Showing 135001 words to 138000 words out of 217237 words
ki same ni ko a ina ina son ganinki, ko wace irin uwa ce ke ina son ganinki dan Allah....”
Cikin kuka Ummulkhar take fadin hakan hannunta rike da loudspeaker dayan kuma rike da takardar yayinda idanuwanta suke zubar da hawaye.
Babu wanda zuciyarsa ta raya masa sai matar nan, sosai ya maida hankali yana kallon gurin da take zaune tare da yaranta, the way ta take sharar hawaye ya kara karafafa zatonsa a kanta, labarin yarsa ya shigo ciki duk kuwa da bata fadi sunansa ba ko sunan yarsa sai dai ta fadi cewar mahaifin yarta ya zargeta da kisan yarsa saboda kaddarar mutuwarta ya fada mata, kamar yadda kadarar gushewar hankalin abokin aikinta ya fada a kanta, an keta mata haddi an ketawa yarta, mijinta ya ci zarafinta, a kokarin kwatar hakkin yarta mijinta ya saketa, ga labarin samun aikin kamfanin da tai ya shigo ciki sai dai shi ma bata fadi sunan kamfanin ba.....
Wani irin kallonta yake, har ya ji kamar gilashin dake idon sa ya tare ganinsa sai ta ya cireshi yana cigaba da kallonta, ita kuma ta soke kai kasa yana ta latsa waya tana sharar kwalla, wa akai wa fyade? Wacen karamar ko babbar? No wait mutunen da take bawa abincin a kusa da kamfaninsu abokin aikinta ne? Is that why take kokarin kula da shi? Waye mijin na ta? Waya ke bibiyarta?
A lokaci daya ya jerowa kansa wadannan tambayoyin, da bashi da amsar su, and he can't take his eyes on her kamar his life defend on her, tun bata lura da kallon da yake mata ba har ta lura ta soma rasa natsuwarta, sai a sannan ya saka gilashin idonsa ya cigaba da kallonta ta yadda ba zata fahimta ba, zuciyarsa cike take da tambayoyin da ita kadai zata iya amsa mashi su, ita kadai duk wannan abun akanta? Be tana jin labarin da ya shiga zuciyarsa ta tsuma zuciyarsa ba irin na yau, bw tana jin labari mai tausayi da tashin hankali ba irin yau, kuma a haka she's still alive tana ta farincikinta ita da yaranta, har akai abunda za ayi a gurin aka tashi be kawarda hankalinsa daga kanta ba.....
______________________________
Yau na yi 5,176k words na biya bashi 🙌😍
#Team Aminu
#Team Abdallah
#Team Ahmad
#GN
#KhadeejaCandy
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: I think you'd like this story: "GOBE NA (My Tomorrow)" by KhadeejaCandy on Wattpad https://www.wattpad.com/story/247701926?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=story_info&wp_page=story_details_button&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZkyWKvWuHXhIRzZDEluZ%2BuUXayIbDBikXAQA%2BM4xeAsJY%2Fh9rtovTCoQphCdFYUPM4K1nHTquOLcFfifZUhwZ0RRyERddTi4AY1OYORg8gUhN9fNU%2FLr6t3SMGO9O8M2
*GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣3️⃣
ABDALLAH POV.
He's walking slowly tun daga inda ya aje motarsa har zuwa cikin falon Hajiya, gidan sai kamshin sabon fenti da aka yi jiya yake. A gajiye ya shigo falon sai ya tarar babu kowa sai sanyin ac. Zaunawa yai a saman sabin kujeru da Hajiya ta sake ya ciro wayarsa yana latsawa, ya kusan minti talatin a haka sannan Hajiya ta fito rike da wuka da katon mangoro a plate.
“Husani kai ne ka shigo”
Ya dago a hankali ya kalleta.
“Eh Hajiya barka da yamma”
“Yauwa sannu dai, ya aikin? Yau baka shigo da safe ba”
“Na fita aikin ne da wuri saboda tiyati za ayi, shiyasa”
“Okay abincin fa akawo?”
