Showing 105001 words to 108000 words out of 217237 words
nasa ya sauya ga tsoronta da yake kamar mutuwarsa, abubuwa sai fada masa suke.
“To idan ba zaka iya zuwa kai wa matar taka fada ba, ni zanje da kaina nai mata fadan kuma dole na yayanka su zauna a gidanka kamin uwarsu ta dawo, dan yara ba za su zauna suna ta gararanba a gari ba ba kamar marasa gata”
Da sauri ya dago kansa jin Hajiya tace zata je tai wa Murja fada.
“A'a Hajiya zan sake mata magana zan lalaba har ta yarda”
“Har da yarda? Ka lallabata? Uwarka ce ita? To ba zan lamunta ba, ba zan dauka ba, ko tana so ko bata so dole ne yara su dawo gidan ubansu, da har zance zan rika maka su amman yanzu na fasa ko zaku mutu sai sun zauna a gidan nan”
Cikin rashin jindadin ya kalli Hajiya.
“Hajiya komai dai a bi a hankali kin san ba ko wace mace ke son rikon yaran wata ba, kuma kin ga bata haihu ba so duk wani responsibility na yara bata san shi ba”
“Idan suka zauna gidan ka daukar musu mai kula da su, yaran ma ai da wayonsu kuma ba fata muke a wani dade ba mahaifiyarsu zata dawo, duk yadda za ayi sai ta dawo duk inda zan fita na shiga sai na yi amman Halimatu sai ta dawo maka, ko dan arzikinka ya dawo”
“Shine kawai abunda nake fata yanzu ni har abunda nake ganin yafi a bar yaran a hannunta idan zata dawo sai ta dawo tare da su gaba daya, sai na kama mata wani gidan ita da yara su zauna”
“Idan ba a karbe yaran ba taya za ayi? Ta dawo? Ai sai an karbe yaran shaukin sonsu da kaunarsu ya shiga zuciyarta sannan ta san muhimmancinsu ta dawo maka”
“To Hajiya idan Murja bata yarda da zamansu ba ai dole na hakura har ta dawo gaba daya..... ”
Ya karasa yana ciro wayarsa dake ringing daga cikin aljihun gaban rigarsa, ganin daga gurin aikinsu ne yasa shi hanzarin daukar wayar. After sun gaisa mutumen yake sanar masa ya zo yanzu ana nemansa.
“Okay gani nan zuwa, amman lafiya dai?”
“Ka zo dai”
Ya sake amsawa da okay sannan ya kashe wayar gabansa na mugun faduwa kamar yadda jikinsa yake fada masa ba lafiya ba.
“Wato yanzu sai ta aminta sannan yara za su zauna gidan lallai Aminu, kamar ba kai ba kamar an sauya ka Wallahi”
“Rayuwa dole ai tana sauyawa Hajiya, yanzu dai bari naje gurin aiki ana nemana”
Ya fada yana mikewa tsaye, Hajiya kam da kallon mamaki ta bishi har ya fice. Direban Hajiya yai ma magana ya sauke shi a gurin aikin na su da zimmar idan ya gama abunda yake sai ya samu wani cikin abokan aikinsa su sauke shi gida, tunda abun ya zame masa haka mota bata kaunarsa sabuwar da ya siya ya kashe mata kudi har ya gaji bata gyaru ba, idan ma ta tashi cikin kwana biyu zata sake samun wata matsalar.
Cikin tsoro da tunani kala kala ya shiga ofishin shugaban na su, ya tararda wasu mutane a ciki hakan yasa shi neman guri ya zauna har sai da ya sallami bakin nasa sannan ya karasa gurin teburin ogan yaja kujera a daya daga cikin kujerun da mutanen suka tashi ya zauna yana mika masa gaisuwa.
“Makullin office dinka nake son ka ba ni da duk wasu takadar da suka shafi ma'aikatar da wadanda suke hannunka...!”
Tas tas tas gabansa yai mugun bugawa.
“Ranka ya dade lafiya dai?”
