Showing 186001 words to 189000 words out of 217237 words
ma zan yi na huta. Zaunawa yai a kujerar da ke fuskantar tawa yana kallon yanayina.
“Akwai damuwa a tare da ke, fada min minene”
“Ina son na aje aikina”
Na fada kai tsaye sai yai min kallon rashin fahimta mamaki karara a fuskarsa.
“As how...?”
“I want to resign”
“No i mean why?”
Na yi shiru kamar ba zan amsa shi ba.
“Saboda na ce zan rika kai ki kullum na dauko ki? Idan ba kya ra'ayi that's normal we can talk, kin san bana son bacin ran ki i won't force you”
“Ba Saboda shi ba ne, Abdallah ya bukaci haka.....”
Mikewa yai tsaye yana murmushin da zan iya kiransa da dariya.
“That stupid guy ko?....”
“He's not stupid, Abdallah yana da muhimmanci a rayuwata...”
“How dare you.......!”
Ban karasa ba ya daka min wata mahaukaciyar tsawa ya ture desktop din dake saman teburina ta fadi kasa har wani zaro ido yake kamar mai aljanu yana maida numfashi da karfi. Tsorata nai garin na mike tsaye kujerar da ke kai ta kade ni na fadi ni da ita, kamar yana jira sai ya zagayo inda nake ya risino kusa da ni ya nuna da yatsa.
“Ba a maganar wani namijin a gabana matukar ina son mace, ina da kishi ki kiyaye wannan, bana lamuntar ki kira wani namijin da muhimanci a rayuwarki idan ba mahaifinki ko dan ki ba”
Sai da ya fada min hakan sannan ya mike tsaye ya fice daga office din a fusace, nikam daman jira nake yana fita na tashi tsaye na dauke wayata da jakata na fito daga kamfanin gaba daya na dawo gida. Da daren ranar sai ga shi ya kira ni yana ta bani hakuri akan abunda yai min, na yi zaton ko zai yi magana akan aje aikin da nace zan yi ko kuma Abdallah amman be min ko daya ba sai da zamu yi sallama sannan yace min.
“Ki yi ma Mama magana, ta fadawa wadanda ya kamata sai su saka mana rana da za su zo”
“To”
Shine abunda na ce sannan ya aje wayar, na fada mata kamar yadda ya bukata sai dai maganar yarana na kasa masa ita kuma abun ya tsaya min a rai. Da aka fadawa kanen mahaifina sai suka nuna jindadinsu suka tambaye waye shi miye sana'ar shi a ina iyayensa suke duk na fadawa Mama ta fada musu, the following day suka saka musu rana assabar wato jibi kenan.
Kamin ranar Ahmad ya zo shi da abokansa biyu suka gaishe da Mama da Inna suka kawo musu alheri mai yawa da kudi. Tun daga ranar a kowa wane karshen dare wato misalin hudu da rabi ko hudu na kan tashi nai alwala nai sallah nafila raka biyu raka ta farko zan karanta fatiha da kulya'ayu sau goma, a raka ta biyu kuma na karanta fatiha da kulhuwallahu sau goma sha daya, bayan na sallame sai na sake sujada na yi salati sau goma, nai Subhanallahi walhamdulillahi har zuwa karshe sau goma, sai rabbana attina fidduniya hasana wafil'ahherati har zuwa karshe sau goma sannan na fadawa Allah bukatata na auren Ahmad idan akwai alheri a cikin Allah ya tabbatar ya bani ikon amincewa kuma ya saka min natsuwa, idan kuma babu alherin Allah ya kawo min mafi alherin shi ma ya zaba masa wata. Haka na jera rana ku nan kullum sai na yi sallah nan na roki Allah.
A iya tunani idan sun je za su gaishe da iyayene kawai wato kanen mahaifina da yayyensa, da kuma neman izinin zuwa fira kamar yadda ya fada min ashe ba haka ba ne. Da goma suka ce masu za su hadu misalin sha daya saura sai ga kiran kanen mahaifina ya shigo wayar Mama, be ce mata komai ba kawai yace ta ba ni wayar.
Na karba na kara a kunne ina masa sallama sai ya amsa min yai na mika masa gaisuwa ita kan be karba min ba yace.
“Ba ki fada mana idan sun zo za ayi daurin aure ba? Haka nan ake abu ba a fadawa sauran yan'uwa ba ba ayi komai ba? Gasu nan sun zo da mota kusan biyar da mutane da goron daurin aure da alawa da dabino”
Kasa magana nai, sai na ji abun wani iri wai daurin aure haka nan kawai daga zuwa tambaya sai kace na fado daga sama, to me ni ma zan ce? Nace a a karya yake ban ce a daura auren ba? Ko kuma na ce ban amince da hakan ba? Ban gama tunanin abunda zan fada ba na ji muryarsa yana fadin.