“A a gida zanje yanzu”
Daga haka bata sake ce masa komai ba, shi ma kuma be ce mata ba, daman kusan kullum idan ya shigo gidan shiru yake ko wata maganar ake sai daiya bisu da ido.
“Ana ta shirye shiryen biki har yanzu baka ce komai ba”
“Allah ya sanya alheri”
Ya fada a takaice, sai kuma yai shiru kamin ya sake kallonta.
“Hajiya na yi wani laifi”
A take ta dago kai ta kalleshi da sauri.
“Mi kai?”
“Kin min tsakani da Halima, tun daga lokacin ban sake kula ta ba, sai kwana goma sa suka wuce, na ganta a hanya tana tafiya da tufafin da be dace ba, hakan yasa na tsaya na dauke a motata saboda kare mutuncinta, ki yafe min dan Allah”
“In ban da kai da abun ka, miye amfanin kare mutuncin macen da bata san mutuncin kanta ba, da wata ce ai ba zata yi shigar banza ta fita ba, talla take yi kenan Allah ya kyauta”
Yawu ya hade da karfi da ba Hajiya ba ce da be lamuncin jin wani kalami marar dadi daga bakin kowa ba akan Halimatu idan ba zai iya cewa komai ba to ba zai saurara ba.
“Wato dai na gane ba zaka iya fita daga tsafgar yarinyar nan ba, saboda ka samu salama kuma ku samu fahimta da dan'uwanka yasa na yi muku tsakani amman hakan be wadatar ba, tun da ga shi nan har yanzu ba ku jutuwa da juna, kuma ka kasa daina kulata, har yanzu dai tana nan cikin ranka, yarinyar da ta haifarda rashin jituwa tsakaninku? Yanzu shirye shiyen auren dan'uwanka ake amman babu ruwanka komai sai dai ka bishi da ido haka ake? Ku uku kawai Allah ya bani idan ba ku hada kai ba ya kuke son zama?”
“Ba daga ni ba ne Hajiya, Abdulhamid yana ta ganin laifina ne har yanzu, ko magana nai masa sai idan yaga dama zai amsa ni”
“To ai dole ya rika maka haka, taya zaka rika bibiyar matar da ya saka? Wacce ta zama makiyiyarmu? Ta ruguza rayuwarku?”
Kallon mahaifiyar tasa yai ya dauke kai, wani lokacin idan tana yin abu kamar wacce bata taba karatu ba, ne san abunda yasa son zuciya yake rinjiyarta ba. Be ce sake ce mata uffan ba har tai fadan ta gama, sannan yai mata sallama ya fice zuwa gidansa. Da dan kuzarinsa ya shiga gidan yaransa na harabar gidan suna wasa kasancewar yau Thursday after school babu islamiya a yau. Da gudu suka zo suka masa oyoyo ya daga su sama yana dariya ya sauke sannan ya rika hannunsu suka shiga cikin falon, a falon ya sake musu hannu ya nufi kitchen gurin da yake jiyo motsin Suwaiba. Daga baya ya rumgumeta yana sumbatar gefen kumatunta.
“Madam me kike girka mana”
“Me nake girkawa dai ni da yarana kai da bazawarar ka ta dauke maka nauyin cin abincin gidana”
Ta fada tana yatsina fuska. Sai yai murmushi rabon da Halima ta aiko masa da abinci tun ranar da ya dauko ta a mota, ya juyo da ita tare da saita idanuwansa cikin nata.
“Kin ga abunda ke hada ni da ke mita, da rashin yarda, wanda ya baki labarin tana aiko min abincin be baki labarin ta daina ba?”
