Showing 216001 words to 217237 words out of 217237 words
wacce yake aure ta riga ta lalata mahaifarta. Ga dan'uwansa wato Sadi ya zama aban tausayi domin ciwo ya kai shi kasa babu kyau gani, sam ba zaka ganshi kace shine ba, nikam hakan dadi yai min domin kuwa Allah ne ya nuna masa iyakarsa tun a yanzu kamin ayi wani hisabin a lahira....
Kiri da muzu Ya Omri ya hana ni zuwa barkar haihuwar da Suwaiba ta sake yi na macen da Abdallah baya so, duk kuwa da kasancewar ita din ta zo a lokacin dana haifi yan uku, sai dai mijinta be zo ba kuma be aiko ba be kuma kira ba. Sai na rasa yadda zanyi taya zata haihu na ki zuwa bayan kuma na sani, ai sai ga rashin kyautawa ta, da na san zai hana ni tun farko da ban tambaya ba sai na masa wata karyar na tafi.
“Idan ban je ba ba zata jidadi ba ko Mama ba zata jidadi ba kuma Wallahi ban kyauta ba, komai fa ta wuce abunda ya faru duk a baya ne”
Banza yai min yana ta wasa da yaransa sai kyalkyalar dariya yake shi da su kamar ma be san ina zaune a dakin ba. Can ya dago ya kalle ni.
“Magana kike?”
“Barkar Suwaiba”
“Idan ba bacin raina kike son gani ba ki daina min maganar nan, haka kawai ki taka ki tafi gidansa yai ta kallonki”
“Ba zanje lokacin da yake nan ba”
“Na ce ba za a je din ba, ko a munafunce ban amince aje ba”
Ya fada fuskarsa babu alamun wasa, har yanzu yaki yarda Abdallah ya daina so na ya kasa manta abunda ya faru na rasa wane irin kishi ne Ya Omri yake fama da shi ko mai sunan Abdallah baya so, Aminu ma dan ya zame masa dole ne. Duk yadda na so nai convincing dinsa ya amince fir ya ki a dole na hakura sai dai na siye abubuwa na bada nace a kai mata wanda na san hakan ba zai mata dadi ba.
Ranar wata Lahadi ina zaune dakina rike da waya ina chat ya shigo rike da wasu takardu ya zauna kusa da ni yana fadin.
“Ina tunanin bana da mu za a yi hajji”
Ban san lokacin dana jefar da wayar hannuna ba na tashi na fuskance shi baki sake ido har gurin gira.
“Da gaske?”
“Yes tun da yara sun yi kwari ai ya kamata ke ma ki kai ziyara, sai mu koma tare, idan Allah kuma ya amince mana kuma sai mu yi ummara idan lokcin yayi”
Rumgume shi nai cikin wata irin murna marar misaltuwa sai ya fara dariya yana fadin.
“Idan mun dawo zaki karo min yan uku”
“Har yan goma zan karo maka”
Ya fara dariya yana rumgume ni.
“Kamar gaske, salon kukan ya dawo ta fitina ko”
Murmushi nai sai ya rike fuskata yana kallon cikin idona kamar ba gobe.
“I love you so much”
Ya fada da rada sai ya sumbanci goshinsa na mayar masa.
“I love you more”
Abunda ban sani ba, ba ni kadai Ahmad ya biyawa ba har da har da Mahaifiyarta da Inna, bayan gyaran gidan da yai musu ga dawainiyar kai abinci duk wata kusan hidimarsu ta dawo kansa, tsanannin dadi da farinciki har na rasa inda zan saka kaina. A tare mu kai hajjin da su wanda su kansu ba su taba saka ran wata rana za su tafi ba balle kuma ni, sai gashi komai ya canja mana kamar ba mu ba, bayan wuya sai dade kuma mai hakuri kan dafa dutse, abunda ban taba zato da tsammani ba shi yake ta zuwa min ba ni da matsala da Hajiya sai dan abun da ba a rasa ba, kusan ma yanzu tafi son jikokin fiye da da domin a yanzu Siyama tai aure tana dakinta ta bar Hajiya sai idan ta kawo ziyara, kamar dai su Hafiza da Husna da Aisha hankalina a kwance yake a yanzu ga yara a gabana gwanin sha'awa muna rayuwa cikin daula kamar gidan ubansu.