“Ke nake saurare Halimatu”
“Baba duk yadda kuka yi daidai ne”
“A a ke muke saurare, ke kika turo shi ai idan kin amince sai a daura ni ba mu da matsala idan kuma ba ki amince ba sai ya nemi sasanci a gurinki”
Gaba daya sai na zama kamar wata kurma, na kasa cewa na amince ko kuma a a ban amince ba, zuciyata tai wani irin nauyi kamar wacce bata tana aure ba.
“Na amince Baba”
Na fada hawaye na sauko min ina numfashi daker.
“To Ma-sha-Allah, Allah yasa alheri sadakin fa nawa za a yanka masa?”
“Baba duk yadda kikai daidai ne”
“To Allah yai miki albarka”
“Amin....”
Na amsa ina fashewa da kuka, ji nake kamar ban taba auren ba gaba daya abun ya zame min bakon al'amari, da gaske kuka nake sosai kamar wata karamar yarinyar da akai wa auren dole, Mama tai yi ta tambayar dalilin kukan nawa na kasa fada mata saboda kukan da nake ji nake zuciyata kamar zata fasa kirjina ta fito waje, idan aka tambaye ni dalilin kukana ba zan iya fada ba domin nima ban san abunda ya saka ni kukan ba.
Abu kamar wasa bayan minti talatin Kanen mahaifina ya kira ya fadawa Mama cewar an daura aure ne, ijiyar auren Ahmad uku ta hau kaina, a lokacin ne kuka yace dazun ban ci komai ba yanzu zan yi shi, kowa ya cika da tsananin mamaki a gidan sai dai dukansu suna murna sanin cewar alheri ne wannan karon yai musu bazata ba sheri ba, duk wanda ya tambayi mi nake yi ma kuka sai na ce ban sani ba domin har ga Allah ni kaina bansan dalilin hawayen ba.
Bayan kamar awa daya kanen mahaifina suka kawo goro da alawa da dabinon dauren aure sannan ya ciro dakina a aljihunsa ya rika hannuna ya danka min.
“Ga sadakin nan Halimatu, mun ce su bada 30k sai suka ce one million za su biya, babu yadda ba mu yi ba akan su rage amman suka ki, ina addu'a wannan aure yasa ya sanya nasa albarka ya saka alheri yasa gidan zamanki ne”
Da gaske miliyan daya nake gani a matsayin sadakina, ni Halimatu abunda ban tana gani ba ban kuma tana ji ba an biya sadakin bazawara har haka kuma bazawarar ma mai aure biyu da yaya hudu. Dana karba sai na bawa Mama na ce ta aje min, ita kuma ta kulla goron da alawa da dabino ta bada aka kai makota wai a fada musu an daura auren Halimatu yau.
A lokacin da su Namra suka dawo daga islamiya sai ta dame ni da tambaya.
“Momy aure kika yi?”
Na gyada mata kai.
“Momy da wa? Da wa? Da wa?”
Sai na kasa masa nata ita kuma ta kasa daina tambaya har sai da Aisha ta daka mata tsawa.
“Haba Namra wannan tambaya haka?”
“Momy Daddy kika aura?”
Na girgiza mata kai alamar a'a sai ta fashe da kuka sosai.
“Momy tafiya za ki sake yi?”
A gurin ta fadi da uniform dinta na islamiya tana ta kuka. Babu wanda ya rarrashe ta sai Hafiza ita ta fada mata wanda na aura kuma ta fada mata wannan karon ba zan tafi na bar su ba ne tare za mu tafi.
Har akai sallah la'asar ban daina ganin kamar mafarki nake ba, kuma ban daina hawayen ba, ina zaune saman carpet din dana kare sallah ina yi ma Allah godiya kuma ina kara rokon ya tabbatar da alheri a tsakaninmu, sai ga kiran Abdallah ya shigo, rawa jikina ya fara yi na fara kallon wayar kamar na ga wani dodo, na kasa daukar kiran har ya katse, lokaci daya na fashe da kuka marar sauti, na san duk inda yake a yanzu ya samu labarin daurin aurena wanda hakan ba zai masa dadi ba.
Bayan sallah magariba aka daf da sallah isha'i wani gurin ma har an fara yaron ya doko sallama ya shigo gidanmu da manyan ledodi.
“Wai gashi in ji Ahmad kuma yace yana sallama da Halima a waje”
Wani irin faduwa gabana yai sai naji kamar ban taba arba da shi ba, kamar wani bako na ji shi, har nai kamar ba zan je ba sai dai yadda Mama ta matsa min yasa dole na zari Hijab dina na saka na nufi kofar fita jikina ba kwari gabana sai faduwa yake. Can nesa da gidanmu na hango motarsa a fake sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na doshi gurin, kamin na karasa na ji an rumgume ni ta baya ya dora kansa saman wuyana.