“Kana kareta ne kawai, amman yq za ayi ta daima bayan ta fara kuma silar hakan ka daina cin abincin rana a gidanka? Daman can ai irin yan barikin zaurawan nan sun fi kowa iya karuwanci”
“Abunda take min kyautatawa ce kawai a matsayina na dan'uwanta kuma kin fi kowa sani Halima na tsattsiya ce”
Yana fadar hakan ya sake ya juya ya fice daga kitchen din fuskarsa na nuna rashin jindadin kalaman Suwaiba, tabe baki tai ta bishi da kallo haushi, ita kadai ta san abunda take ji ta rasa gane wani irin so yake ma Halima? Ko da yake ba laifinsa ba ne laifin Halimar ne daman shi namiji ai kamar yaro ne, duk inda aka bi da shi can yake, ta dade tana masa maganar abincin da Halima take aika masa a office duk kuwa da kasancewar ya sha nuna mata cewar baya son maganar, ta hanyar Yayanta da ke aiki Asibiti a matsayin nurse ta samu labarin.
“Sai na ci miki mutunci Wlh, sai na bayyana halinki a gaban kowa, daga lokacin zan gani idan za ki sake bibiyar Abdallah banza ballagaza kawai, in banda jahilci taya zaka auri yaya kuma ka koma bibiyar kane, kaji iskanci, sai an tozarta ki Wallahi”
Ta fada tana kwafa sannan ta juya ta cigaba da aikinta...
AHMAD POV.
tukin motar kawai yake amman hankalinsa yana can ya tafi gurin labarin da ya ji, sai a yanzu ya fahimci a kashi 100 na kaddarar rayuwa shi ko kashi daya be dauka ba, domin shi ya da mata sai mahaifi kawai ya rasa, amman ita ta rasa abubuwa da yawa a ciki akwai farinciki akwai gata akwai mutunci, a haka kuma har tana filin sake daukar wani kalar bacin rai a zuciyarta, tunawa yai da yadda take yawan masifa wata kila saboda tana cikin damuwa ne, ta yi kokari ta jajirce da har bata haukace ba ko kuma wani ciwon ya hana ta tashi kamar yadda shi a yanzu ciwon zuciya yake neman kai shi kasa. Tunawa da yai da irin abunda yai mata a wacan lokacin da kuma kadeta da yai yasa jin wani iri, anya mai irin wannan rayuwar ya cancanci a sake shimfida masa wata bakar magana ma balle har a aikata masa wani abu marar dadi? An keta mata an keta haddin yarta shi ya fi komai tsaya masa a rai, see yadda yake kyamar auren matar da ta auri wani auren sunna ma, to ita faya zata ji an yi mata da karfi? And ayi wayarta yar da bata san komai ba? And a lokacin kwatar hakkin yarta mijinta ya saketa bayan kuma kanensa ne ya ketawa yar haddi, wani irin mugun miji ne wannan? Baya son ta aureta ne? Ko dole akai mata? Aunata yake a matsayin Siyama, ya zai ji idan wani ya taba masa kanwa kamar haka? And the most saddest thing bata da mai tsaya mata tun a wacan lokacin, she's the first born ya tuna a cikin wasikarta ta fadi hakan, and the other sad part is ya kara mata damuwa da zarginta da mutuwar Namra, sai a yanzu yake gode Allah da Hajiya ta hana shi daukar mataki a kai da ya cutar da innocent soul.
“Gwarzo... Ba gida za mu je ba?”
Sai a lokacin ya tuna ba shi kadai yake a motar ba, Hajiya tana baya tare da shi.
“Gida za mu je”
“Na ga ka dauki wata hanyar ne”
Sai a lokacin ya lura, bakinsa ya cikawa iska ya busar sannan yace.
“Zagoyo zan yi”
“Okay, bikin nan ya kayatar sosai fiye da yadda aka saba yinsa a shekara, wai ka gane wacce ta ci gasar nan kuwa?”
Hajiya na yin maganar zancen yaranta ya fado masa, na cewar idan ta ci zata biya musu kudin makaranta.
“Wow....”
Ya furta a fili yana jinjina irin jarumtarta da karfi zuciya. Hajiya kuma sai ta dauka da ita yake sai kawai ta cigaba da shimfida masa labarin.
