Showing 171001 words to 174000 words out of 217237 words

Chapter 58 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

204

memories we share together kamar yadda ya fada, babu abunda na fi tunawa kamar tears din da muka share with one tissue, and location da yai maganar wai ko dai ina son sa ne? Samun kaina nai da murmushi, kamin wani lokacin bachi yai gaba da ni.
Na farka raina Fresh har wani shauki nake ji, domin ina aiki ina yan wake wake na, ina cikin shiryarwa su Namra su tafi makaranta muka ji muryar wata mace wacce hausa bata isheta sosai ba.

“Dan Allah wacece Halima”

Zumut nai na fito ance son kira kamar bazarawa, na amsa da cewar ga ni ina kallon matan ashe ba daya bace sai dai dukansu su biyun suna sanye ne da uniform din yan sanda. Kamar jira suke na amsa suka nufo inda nake suna fadin.

“Zamu je da ke office din mu ki amsa wasu tambayoyi”

“Me nai?...”

Ban gama rufe baki ba suka rika ni muka fara ja in ja da su, da gudu Hafiza ta zo ta buge hannu police din ta hau ta da masifa.

“Mi tai muku? Haka kawai za ku shigo cikin gida mu kamata? Wace duka ta baku izinin shiga gidan mutane anyhow”

Police din ta nuna ta a fusace.

“Ke mahaukaci ki san abunda kike yi, karki ce zaki taba police zan ci mutuncinki, marar kunya kawai”

“Yes louder pls mu nan gidan sai mu kashe mutum ba komai ba ne a gurin mu, dan haka mun fiki tantiranci”

Cewar Hafiza tana zare mata ido kamar ba da police take fada ba. Sai da Mama ta daka mata tsawa sannan ta umarce da ta dauko min Hijabina.

“Amman Mama...”

Hafiza bata gama fadar abunda zata fada ba Mama ta tari numfashinta.

“Dauko mata Hijabinta na ce, duk inda za a je indai tana da gaskiya gaskiyarta zai fito da ita, Allah yana tare da mai gaskiya”

Ranta be so ba taje ta dauko min Hijabi na karba na saka, sai da muka fara tafiya sannan yarana suka fashe da kuka, ba ma kamar Amal wacce ta biyoni har kofar gida tana kiran sunana.

“Momy.....”

Ban san lokacin da hawaye ya wanke min fuska ba, ko ba komai sun tozarta ni, sun saka ni a motar police patrol, duk wanda zai gan ni a ciki dole na zargi wani laifin na aikata, duk kuwa da kasancewar ban san abunda nai ba, ga kuma mutane da suka tara mana a kofar gida, domin motar har da maza sai suka tsaya daga waje. Ina jin lokacin da Inna take tambayatar wane station ne za a kai ni sai mai tukin motar ya amsa mata da.

“State CID”

Har muka isa gurin ban daina tunanin abunda na aikata wanda zai saka ayi min wannan kamun ba ban san na yi fada da kowa ba, ban san na yi wa wani kazafi ko kage ba, ban san mi na tarewa wani ba. Abun da kamar wulakanci domin muna isa suka saka ni a cell suka rufe, ko minti biyar ban yafe ba ba na hango Inna tare da Aisha da Mama da, like ten minutes wani kanen mahaifin mu ya iso gurin tare da yayansa.
Na yi minti talatin a ciki sannan aka fiddo ni aka nufi wani office da ni, ina shiga na samu Hajiya a zaune tare da yan'uwanta, kallo daya na yi mata na gane dalilin kamoni da akai. Mutumen da ke zaune a gabamu yana karanta min abunda ake zagina da shi dan Hajiya Altine wato yayar Hajiya, na san shi ya san ni amman a yau sai kamar be taba ganina ba.

“Ni ban san inda Abdulhamid yake ba, kuma ban san inda Abraham yake ba, nan fa cid ce babba kuma kai police ne Yusuf kai baka sani ba ni ya za ayi na sani?”