“Al-hamdulillah...... Lims you're finally mine....”
“Mutane za su iya ganinmu”
Na fada ina hango daidaikun mutanen da ke can nesa da mu suna sha'aninsu wasu kuma na alwala. Sai ya sake ni ya juyo da ni yai kissing goshina kana ya hade goshinsa da nawa yana goga min hancinsa a hankali sai kallon cikin idona yake.
“Why are you crying?”
Ban ma san da hawayen sun zubo min ba sai da yai maganar, shiru nai ban amsa shi ba.
“Lims do you love me....?”
“Ban sani ba...”
Na fada da iyakar gaskiyata, wasu hawayen na sauko min, halshensa na ji a saman kunci na yana lasar hawayena.
“Wannan hawayen mai sanyi ne, ni na san kina so na Lims....”
Ya fada bakinsa na taba nawa murya can kasa kasa kamar mai rada, saurin lumshe idona nai muna ta shakar numashin juna....
___________________
Ayi hakuri two days mun yi biki shiyasa ban samu damar typing ba 🙏
Gashi nan na yi muku 5k words na biya bashi 🏃🏻🏃🏻🏃🏻
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lambobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:10 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣8️⃣
Raba jikina nai da nasa.
“Mutane za su iya ganinmu”
Be ce min komai ba yaja hannuna ya karasa gurin motar da ni ya bude gidan baya na shiga sannan shima ya zagayo ya shigo ya rufe sannan ya rika hannayena ya soma murzawa yana kallon fuskata.
“Ban miyasa nake jin ki a zuciyata fiye da kima ba, ina jin cewar na fi kowa dace a duniyar nan, a yanzu bani da wani buri sai na aurenki kuma ya cika ina son sosai, irin son da bana jin wani namiji ya taba miki shi, bana tunanin akwai namijin da ya fi ni son ki”
Ya sumbanci hannun nawa.
“Kamin na aureki, idan wani ya fada min zan aureki zan karyata shi kuma na fusata, amman a yau da Yayan mahaifin yai min albishir da cewar an daura aurena da ke sai na rasa inda zan saka kaina dan murna, na rasa abunda zan bashi na kyautata masa na goron abunda ya fada min, na gode da kika amince min na gode da kika ba ni damar shiga rayuwarki, na gode da kika karbe ni a duniyarki”
Ya karasa tare da kai hannunsa yana shafa fuskata, sai kuma ya jani jikinsa ya kwantar da ni ya rumgume ni sosai kamar ba gobe.
“I love you so much Lims”
Ya fada calmly kissing my forehead, dayan hannunsa kuma yana mutsa yan yatsun hannuna. Mu kai shiru kamar babu mu a cikin motar baka jin komai sai saukar numfashinmu, can ya saka hannunsa ya dago kaina ya dora bakinsa a saman nawa kamar zai tsosa sai kuma ya bar shi a haka yana ta kallon idona da na rufe, ji nai an busa min iska a saman idon hakan yasa na bude muna hada ido sai ya hade bakinsa da nawa, a hankali yake kissing din lisp dina sai kuma ya cire bakinsa a nawa ya kai gurin tsinin hancina ya tsosa sannan yai kissing forehead dina ya sake rumgume ni a kirjinsa tsantsa yana sauke ajiyar zuciya.
“What else i can say more than Al-hamdulillah, you're finally mine”
Muna haka na hango mota ta faka a kofar gidanmu, ina ganin motar na san cewa Abdallah ne, Ahmad kam be gane shi ba har sai da ya fito daga cikin motar ya jingina yana lasa. Wayar da ke hannuna tai ringing kiransa ya shigo, kallon wayar nai na kalli Ahmad sai na kasa daga kiran.
“Me ya zo yi?”
“Wata kila yana son magana da ni ne”
Bude motar yai yace min na fito muje, abunda ban so ba ke nan domin nasan ganin mu a tare da Ahmad ba karamin bata ran Abdallah zai yi ba, ba zan iya musa ma Ahmad ba kamar yadda ba zan so Ahmad yai abunda zai kara batawa Abdallah rai ba. Ya rufe motar sannan ya rika hannuna muka nufi gurin da Abdallah yake tsaye, daga inda yake tsayen ya dago idonsa yana kallon mu har muka iso, na kasa ce masa komai shi ma be ce min ba Ahmad ma be masa magana ba, sai kallon juna suke kana ganinsu kasan da akwai abunda kowa ya aje kasan zuciyarsa, Ahmad murmushi yake yana ta lilo da hannuna duk yadda na so na kwace hannun sai ya ki saki, na yi tunanin Abdallah zai yi wani abun ne ko kuma ya fada masa bakar magana amman ga mamakina sai ya sakar wa Ahmad murmushi ya mika masa hannunsa.