Wanda ya kira da ranka ya dade ya dauko wata takardar ya mika masa, sanyi jiki Aminu yai gurin karba kamar yasan abunda ke ciki ba alheri ba ne.
“Ranka ya dade takardar me ce?”
“Ka karanta ai ka yi boko”
Ya hade yawu yafi a kirga sannan ya bude zungureriyar takadar wacce ya kasa fahimta abunda aka rubuta a ciki ba dan kuma be iya karanta turancin ba sai dan baya cikin natsuwarsa.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, ranka ya dade me nai aka kore ni? Kamar kora na ke gani ko?”
Ya tambaya jikinsa na bari bayan ya karanta takardar a galabaice ga wata uwar gumi daya tara a goshi.
“A gaskiya ni kai na ba zan fadar dalili ba abu ne daya taso daga sama”
“Amman ana sallamar mutum ba tare da yayi laifin komai ba ranka ya dade? Idan wani laifi nai a fada min sai na gyara, aikin nan shine rayuwata”
“To ina ganin abunda yafi ka koma gida sai ka rubuta apology letter sai ya aiko min ni kuma zan tura ta sama In-Sha-Allah, amman dai sun fi zarginka da wasa da aikin ga kuma rashin zuwa aikin akan lokacin”
“Allah yasa hakan shi yafi alheri, na gode”
Ya fada yana mikewa tsaye jiki a sanyaye zuciyarsa a daure. Office din nasa ya nufa a lokacin daya shiga sai ya rasa abunda zai yi a ciki sai kawai ya nemi gurina zauna ya rumtse ido, tunani yake son yayi ya kasa tunanin me zai yi? Kayansa da suke office din ya kwashe ko kuma tunanin gobensa? Ko tunanin laifin da ake tumarsa da shi? Anya wannan kawai ya isa ya saka a koreshi daga aikin da ya shafe shekaru yana yi? Ko dai akwai wani wanda yake masa makarkashiya yake bibiyarsa da sheri? Shigowar abokinsa ne yasa shi dago kai ya kalli kofar da idanuwansa da suka gama sauya kala.
“Tahir kaga abunda mutanen nan suka min?”
Ya fada yana nuna masa takardar kamar ya fasa kuka.
“Aminu sai hakuri idan mahassada suka saka mutun a gaba sai addu'a tun jiya aka bada takardar nan amman kowa ya kasa kawo maka shine yau bayan ka bar office yace a kira ka shi zai baka”
Ya busar da iskar bakinsa.
“Yace na rubuta takardar bada hakuri”
“Kai share banza ai duk da shi akai maka wannan sherin budurwarsa yake son dorawa a kujerarsa”
“Wacece Habiba?”
“No Jalila dai ba tare yake da ita ba”
Duk wata magana da yake yana yinta ne kawai cikin karfin hali amman ba dan yana da kuzari da karfin zuciya ba. Da taimakon Tahir ya hada duk wani abu daya san na shi ne ya kwashe a office din ya saka a kwali Tahir ya saka masa a motarsa, sannan ya koma office din shugaban na su ya mika masa keys din da wasu abubuwan da suja shafi ma'aikatar yai masa sallama ya fito.