“Wannan ce fa mahaifinyar su Namra yarimyar da ke tare da Baby Namra, ashe har yanzu bata manta da ita ba, tace idan ta ci sadaukarwar ta Baby Namra ce”
Be ce komai ba sai tukin yake a hankali yana jin wani abu na masa yawo a zuciya na rashin jindadi har suka isa gida.
“Labarin ma da aka karanta ina kyautata zaton na mahaifiyar yarinyar nan ne Halima.... ”
“Halima...... ”
Ya maimaita sunan yana kokarin juyowa ya kalli Hajiya, be taba sanin sunanta ba sai yau, duk kuwa da aikin da take a kamfaninsa, sunan da ya fi ko wane suna yi masa dadi a duniya, har yanzu yana ganin yadda ya wulakanta a kamfaninsa a lokacin da ya bukaci a canja mata position sai a yanzu yake ganin hawayen da take da irin rokon da ta soma masa tana kuka tana fadar dan Allah kar ya koreta tana bukatar aikin nan, and in the restaurant a vip 1 a lokacin da ta zauna a saman kujerar sa matarsa take zama, he remember wadansu kalamai da ta fada, wacce take nan ta yi sa'ar ba kamar ita ba, daman duk wannan take nufi?
“Oh ya rabb”
Ya furta a fili gaba daya zuciyarsa ta daure ta yi nauyi da tausayin Halima. Can ya tsinkayo Hajiya na kokarin fita motar tana fadin.
“Domin labarin da mahaifiyarta ta ba ni, yayi daidai da abunda aka fada a gurin nan kuma ga shi taje tare da yaran, ina jin labarin na gane ita ce, cikin ma uwar bata fada min duka ba, tun da wani abun sai a yanzu na ji, amman matar nan ta ga rayuwa Wallahi ban san lokacin da nai kuka ba”
Fitowa yai daga motar yana kallo mahaifiyarsa wacce ke sanye da tsadadden lace.
“Amman Hajiya ba ki taba fada min ba”
Hajiya ya kalleshi da kyau.
“Ina zan fada maka labarin makiyiyarka? Matar da kace baka son jin komai nata”
“Da kin fada min ko da a tsawace ne, ko kuma ki cilasta min saurare ai dole zan ji, wani mai imani ne zai ji labarin matar nan be ji tausayinta ba?”
Ya fada yana hade yatsunsa fuskarsa dauke ta tausayi.
“Duk lokacin da nai unkurin fada maka sai kace ba zaka saurara ba, tausayinta ne yasa na hana ka kaita kotu ai, ko lokacin da aka fada maka bata cikin hayyacinta ba cewa kai karya ne ba, saboda kawai ta kashe maka ya ne? Ni ko na san mai imani ba zai kashe rai ba sai idan wata kaddara ta fada masa, sai a yanzu da Allah ya kaddara ya bude maka zuciya ka ji komai”
Yes he remember an fada masa she's unconscious ya ki yarda, and he remember how her father beg him akan case din amman be saurareshi ba, and the slap a lokacin da ta kawo Baby Namra asibiti ya mareta har sai da ta fadi..... Ji yai wani irin abu na rashin jindadi da kyautatawa ya mamaye shi, be taba jin tausayin wani abu mai rai kamar a yadda ya ji tausayin Halima ba a yau, a waje daya kuma yana ta jinjina karfin hali da dakiyar zuciya.
Part dinsa ya nufa yana ta tunani kala kala yes hak rayuwa take zaka ga mutum kawai sometimes a cikin farinciki amman ba san abunda yake zuciyarsa ba, ba zaka iya fassara damuwarsa ko nasararsa ba, da ace be ji labarin Halimatu ba da har yanzu be daina mata kallon makiyiyarsa ba, wata kila da Allah kadai ya san irin abubuwan da zai mata....
A dare kwana yai da tunanin abun a ransa, duk kuwa da yasan condition dinsa rage yawan tunani yana ciki.
HALIMATU POV.
