkon zuwana kamfanin neman aiki.
A yanzu kam kullum a cikin fargaba nake ina karanta masa hasbunallahu da rokon kar Allah yasa ya ganni har na samu wani aikin na bar masa kamfaninsa, domin ina ji a jikina cewar duk ranar da ya gano ina aiki a karkashinsa sai ya wulakanta ni ya ci min mutumci kamin ya koreni.
Bayan shi ba ni da wata fargaba kuma ina jindadin aikina, ko ba komai kamfanin yana kusa da inda Abdallah yake aiki, hakan yasa na daukarwa kaina kullum da misalin karfe biyu na rana sai saka order an kaiwa Abdallah abincin rana a office dinsa, tun ina zuwa kullum na kai kudin har na fara biyan na wata wata, sai dai duk da haka Abdallah be taba kira wayata da sunan ya min godiya ko ya nuna min ya jidadin abunda nake masa ba, ko kuma ya gargade ni akan na daina ba, sai dai mai kai abinci ya fada min be taba cewa a daina kawo masa ba, tun daga lokacin da na fara aiki a kamfanin kusan kullum sai na turawa Abdallah sakon Barka da Safiya abun har ya xame min kamar ibada sai dai shi be taba maido min da amsa ba, idan na masa magana a whaspp ko fb sai ya karanta amman ba zai ce min komai ba, tun ina jin babu dadi har na soma sabawa da wannan sabon halin nashi.
Haka zai shigo gaishe da su Mama da Baba gida, ba zai ko kalle inda nake ba haka ba kuma ba zai hana na yi masa magana ba, wani lokacin ya kan amsa min sai dai idan na matsa da magana sai yai mana sallama ya tafiyarsa.
Gaba daya ya canja min taimakon da yake ba ni ya daina, sai dai ba shi ya dame ni ba kamar rashi sakin fuskarsa da kula ni da yake a yanzu, ga shi Allah ya dauki soyayyarsa da kaunarsa da tausayinsa ya cika min zuciya da su. A yanzu ta kai idan ba zancen Abdallah ba bana son labarin ko wane namiji, duk wata soyayya da nai wa Aminu da Abdulhamid a baya ashe ta karya ce a yanzu nake soyayyar da gaske, haka zan raya dare da begensa a zuciyata da tunanin abubuwan alherin da yai, da girma da yaraba hudu amman tunanin soyayyar wani ta hanani sukuni, idan na ga wani da sunansa sai na ji ya burgeni saboda kawai Abdallah.
Sai a yanzu na gane cewar na aikata kuskure babba na zabar Abdulhamid na bar Abdallah, a yanzu kam ina ganin laifin Abdallah kadan na cewa yana so a lokacin da igiyar aure take saman kaina, da farko ina daukar cewar fushi yake da ni daga baya kuma sai na fahimcin cewar kamar kokarin cireni yake a ransa ya nesanta kansa da ni, wanda hakan ba mai yiyuwa ba ni a tsakanin ni da shi, har ga Allah na tabbatar Abdallah yana so na, kamar yadda nake jin a yanzu da a raba ni da soyayyarsa kara a raba ni da raina.
Ko da Abdallah ba zai aureni ba ina son na saka masa da soyayyar da ya nuna min ni da yayana.

“Wai da gaske kike za ki shiga gasar nan?”

Kaina na dago na kalli Hafiza wacce tai min maganar ina murmushi domin na lura kamar bata yarda da zancen da nai na cewar zan shiga tare da yara a wasar da za'ayi Next Week ta children day ba.

“Why not? Ko dan farincikin yarana ai zan shiga, bani da matsala da kowa yanzu ba aure ke kaina ba balle na ce”

“Amman gaskiya matan hausawa ba sh cika shiga irin wannan ba”

“Ai dai mata suna shiga ko? To nima zan shiga idan na saka wando zan dora abaya a sama na saka karamin hijab dina”

Na fada ina jin cewar har a raina zan yi domin farincikin yarana kawai, domin a yanzu bani da damuwa sai ta yarana da iyayena sai kuma tawa, na tattara komai na aje a gefe, Aminu ma da ya matsa min na fada masa kotu zan kai shi idan be daga min kafa ba, sannan na jadadda masa matukar be saka Sadi a kotu an kwatarwa Namra hakkinta ba ba zan taba yafe masa ba, wanda nake tunanin abu nai wahala yai hakan ko dan Hajiyarsa na san ba zata bari ba.

“Yes Momy kuma mu za mu cinye....”

Aiman ya fada yana daga hannu tare da dariya, sai na gyada masa kai.

“In-Sha-Allah kuma idan mun yi ta daya, zan yi amfani da kudin na saka ku a wata makaranta private school so that ku samu karatu mai kyau, sauran kudin na rika juyawa ga aikina kamin lokacin biyan wasu yai na san zan samu na biya”

Namra ta yi karaf tace.