Tun da suka kamo hanyar gida Tahir ke ta ba shi magana yana nuna masa hanyar da zai bi a maida shi aikin da kuma manyan mutane da ya kamata yai ma magana. A cikin motar Tahir ya bar komai nasa ya fita daga motar ya shiga gidansa cikin damuwa da tunani kala kala, he wasn't surprised ganin motar Sadi a harabar gidan daman can ya saba zuwa gidan idan an kwana biyu wani lokacin kuma yana shigowa tare da shi, suna da kyakkyawar fahimta tsakaninsa da Murja ba kamar Halimatu da daman can tun a farkon fari basa samun jutuwa wanda ya samu asali daga Hajiya wacce bata son Halimatu. Tafiya yake yana jin kamar ba kasa yake takawa ba saboda damuwar data cika masa ruhi, a yau kam ba tare da ya kira murja ya sanar mata da zuwansa ba zai shiga gidansa duk kuwa da kasancewar tai masa gargdin cewar karya dawo gida babu notice, sai dai tashin hankalin dake tare da shi a yau ya mantar da shi dokarta, shi yanzu ma tsoronsa daya kar ya fada mata gaskiya ta guje masa, ko kuma ta juya masa baya, anya ma zai iya fada mata cewar an koreshi daga aiki bayan ko amarci bata gama ci ba? Duka duka ko shekara batai ba tana tunanin jindadi zai bijiro mata da wannan maganar? Har ya tura kofar falon ya shiga be yanke shawarar fada mata gaskiya ba ko kuma boye mata idan ma ya boye mata me boyewar zai haifar tunda dole ne wata rana sai ta san gaskiya. Ganin babu kowa a falo sai tv dake aikin watso labarai yasa shi mamaki, sai dai be kawo komai a zuciyarsa ba ya leka kitchen din dake bude nan ma wayan babu kowa kai tsaye ya nufi dakin Murja yana tabawa ya ji shi a kulle an saka masa key daga can ciki. Hakan yai mugun daga masa hankali har ya kai hannu yai knocked sai kuma wata zuciyarta hana shi, to ko dai Murja bata nan ne? Ta rufe dakin ta manta bata rufe falon ba? Idan kuma bata nan mi ya kawo motar Sadi a cikin gidan? Kuma ina Sadin yake? Juyawa yai da sauri ya fice daga falon ya zagaya ta can gurin windows dakin Murja da zimmar ya leka dakin sai ya samu windows din suma a rufe.
Dawowa yai falon ya zauna ya zubawa kofar dakin ido, yana ta kokarin hana zuciyarsa zargi yana ta kokarin kyautatawa matarsa da dan'uwansa zato! Sai me? Sai ya kasa natsuwa ya kasa sukuni gaba daya sai ya manta da zancen sallama hankalinsa gaba daya ya dawo a nan. Wata dabarar ce ta zo masa sai ya fita harabar gidan daga can inda ba za a jiyo muryarsa ya kira line ta da sunan da yai saving number ta sweetheart ringing tai har sai da ta kusan yankewa sannan tai picking.
“Hello Baby”
“Na'am ykk zan dawo gida yanzu”
“Okay sai ka iso i love you”
“I love you too”
Ya amsa mata yana maida numfashi. Sannan ya maida wayar aljihu ya nufo falon, har lokacin ba a bude dakin ba kuma be ji motsi ko alamar za a bude din ba hakan yasa shi jin sanyi a ransa sai hankalinsa ya fi karkarta da yarda cewar wata kila ta fita wani wajen ne? But wait idan ta fita ina Sadi? And me ya kawo motarsa a nan?
Ganin ba shi da amsar tambayar yasa shi sake nufar kofar dakin da zimmar knocked sai dai kamin ya karasa aka bude kofar daga can ciki ga mamaki Sadi ya fito daga dakin sanye da shadda yellow hullarsa a hannu yana gyarata. Kamar hoto haka Sadi yai tsaye a gurin ganin Amnu, kamar yadda Aminu ma yai tsaye kamar an dasa shi a gurin sai dai hakan be hana shi murmushin mamaki ba.
“I...na.. Mu...rja...”
Ya tambaya maganar na fitowa daga bakinsa daker. A rikice Sadi ya nuna masa dakin daya fito a take gumi ya karyo masa.
“Tana..... Ta... Na... Ci... Ki.... Al.... Al... Aljannunta.... Ne suka... Taso.. So... So... So”
Murja kamar jira take tana jin haka ta buga wani mahaukacin ihu ta fadi kasa ta soma murje murje....
HALIMATU POV.