“Karki fada min maganar banza karki sake kiran sunana ki dauka ba ki taba ganina ba a rayuwarki”

Shine abunda ya fada min a tsawace, sai na kalli Hajiya na ce.

“Ba kiyayya ta shiga tsakanina da Abdulhamid ba, soyayyah ce kuma shi ya ji ba zai iya zama da ni ba ya rabu da ni, me zai saka ki yi min wannan zargin? Me nai miki Hajiya wannan maganar wace irin kiyayya ce?”

“Au baki sani ba? Munafuka, ai auren da kika masa ba na Allah bane, kin janyo hankalinsa saboda ki ci dukiyarsa tun da kin ga shi yafi dan'uwansa kudi, to shi aiki yake yana sai da motoci, dan uwansa kuma likita ne kawai, ko cikin nan Allah kadai yasan gaskiyarsa kin dauka ba zai yarda ta magana tun da kin shanye shi kamar yadda kika yi ma Abdallah, duk yadda akai da hadin bakinki aka sace min d'a, tun da kin ga zai yi aure kin ji bakinciki, wai dan har baki da kunya kike soyayya da kanensa? Kin taba ganin inda aka auri yaya kuma yana da rai a auri kane? Wato gaki autar mata ko, ban cin kin raba kansu kuma ki shiga ki mulke mu son ranki ga bayi, kin ma ci uban rainin wayo Wallahi”

Haka tai ta jera min bakaken maganganu sai abunda ta mance, jikinta har rawa yake kamar zata dake ni. Ban taba jin nadamar aikata wani abu ba kamar auren Abdulhamid a wannan lokacin, sai dai bawa be isa ya wuce kaddararsa ba.

“Za ki fada mana da arziki ko kuma sai cilasta ki?”

“Ban san komai a kai ba”

Na fada ina hawaye, bana son fadar komai saboda kar na jefa Ahmad a matsala, kuma idan Hajiya ta san ta dalilina ne zata kara zargina ne.
Haka aka raya aka kada aka juya aka na tsaya kai da fata ina fadar ni ban san komai akai ba. Daker aka bawa kanen mahaifina damar shigowa cikin office din wanda shi ma kanene ga mahaifinsu Abdallah, babu irin maganar da be yi da Hajiya ba amman ta ki saurarawa ita ala dole sai na fadi inda danta yake.

“Hajiya zumunci kike kokarin lalatawa, abunda kike yi be kamata, da uban yarinyar da mijinki uwarsu daya ubansu daya, akan me za ki yi wannan abu? Idan Alhaji yana da rai ke kin isa ko hararar zuri'arsa ki yi? Wallahi na tabbatar da ace Alhaji yana da rai yau ba za ki kwana a gidansa ba”

“To sai kaje ka taso da shi a yanzu ka saka ya sake ni, ni ba ku ga abunda tai min ba ta raba kan yayana, da gangan ta kulla soyayyah da Husaini yanzu kuma ta zo ta auri Hassan, yaro ya bata ga ayoyi tambaya akanta sai ku ce na kyaleta saboda ni ban san zafin haihuwa ba? Wallahi ko Alhaji ne a raye ba zai yarda a taba masa yayaba”

Kamar wacce take fada a ciki unguwa haka ta rika daga muryarta tana fadi abunda ranta yake so, Baba Buhari sai yai shiru kawai yana mata kallon takaici. Muna office din har la'asar, ganin na ki amsa laifina na ki na fadi komai yasa Yusuf din yace a shiga da ni wani daki, sai ya hada ni da wasu mata police suka tafi da ni wani bangare na gurin, suka shiga da ni cikin wani daki mai hudu, a yadda na fahimta abun kamar hadin baki ko ma nace cuta ce zallarta domin a iya sanina ko maza sai idan an dokesu kuma an kwana biyu ba su fadi kowa ba sannan ake saka a gurin, amman ni kamar daman can suna jira na ne. A rayuwata ban taba ganin inda aure ya zama kiyayya ba kamar nawa da ya zame min haka da Hajiya.