Labarina ya taba zuciyar mutane da yawa a guri kuma nima ya taba ni a karan kaina, domin sai rayuwar da tunanin gobena ya dawo min sabo. Iyakar kokarin da nai kar nai kuka a bainar jama'a ne, sai dai na zubar da hawayen da ban san adadinsu ba, an rayuwata ta lalace kuma an bata ta yata, amman na yarda da wani abu daya, ko dan yayana zan rayu, zan kara jajircewa zan tsaya tsayin daka na amsa sunan da Ummulkhar ta kira ni da shi wato Jaruma.
Rai na ya kwadaitu da zancen kudin da ta ware min a cikin albashin kamar yadda ta fada, sai dai ina tunanin karbarsu abu ne mai wahala a gurina domin zai iya zama silar da zata saka a gane ko wacece ni wanda hakan zai hanani sakewa cikin mutane.
Ba mu tashi daga taron ba na ji alert a wayata, na naira miliyan daya, aiko a take na nemi damuwata na rasa farincikin ganin kudin ya maye gurbinta.
Cikin murna muka fita daga taron wani abun burgewa sai muka zama abun kallo har da masu dauka hoto a tare da mu da award din da aka ba mu, ina yin gaba kadan na hadu da blessing abokiyar aikina, sam ban san ta zo taron ba sai da tai min magana mun gaisa da ita ta tayani murna sannan ta gaisa da su Namra tana fadin ashe ina da yara. Sai nai murmushi.
“Ke ma ai kin san ina da yaya”
“Eh amman ban dauka har hudu ba, kuma kyawawa da su har sun fiki kyau”
Dariya nai sai ta soma tambayar dalilin rashin zuwana aiki kwana biyu. Ban boye mata komai ba na fada mata cewar wani dan'uwana ya hana ni aikin ne saboda uniform din be dace da ni ba. Dariya ta fara min tana ta mamakin wautata, wai ya zan daina aikin ban je ma fada musu dalilina ba idan ba su aminta su canja min kayan ba ko kuma gurin aikin ba sai na daina amman a haka ai ba ni da hujja kuma na bar damata ne. Ta yi tamin magiyar na je gobe na fada musu haka idan basu yarda ba sai n aje aikin, ni kuma na amsa mata da to duk da nasan ba za su yarda su canja min ba, amman yanzu na samu kudina zan iya yin sana'a ta kamin na samu wani aiki, tare muka jera muka fita tana fada min wata mata da ke yawan zuwa nemana tun da na daina zuwa aikin har number wayarta ta bari tace idan na zo a kirata. Ni kam mamaki ya cika kuma tsoro ya kama ni wacece kuma? Allah yasa ba wani karin damuwar ba ne, can kuma matar Kabir ta fado min a rai wata kila ita ce, dan nasan wannan mugun Ahmad din ba zai kyale shi ba, domin ko a yanzu na lura da kallon bakincikin da yake min, na ja masa fada da mahaukaci kuma ga shi na ci gasa na san hakan ba karamin zafi yai masa ba.
Idan na naje aikin Yunus din zan yi ma magana ko Tahir wanda shi ne shugaban sashen mu, shi kam na san ko kallo ban ishe shi ba kuma ba zai saurare ni sai dai ma ya fada min wata bakar maganar.
A ranar gidanmu ya cika da murna ba mu kadai ba har da makotan da suka samu barin sai da suka zo taya mu murna, Inna da Mama duk tsoro ya kama su wai kar a biyo dare ace sai an bada miliyan din, har ta hana a fadawa. Ba su kadai ba ni kaina na kwana da tsoro a ranar saboda halin tsoro da kasar nan take ciki abu kadan zai tsonewa wani ido.
Washe garin na tashi raina fes zuciyata kal babu damuwa ko kadan sai farinciki da annushuwa rabon da na samu kaina a haka har namanta, domin a yanzu bayan damuwata har da ta Abdallah tana damuna, tun daga wacan lokacin da yai min magana ban sake sakewa ba, su namra ma baki har kunne suna ta far'a, ban barsu sun je makaranta ba sai da nai kusu kashedi akan kar suje