“Momy pls ki siya mana kayan wasa kuma pls”

“Zan iya muku, ki yi addu'a Allah yasa mu yi na daya”

“Amin kullum zan yi addu'a idan na yi sallah”

“Da alama dai wanda ya siya miki ticket din nan ke da yaranki yana ji da ke sosai, ko mother letter din nan fa kusan 20k ake bada ita”

Hafiza ta fada tana dago min wata farar takardar mai zagen kamar abun zinari.

“Kuma kin ga ticket ma na shiga gurin kawai 10k ne na shiga game kuma 30 domin ko baka ci ba za su baka wani abu wanda kuma yai na daya million daya da award da kallon azurfa, haka dai na biyu har zuwa na biyar, muma na ga alamar shi wannan bawan Allah da yake ta wahala da ke kamar ba ma sonshi kike ba, oh maza akwai daukarwa kai wahala”

Ta sake fada tana tabe baki

“Baki san waye shi ba, kin taba ganinsa?”

“No kawai dai naga yana ta kashe miki kudi ne hakan nan, ko jiya sai da Mama tai magana har tace zata same ki ku yi magana indai a aurenshi za ko yi ba, to ki sallame shi kar dawo daga baya yace sai an biyashi”

Shiru nai na dan wani lokacin, idan har Mama ta same ni da zancen ban san me zan fada mata ba, idan har taji cewar kafiri ne zata tsorota ta kuma nemi hanani kulawa wanda na daina tuntuni amman shi ya kasa janye kansa daga jikin kullum sai neman kara shiga jikina yake, na rasa yadda zan yi da shi babu bakar maganar daban fada masa ba babu irin gargadin da ban masa ba amman babu abunda ya canja.

“Yana da kyau Momy amma yana saka sarkar cross kuma yana sawan cin chewing gum....”

Na yi saurin rufewa Namra baki.

“Kar naji maganar nan gurin wani, duk wanda ya fadeta a cikinku sai na dokeshi, tashi ku shiga ciki... ”

A tsawa na yi musu maganar fuskarta babu alamar wasa hakan yasa duk suka tsorata har Amal suka tashi suka shige daki suka bar mu a waje ni da Hafiza, a kokarin dauke hankalinta daga zance na dauko mother letter din na rike ina tambayarta.

“Me ake da wannan hala?”

“Uwa ce zata rubuta tahirin rayuwarta da kuma yadda take kula da yayanta daga karshe sai ta rubuta daga uwar su wane da wane, sai ta saka a cikin dan box din wasika, idan mc ya zo shi zai karanta sai ya fada cewar daga uwar su wane idan anji an san ko su waye ake nufi”

“Wow abun ya kayatar”

Na fada ina jin cewar ni ma zan rubuta komai na rayuwarta a cikin wasikar da kuma yadda nake kula da yarana sai dai na zan fadi sunan da suna yara ba ba, ba so nake a san ni ba kawai dai ina son nao sharing tarihin rayuwata ga wadansu iyayene musamman abunda ya shafi Namra domin kawai ya zame musu darasi su kula da yaransa da kyau, ba kamar yadda ni nai sake har haka ta faru da yata ba, zan rubuta komai nawa a cikin har da rayuwar aurena a gidan Aminu da auren Abdulhamid da soyayyata da Abdallah, haukacewar da Kabir yai da kuma mutuwar Baby Namra fyaden da akai min akaiwa yata, sai dai ba zan fadi sunan kowa a ciki ba.

“Ke fada min ina kike hadu da shi?”

Ta tanbayeni daman na san za a rina, a banza ma Hafiza tai gulma balle wannan mai dalili. Abunka da yar'uwa duk kuwa da kasancewar ba uwar ma daya ba uba ne kawai amman bama boyewa juna abu idan ma ba wanda ya sani ba ba zai taba sanin cewar ni da Hafiza yan uba ne ba, domin a gidan m ba zaka taba sanin yan dakin Mama da kuma yan dakin Inna ba, kowa uwarmu ce idan Mama bata nan bama da matsala ko damuwa mun san Inna zata mana kamai, kusan Hafiza ma a dakin Mama take komai nata a can take yi wani lokacin ita da Mama har sirri suke babu wanda ya sani sai idan sun fada.
Kamin na gama bata labarin har mararta ta cika da fitsari, tsoro duk ya bayyana a idonta da jikinta.

“Bari nai fitsari na dawo”

Da gudu ta nufi bandakin da ke tsakar gidamu tai fitsari sannan ta dawo ta zauna tana zaro ido.

“Dan Allah ki ce kin yafe masa mana, Wallahi zai iya fusata ya zo ya halbemu, kin ga dai ni ko dan karatun ban gama ba, balle na ci moriyarsa, ga yaranki kanana, Baba Lafiya ma bata isheshi ba, dan Allah ki yafe masa kar ya zo ya halbe mu dan Allah kema zai iya halbeki Wallahi...”

Da farko dai na dauki maganarta serious daga karshe kuma sai ta bani dariya domin na lura tsoro ya gama cika mata ciki, ina cikin dariya Baba ya shigo bakinsa a haushe yana da far'a.