“Ba zaki fada ba?”

Dayar ta fada min cikin tsawa.

“Ni ban san komai ba”

Na amsa ta har lokacin zuciyata bata ayyana min na fadi komai ba. Wata hula suka saka min a saman hijabin da ke kaina, sai kuma suka cire min Hijabi suka saka min hular, wani namiji dake gafena na ga ya kunna wani abu sannan na daki hular kan nawa, a maimakon na fara bayani kamar yadda aka ce min mutane suna yi sai na nemi hankalina na rasa.




AHMAD POV.

Murmushi yake yana kurba tea dake hannunsa, ya nade kafafauwansa yana zaune gaban Hajiya, ita ma murmushin take tana fadin.

“Haka nake son mace tana da tsantsaye da rayuwa, kasan da wata ce kana bata motar nan zata hau murna ta karba jiki na rawa”

“Sosai ma Hajiya, kuma Wallahi wannan abun ya kara min kirmarta sosai a idona, sai na ji ta kara shiga raina sosai Wallahi”

“Amman ka mata magana kuwa?”

“Har ynzu dai, ki taya ni da addu'a, tana da dan taurin kai dan kadan kuma tana da wuyar sha'ani shi ma kadan, saboda tana tsoron rayuwa”

“Allah ya tabbatar da alheri yasa kuma ya karba maka”

“Amin Hajiya Amin”

Ya amsa cike da jindadi addu'ar mahaifiyarsa, sannan na aje mug din ya mike tsaye.

“Bari naje office”

“To Allah ya tsare, ka dai kusa zama babban mutum kamar da”

Murmushi yai ya fice yan shafa kansa. Driving yake zuwa office cikin nishadi da annashuwa, haka nan kawai idan ya tuna yayi waya da Lims da daren nan sai yaji wani dadi ya lullubeshi. He arrived in time just to see her face yana son yadda yake tsawa jikin windows yana hangota musamman idan zata bude windows din office dinta. Haka yai ta tsaye a gurin tun yana duba agogon ya ga nine saura har ya koma ya zauna can kuma ya taso ya tsaya ya koma ya zauna har kusan 11am abunda bata taba ba, domin duk dadewarta bata wuce 9 ko 9:30.
A take ya ji duk ya damu, wayarsa ya dauka ya kira wayarta sai ya jita kashe, a lokacin ne ya fara tunanin ko dan abunda ya faru jiya yasa yau ta ki zuwa aiki kuma ta kashe wayarta? Sai duk yaji ya shiga damuwa, har kusan 3pm ba wani labari, line ta ya sake gwadawa, sai yai sa'a wannan karon ya shiga, kamin a dauka duk ya matsu.

“Hello Lims”

“Ba Halima ba ce kanwarta ce Hafiza, Halima tana gurin yan sanda”

“What? Miya faru?”

“Dazun suka zo suka kamata da safe, ba irin wulakanci da ba su mana ba nan gurin wai suna zarginta da hannu a batan tsohon mijinta, tana can hannunsu sun kulleta”

“What? Wane station din ne?”

“State cid office”

Kashe wayar yai ya mike tsaye cikin zafin rai da rashin natsuwa na kira lauyansa, sai da yai masa bayanin komai sannan ya fada masa cewar su hadu a can din.
@360 na isa gurin, ko motarsa kadai ka kalla kasan babban mutum ma'ana mai ji da naira balle kuma shigarsa ta suit da yai, yana shiga cikin gurin lauyansa ya iso, duk wani shiga da fita da ake ciki lauyansa ne yake magana bashi ba, suna shiga office din aka kira Hajiya ta iso tare da Hajiya Rukaiya, ba su zauna ba Abdallah ya shigo office din shima.
Ahmad na kallonsa ya watsa masa wani mugun kallo.

“Kai kasa aka kamata kenan?”

Abdallah yai kamar be ganshi ba ko inda yake zaune be kalla ba balle har ya amsa shi. Hajiya ta kalli Ahmad da kyau tace.