Gobena tai kyau, Gobena ta zo min ta inda ban zata ba, Gobena ta same min mai Annuri da haske.
***** ******* ******* *****
AFTER SOME YEARS...
Da gudu Amal ta fito dakinsu Adnan ta ho kaina kamar zata fada kan tsohon cikin da ke jikina sai kuma ta dawo bayana ta boya, Adnan din sai kokarin kamota yake.
“Ya akai?”
“Momy wai ina operating system tazo ta karbe”
“Momy ba tashi bace ta Anty Namra ce kuma tace kar na bari ya dauka”
“To ina ruwanki ki bani karatu nake”
Sai a lokacin na daga kai na kalleshi.
“Kai ina taka?”
“Ya ki tashi Sudais ne ya saka mata ruwa”
“Amal ba shi idan ya gama sai ya baki ki aje masa”
“A a Momy tace kar na bashi”
“Zan barshi ya doke ki fa”
“Ni dai ba zan bada ba gaskiya”
Ta fada tana make kafada.
“Je ka dauko ta Aiman kyale ta yar neman fitina”
Da huci ya nufi dakinsu yana fadin duk da shiga hannunsa sai ya doketa, daga inda take tsaye ta rika masa gwalo tana cewa.
“Ai dai na hana, kuma idan ka dake ni idan Daddy ya dawo na fada masa, ai yace ka daina dukanmu”
“Bana son hayaniyar nan sauka saman kaina”
Na daka mata tsawa sannan ta sauka saman kujerar ta nufi gurin Lil Namra, tashi nai na nufi bedroom dina ina tafiya daker......
*TAMMAT BI HAMDILLAH*
Godiya ga Allah mai kowa mai komai wanda ya bani ikon fara rubuta labarin nan 8 months ago har na kawo yau. Darasin da ke cike Allah ya bamu ikon amfani da shi ya yafe mana kuraruranmu.
Godiya ga makaranta labarin Gobena a duk inda suke, da yawa mun fara rubutun nan da wasu amman ba mu karasa tare ba, sakamakon yanayin labarin, wasu sun fada min basa son labarin da babu soyayya wasu su ce min wahalar Halima ta yi yawa sun daina karantawa so so kaza kaza, a haka dai na daure na cigaba da rubutawa, Na fada tun farko cewar ban sani ba ko labarin zai muku dadi ko akasin haka domin ba zallar soyayya ba ne, rayuwace ta kalubalen da fadi tashin na rai da kaddara, ni na san akwai wadanda suka fi Halima shiga gararin rayuwa a zahiri, kuma bayan wuya sai dadi, sai gashi ina tsaka da rubuta nai ta haduwa da mutane masu kwatanta rayuwarta da ta Halima wata ma idan ta fada min halin rayuwarta wallahi har ta fi Halima shiga matsala, ban da wace akwai tace min sak yadda Aminu yake haka mijinta yake, akwai wacce tace min yadda Sadi ya lalata yar dan'uwansa Namra, haka kanen mijinta ya lalata yarta, wasu kuma matsin lamba ce daga iyayen miji kamar yadda Halima take sha.
Ina matukar godiya kuma ina jinjina gurin wandanda suka jure karanta wannan littafi har muka kawo yanzu Allah yasa mu amfana da darasin dake ciki.
Godiya gare ku yan wattpad, da yan Whatsapp, da facebook i love you All Fisabilillah ina godiya sosai Allah ya bar ran so.
1 ina ya fi burge ki a cikin littafin nan?
2 Mi ya fi baki tausayi?
3 ina ya fi baki haushi?
4 ina ya fi saki dariya?
5Wane darasi kika koya a cikin littafin nan?
6 Any kuma zaku iya yarda da kaddararku kamar Halimatu?
Ance bayan wuya.......☺
*** *** ***
Sai kuma idan mai kowa mai komai ya amince min mun hadu a littafi na gaba.
Best regards 💚💛💜💙❤
Khadeeja Candy 🌺😍😘