“Kun ji abun Allah yanzu fa sallamar da kai min ina fita wani ya bani 100k kyauta”

Ni da Hafiza muka hada ido kamin su Inna da Mama su fito daga dakin da murnarsu, gaba dayan gidan sai ya kaure da murna abunka da talaka mai neman na yau da gobe ya samu kyautar 100k a rana daya ina bakin yan gidanmu zai rufu, ni kaina na nuna murna kuma na jidadi ganin yadda Mama da Baba da Inna suke ta murna suna masa addu'a, sai dai ni na san mutum daya zai iya wannan abun wato Abraham.

“Amman Baba kai kadai ya bawa kyautar?”

“Gaskiya bani kadai ba ina tsaye da Malam Isuhu ya min sallama ya miko min 100k shi kuma Isuhu ya ba shi 5k”

“Baba yaro ne?”

“Aa dattijo ne amman ba zai kaini tsufa ba gaskiya, yana cikin wata bakar mota mai kyau kana ganinta ka san mai kudi ne sosai, shi dai mai ja masa motar ne matashi”

“Uhmm”

Na fada ina rafka uban tagumi tare da kallon Inna da ke fadi.

“Allah mai iko sai ka ji wani yayi kyautar abu kamar banza yanzu har dubu dari ka bayar kyauta, wasu Allah yai musu arziki”

Mama ta taya ta.

“Ina jin dai zakka ce, ko kuma irin masu kudin nan da ke bin gidajem talakawa suna ba su kudi”

“Ko dai minene mun gode Allah shi kuma Allah ya saka masa da alheri, daman an kwana biyu ba mu girki da nama ba gobe da safe idan Allah ya kai mu sai a samu mana nama mu ci”

Cewar Baba, sai duk suka dariya ban da ni da ke ta wani tunanin na dabam. Har aka isha'i babu abunda nake sai tunanin yadda zan bullowa lamarin nan, wata zuciyar na fada min cewar na sanar da police kawai n huta ko kuma na sanar dasu Mama idan kuma nai hakan hankalinsu zai tashi, idan kuma na kyale shi abun nan kara gaba zai yi.

Misalin takwas da rabi yaro ya shigo wai an sallama da ni ba waje, da farko na dauka Aminu ne domin shi ma yana min hakan ganin bana daukar wayarsa sai kawai ya aiko kirana kai tsaye sai idan na fita na ganshi, sai dai mafi akari Abraham ya fi min haka, domin shi be tana kirana a waya ba ma, be tana ce min na bashi number ta ba.
Aiko kamar jira nake na zari hijabi na saka na bi bayan yaron da ya aiko kirana, ko da n fita yana can nesa da gidanmu kamar yadda ya saba tsayawa, hango ni yasa shi fitowa daga motar ya rike gambun motar yana ta kallona har n karaso.

“Me kake so? Kana ta bibiyar rayuwata, na fada ka fita daga hanyata, bana kaunar ganinka Abraham kai ne silar lalacewar aurena ba baka aikata abunda ka aikata min ba da har yanzu in zaune tare da mijina... To me kake nema a yanzu?”

“Yafiyarki mana, na rasa gane wace irin mace ce Halimatu, me zan yi ki yafe min? Fyaden da nai miki kuskure ne, na yarda na lalata miki rayuwar aure, amman haka ba ya kara fito da kalar mijinki ne kawai, na nuna miki cewar ba zai iya zama da ke idan wani abun ya same ki ba, and I'm here for you, na ji na aikata laifi amman yafiyarki nake nema, and i promise you zan dauki nauyin yaranki da iyayenki da kanenki, zan inganta rayuwarki”

“Da kudin haram? Kudin da kuke tare mutane masu hakki ku karbe musu abu? To bana so kuma karka sake bawa mahaifin kudinka na haram”

“Su waye muke tarewa muna kwace musu hakki? Halima har addinina n ce zan bari na shiga na ki saboda kawai ina kaunarki amman kin ki aminta why? Daman haka musulmai kuke?”

“Karka kuskura ka kasa zancen addinina a ciki maganarka, kuma tirr da kai ni ba zan auri dan fashi ba dan fashin ma wanda ya keta min haddi”

Ya gyara tsayuwarsa yana kallon.

“Waya ce miki ni dan fashi ne?”

“Miya hada ka da bindiga a wacan daren?”

“Saboda kawai n rike bindiga sai ya nuna ni dan fashi ne, a yanzu ma ina da ita a mota, ke dai ba kisan komai a game da ni ba, ba ki san waye ni ba, iyakar abunda kika sani na miki fyade sai sunana sai kuma bibiyarki da neman yafiyarki da nake”

“Idan na yafe maka zaka daina kula ni zaka daina bibiyata zaka daina zuwa kofar gidan nan zaka daina bibiyar yarana?”

“No ai yafen min da za ki yi shine ki aure ni, ki haifa min yara.....”

Da sauri na rumtse idona ji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login