“Waye kai? Ko kai ne Abraham din? Ni na saka aka kamata ba shi ba”

“To kina nan zaune za a fito da ita, kuma idan akan Abdulhamid ne ni zaki saka a kama ba ita ba, nine silar kama shi da akai yi ba ita ba”

“Kai Malam karka fada mana maganar banza, idan baka san darajar iyayenka ba ni san nawa, karka ce zaka yi ma mahaifiyara rashin kunya”

Abdallah ya fada a fusace. Sai Ahmad ta tabe baki yana kallonsa.

“Kasan darajarta ka bari ta ci mutuncin wacce bata da laifi?”

“Hey my friend don't tell me rubbish”

“An fada maka who are you?”

“Ai kai za a tambaya, ka so nan kana wani nuna isa wa kake a gurin Halima? Wallahi idan na so ko kallonka Halima ba zata sake yi ba stupid human being”

“Oh really? Ni ko zan nuna maka wani abu ne a gurinta, ka jira nan da one month sai na nuna maka waye ni a gurin Halima, sai ka gane darajata ta fi taka a gurinta”

Yana fadar haka ya mike tsaye da zimmar zai fita sai ga lauyansa ya shigo yana fadin su tafi gata can an saka a mota. Ba shiri Hajiya ta mike tsaye.

“Ina Yusuf din yake? Ya za a saki yarinya bata fadi komai ba? Ni ina dana yake”

Juyowa Ahmad yai ya kalleta.

“Dan ki yana Abuja hannun DSS kije ki yi fada da su idan kin isa, and idan wani abu ya samu Halima dukanku ba zan kyale ku ba har kai”

Ya karasa yana nuna Abdallah. Abdallah ya masa wani mugun kallo.

“Look at you fool sai na nuna maka baka isa da Halima ba trust me.... ”

Ahmad be sake ce masa komai ba ya fice. Abdallah kuma ya hau rarrashin zuciyarsa domin ji yake kamar ya hau Ahmad da duka, Hajiya kan jikinta gaba daya ya gama sanyi jin Abdulhamid yana hannun DSS.


_________________
Guess what will happen next.
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy


5️⃣4️⃣

Yadda kafarsa take taka kasa da karfi ya isa ya isar maka da cewar ransa a mugun bace yake, balle kuma kai arba da kyakkyawar fuskar nan tasa wacce ta koma kamar bakin hadari idanuwansa gaba daya sun gama canja kala daga fari zuwa ja. Wani irin nishi yake irin wanda bacin rai ya dannewa numfashi, gumi kawai ke karyo masa daman can haka yake idan ransa ya bace sai gumi da dannewar numfashi.
Tare da barrister suka isa gurin motar, sai ya kai hannunsa ya bude gidan baya inda aka saka Halima, hannunsa ya kai ya taba fuskarta zuwa hancinta dan tabbatarwa idan tana raye, tabbas yaji tana numfashi sai dai kana kallonta kasan bata cikin hayyacinta.

“Wai hula suka saka mata”

Barrister Nuhu ya fada yana tsaye bayan Ahmad, dagowa Ahmad yai ya kalleshi da wata irin murya marar dadi saurari yace.

“Barrister ka shigar da karar matar nan da dan sandan da yai mata wannan abun, zan kaita asibiti yau yau nake son ka fara komai, ba zan iya yafewa ba, ba zan iya kyale wannan abun ba”

Yana fadar hakan ya zagaya zai shiga motarsa sai ga Inna da Husna sun iso.

“Mun gode Allah ya saka da alheri”

Be iya amsa su ba sai kawai yace.

“Asibiti zan kaita yanzu, asibitin Dr Nura za ku iya samun mu a can”

Yana fadar hakan ya bude motar ya shiga, yai mata key, kamin ya isa asibitin ya sake kiran wayar Halima duk da yasan bata hannunta amman yana son magana da Hafiza ne, akai sa'a wayar na hannunta domin ringing daya ta dauka.

“Hello, ke ce kanwar Lims ko?”