Ban jidadin yadda na amsawa Abdallah cewar yes kaunar Aminu nake ba, bayan kuma ni kaina na san karya na fada na fada ne kawai cikin bacin rai sanadiyar maimaita min tambayar da yake ta yi, sai dai a yanzu ina jin cewar ko kallon banza be kamata ace ina yi ma Abdullah ba balle har na fada masa wata maganar marar dadi, na ji babu dadi sosai haka yasa na yanke shawarar kiransa idan na natsu na bashi hakuri, sai dai kuma ya cancanci na kira na bashi hakurin? Hakan ba janyo min wani abun ba? Idan kuma ban bashi hakurin ba zai iya daukar da gaske son Aminu nake, halin a yanzu ko sunansa bana son ji balle har a alakanta kalmar so da shi, no ba sai na kira shi ba indai Abdallah ne da zarar ya gama fushinsa ya sauka zai koma kamar komai be faru ba.
Haka dai muka isa gida a napep da sake sake kala kala a raina, na kulla wannan na kwance wacan har na fita daga napep din.
“Mai motar can fa tun dazun yake biye da mu”
Mai nepep din ya fada yana fito mana da kayan mu, da na daga kaina sai na hango wata kafirar bakar mota mai bakin gilashi wacce ban taba ganin irinta a fili ba sai a fina finai, mai motar kamar ni yake jiran na dago na kalleshi sai ya sauke gilashin motar a hankali, me zan gani? Mutumen nan ne wanda na taba gani a lokacin da na farka a asibiti kafirin nan, wani irin faduwa gabana yai a take na nemi natsuwata na rasa.
“Hasbiyallahu wani'imal wakeel”
Na furta ina cigaba da kallonsa kamar yadda shi ma yake kallona fuskarsa ba yabo ba fallasa.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Na sake furtawa daga Aisha har Husna kallona suke kamin su kalleshi sai yai sauri daga gilashin motar yai ribas ya juya inda ya fito.
“Kin san shi ne?”
Mai Napep din ya tambaya.
“No”
“To Allah ya sawwake yanzu mutane abun tsoro ne, garkuwa ake da mutane ta ko'ina”
Na dan tabe baki.
“Allah na tuba to ni idan an yi garkuwa da ni me za a tsinta?”
“Ai ba shi mutane suke dubawa ba, kuma ai akwai matsafa masu dauke mutane, sai dai kuma idan sonki yake”
Na sake duban mai napep din da kyau kamin nai murmushi na girgiza masa kai.
“Ni kan yanzu ai na girmi so”
“Ta ina? Ga ki kyakkyawa da jini a jika? ”
Daga ni har shi har kannen da muke tare dariya mukai, Maganarsa sai ta tuna min da wata maganar marar dadi da Aminu ya taba fada min.
“Look at you duk kin yi wani muni kin tsufa..... ”
Ajiyar zuciya na sauke na dauki wasu kayan na shiga da su cikin gida ni da Husna Aisha kuma ta tsaya sallamar mai napep din sarkin bargwanci.
Na jidadin ganin Mama da nai duk kuwa da kasancewar na ganta jikin nata sai a hankali amman hakan be hanani jindadin ganin farincikina ba, ba ita kadai ba kowa a gidan ya jidadin dawowata musamman ma yarana wadanda suka rika tsalle kamar na shekara bana gidan, Amal ta zo jikina ta zauna tana ta zuba min shagwaba.
ABDALLAH POV.
Luma biyu yai ya ji kamar ba zai iya cin abinci ba sai ya aje spoon din ya kurba ruwan dake gabansa.
“Lafiya kake yau?”
Ya dago a hankali ya kalli Suwaiba sai ya amsa mata a hankali tare da tashi ya bar mata dinning.
“Bana jin dadi ne”
Da kallo ta bishi ta tabe baki.
“Ai shine daidai da kai na san da ba haka nai maka ba ba zaka fita safgar wannan shegiyar Halimatun ba, amman yanzu da Abdulhamid ya san gaskiya ai dole ka kama kanka dan na san zai taka maka burki da wuri, tun da ku maza ba kunya ce da ku ba yanzu nan sai kace zaka aureta, idan anyi magana kace tausayinta kake to sannu sahabi.... ”
Ta cigaba da cin abincinta ranta fes duk kuwa da kasancewar bata san makasudin bacin ran mijin nata ba, sai dai ta san baya rasa nasaba da abunda ta fadawa Abdulhamid domin a yadda ta ga ransa ya bace ta san ba zai bar maganar ba!