“Congratulations, that's good daman ka ce zaka nuna min ko waye kai a gurin Halimatu ko? Na gani yanzu ina taya ka murna”
Sai da Ahmad ya kalli hannunsa nasa sannan shima ya mika masa nasa.
“Thank you”
A lokacin ne Abdallah ya kalleni da murmushin a fuskarsa yace min.
“Ina taya ki murna”
Ni kam kasa amsawa nai sai Ahmad ne ya sake ce masa
“mun gode”
Sai ya bude motarsa ya shiga yai ribas ya juya ya bar mu a gurin tsaye ina bin motarsa da kallo.
“Kun taba yin wata magana ne da shi?”
“Eh lokacin da mahaifiyarsa ta saka aka kamaki ba, yace min wai ni waye ne a gurinki da har zan nuna masa isa, sai na ce masa zan nuna masa ko ni wanenen nan da dan lokaci”
Na yi shiru bance komai ba, hakan yana nufin shi da Abdallah sun yi sa'insa kenan, wata kila shiya saka Abdallah ya nemi na bar aikin a kamfanin dan ya nuna masa ya isa da ni. Ji nai ya saki hannuna ya juyo gabana yana kallona.
“Bari na barki ki huta, ki yi list din duk abunda kike so kin san yanzu hakkinki da na yaranki yana kaina, da safe zan zo na karba”
Ya fada sannan ya shafa fuskata, har ya juya sai kuma ya juyo.
“Ba ni line wayarki”
“Why....”
“Just”
Ban musa masa ba na ciro line ya mika masa.
“Amman akwai numbers din yan'uwa da kawaye na a ciki”
“Okay idan na dawo gobe zan zo da sabon line sai ki dauki numbers din a ciki”
Kai na gyada masa sai ya juya can kuma ya sake juyowa a karo na biyu yai min alama da na zo, sai na karasa kusa da shi kamar yadda ya bukata, saitin kunnena ya kai bakinsa ya rada min
“Muje ki min sallama”
Ko be fada kai tsaye ba na san abunda yake nufi maybe he want to kiss me or hug, ko something like that, ni kuma bana son mutane su fara saka mana ido ace mun fara yin abunda be dace ba a bainar jama'a.
“Akwai mutane fa”
“To muje zauren gidanku”
“Nan ma za a iya saka mana ido, ka bari har ka dawo”
“Ba zan bari ba....”
Ya fada yana wuce ni ya nufi cikin zauren gidan a dole na bishi a baya, ko da na shiga har ya jingina da bangon gurin yana jiran shigowata, hannunsa ya kai ya kama kwankwaso na ya rike ya hade fuskarsa da tawa.
“So this woman here is mine”
Ya fada da sigar da babu wanda zai ji sai ni, ni dai hankali yana kan kofar gida kar wani ya fito daga cikin gida ya gan mu. Bakinsa ya saka cikin nawa ya tsosa iya yadda yake jin ya samu natsuwa sannan ya sake ni, kamar an masa shocking haka ya zabura da karfi ya bankare sai kuma ya runtse ido, kamin ya bude su a hankali ya kalleni.
“Good night Sweetheart”
Ya fada yana kissing kumatuna sannan ya juya ya fita daga zauren, hakan kawai na samu kaina da son kallonsa, haka n leko a zaune ina ta kallonsa har ya karasa gurin motarsa ya bude ya shiga yai mata key ya fice.
Wata irin natsuwa da sakewar zuciyata da nishadi ne suka ziyarce, rumgumar da yai min sai na ji kamar mu kasance a haka har a bada, gaba daya jikina kamshin turarensa yake murmushi ya maye gurbin hawayen da nake, ina jin a raina kamar na yi dace duk da ban tabbatar din ba, sai a yanzu nake jin wata irin natsuwa da farincikin amincewa da nai, wata kila dazun ba kukan bakinciki nake ba, kukan farinciki nake ban gane ba, da kuma yadda abun ya zo min a bazata.
“I love you so much Lims”
Na yi murmushi ina jindadin tuna kalmar daya fada min a dazun, har yanzu bana jin ina son sa kamar yadda bana jin tsanarsa ko kasan a raina, amman am happy I'm now officially Mrs hakan ma wata martaba ce babba, na juyo na nufo cikin gida, sai da na gama sallah isha'i sannan na bude ledodin da ya kawo min, kaza ce babba har guda biyu da lemu sai kayan tea da katon burodi da kuma ku a cikin farar takarda 20k.
Washe garin ranar na tashi cikin walwala ba laifi ina ta jin nishadi a raina, bayan su Namra