“Eh”

“A gabanki abun ya faru?”

“Eh komai a gabana akai, Mama ta hanani binsu ne can station din, baka ga wulakancin da sukai mata ba har waje suka fita da ita ba Hijab sai da na bita na saka mata mutane sai kallonta suke kamar ta yi sata, tun cikin gida ma yar sandar guda ta fara marinta”

Juyawa yai ya kalleshi Halima wacce idonta ke rufe sannan ya ce.

“Zan tura miki number wani barrister amman ki kira shi da line ki ba line Lims ba ki fada masa duk abunda ya faru zai shigar da kara akan case din”

“To ina ita Halima take?”

“Gata nan zan kaita asibiti”

Yana fadar hakan ya kashe wayar, ya sake waigawa ya kalli Halima, sai duk yaji tausayinta ya kara kamashi, da wani irin karfi ya daki sitiyarin motar, yana wani irin nishi kamar zai ciro zuciyarsa daga kirjinsa.
Yana kunna kai cikin asibitin wayarsa tai ringing kamar jiran kiran yake yai picking da sauri.

“Barrister”

“Na'am Ranka yadade ina son na san cewar shin abunda ake zarginta da shi, bata aikata ba din gaske? Kuma bata da hannu a batan mutumen?”

“Bata da alaka da shi mutumen yana hannun DSS, bata da hannu a batan sa ko wata mu'amala da shi”

“To ya akalarka take da ita?”

Juyawa yai ya kalli Halima sannan ya amsa ma Barrister.

“Matata ce....!”

“Za a shigar da karar a madadinta ne ita kanta ko kuma....!”

Shiru yai for a moment, yasan dai kotu ba a mata wasa, kuma shi din be riga ya auri Halima ba, idan aka shigar da sunan shi din mijinta ne kotu ta gano babu auri a tsakaninsu zai iya kawo musu matsala, how he wish ace ya aureta, ya tabbatar da yau Hajiya ko Abdallah basu yarda ko yatsa sun daga sun nuna mata ba balle har su saka a kamata.

“A madadinta zaka shigar, mutanen nan sun wulakanta ta Barrister i want them to regret, su nemi yafiyarta da kansu kuma kotu ta yanke musu hukunci so that's su san ita ma din mai matarba ce, har marinta sai da yar sandar tai kanwarta ta fada min komai, zan tura mata number ka zata kiraka ta maka bayanin komai, an ji hular da suka saka mata ko criminal sai wanda ya kai kololuwa ake yi ma haka, it's just like plan sun tsara kasheta ne kawai Allah be basu sa'a ba”

“Karka damu za ayi duk abunda ya dace”

Ya sauke wayar daga kunnensa daidai lokacin da ya isa harabar asibitin, sai da yai parking a emergency sannan ya fito yana kiran wayar Dr Nura, sai kuma yai rashin sa'a Dr baya cikin asibitin a lokacin sai dai ya saka ayi mata duk wani abu daya dace kamin ya iso. Gurin Ahmad ya samu ya zauna ya jimke hannunsa ya dora a saman bakinsa yana wani irin kashe ido zuciyarsa sai tafarfasa take.

“Sokon banza wawa”

Ya furta tunawa da kalaman Abdallah da yai.

“Daga ganin matar nan yayanta duk ba na albarka ba ne”

Ya mike tsaye yana jin wani irin tsanar Hajiya da Abdallah, daman can ya tsani Abdallah tun abunda ya faru a kamfaninsa wanda matar Abdallah tai yi ma Halima wulakanci.

“Saboda suna ganin bata da gata kowa ya kwaso hararsa sai ya zuba akanta”

Ya fada yana safa da marwa a gurin. Dr nura be dauki dogon lokaci ba ya iso gurin ya shiga bata taimako da kansa.
  Inna na isowa Mama ma ta iso tare da kanen mahaifin Halima, kana ganin fuskarsu kasan hankalinsu a tashe yake. Dukan yadda Ahmad yajin zafin zuciya sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login