Dakinsa ya shiga ya kwanta ya rasa abunda ke masa dadi, a duk lokacin da ya tuna maganar Hajiya ta gatangar da ta gina tsakanina da Halimatu sai yaji wani abu ya tokare masa zuciya, be tabbatar yana sonta da gaske ba sai a yanzu da yake jin kamar Hajiya na kokarin rabashi da ruhinsa ne. Ya rasa dalilin Hajiya na kin masa uzuri ya rasa dalilin hajiya na tsanar Halimatu tun daga lokacin da ta auri Abdulhamid, yes yasan tayi kuskure na auren Abdulhamid bayan kuma ta san yana sonta, amman ai itama mutun ce kamar kowa ko? Zata iya daidai zata iya akasin haka, then miyasa Hajiya ba zata kalli wannan tai mata uzuri ba? Ko da yake yanzu ba laifi Hajiya ba ne laifin Abdulhamid na yi mata maganar da nuna bacin ransa. Bayan kuma ba shi da wata hujja a yanzu domin da yana sonta kuma ta damu da ita da be sake ta da be juna mata baya ba. Hannunsa ya kai ya dafa zuciyarsa yana kara fadawa wani kogin tunanin.
Wai yanzu duk wani abu da yake yi ma Halimatu janye zai yi? Ba zai sake mata komai ba kenan? Babu wata alaka da zata sake shiga tsakaninsu? Ya tambaya kansa yana jin wani irin shauki da son ganin fuskarta.
______________________
Anya Abdullahi zai iya jurewa?
Da gaske Aljanun murja ne suka taso?
Waye yake bibiyar Halimatu kuma a yanzu?
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣5️⃣
Kasa cewa komai yai ya tsaya a gurin kamar an dasashi, Sadi kan sai gumi yake hadawa abun ka da marar gaskiya, Murja kuma na can dakinta tana aikin ihu kamar da gaske Aljanun ne suka ziyarce ta har da wani yare take shi ba yarbanci ba, ba kuma iyamuranci ba.
“A kaita asibiti, no gurin malamai”
Fadi ya fada wiki wiki da ido, sai Aminu yai masa murmushi tare da gyada masa kai alamar gamsuwa.
“Za a kaita”
Ya amsa masa sannan ya nufi dakinsa jikinsa babu kwari, saman gadonsa ya zauna sai ya rasa abunda zai fara tunani, korarsa da akai a gurin aiki ko kuma tararda dan'uwansa tare da matarsa? Kwantawa yai saman gadon yana ta kallon silin.
“Aminu ka ji tsoro Allah abunda kake mana baka kyautawa, ka rika tunawa kana da yara kana da mata, ace magidanci kamar idan ya bar gida ba zai dawo ba sai karfe daya ko biyu na dare...?”
“Ke Halima a nan gidana ne ina da yancin shigowa a lokacin da nake so na fita na lokacin da na ke so, ba ki isa ki saka min doka a gidana ba”
“Ba doka nake son saka maka ba, abunda kake yi nake kokarin nuna maka illarsa, duk abunda kai wa matar wani sai an yi ma taka, kuma duk abunda kai wa yar wani sai an yi wa yarka....”
“Idan iskancin kike so ni ban hana ki yi ba, ga ki ga guri har kya fada min wani wai sai an yi ma yar wani matar wani dan baki da hankali”
“Allah ya tsare ni, ban aikata zina ina budurwa ba ba zan aikata da aurena ba, ga hakkin yayana ga na iyayena ga na mijina ga na ubangijina? Wallahi ba zan iya ba”
Ya fada tana share hawayenta sannan ta tashi ta bar masa dakin. Tuna wannan yasa shi share hawayensa ya rumgume hannayensa a kirjinsa. A yau na mallakawa murja komai, ita ke saka masa duk dokar da tai mata,