Showing 15001 words to 18000 words out of 217237 words
tana bachi, tana ganin yanayi na ta san ba lafiya ba.
“Halimatu?”
Kusa da ita na zauna,sai na ji wani irin natsuwa da kauna ya shiga zuciyata irin na uwa da ƴa, ban shiga da kuka ba, kuma ban shiga dan nai musu kuka ba amman ganin mahaifiyata sai naji kamar ni ma din karamar yarinya ce a jikin uwarta a take na fara hawaye.
“Lafiya? Lafiya? Miya same ki Halimatu”
Wannan tambayar ce ta fito da Inna daga dakinta tana hamma.
“Lafiya dai?”
Wani irin abu na ji taya zan fada cewar kanen mahaifinta ya lalata? Sai da na ji na samu natsuwar ruhi da ta zuciya sannan na labarta musu komai.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda dukansu suka fada, Inna ta dafe kai, Mama kuma ta daka kirjinta ido a waje tana ta maimaita Hasbiyallahu.
“Wallahi Mama ba zan kyale wannan maganar ba, sai na kai shi kotu sai an kwatar mata hakkinta”
Na fada cikin kuka, sai Mama ta nuna ni da yatsa.
“Kul....! Karki so ma, ki kai kotu? Ki tonawa kanki asiri? So kike a yada ki a redio da tv ke da yarki a buga ku a jaridu? So kike idan yarki tai wayo ta koma ganin laifinki? So kike yarki ta rasa mijin aure? Halima karki yi wannan kuskuren Halima, karki alata rayuwar yarki da taki rayuwar”
Inna ta karba mata.
“Lallai kam duk yadda za a kwato mata hakkinta, zai zubar da mutuncinta ne kawai, wanda be san ayi ma ba yanzu ya sani, suma waenda ake yi ma wa kika taba jin an yankewa wani dogon hukunci? Balle wannan da zai iya tsayawa ya kwaci hakkinsa ya barki nan ke da yarki a cikin mummunar rayuwa, kuma ki jawa kanki da yayanki tsana a gurin dangin mahaifinsu, sannan ki kashe aurenki domin akan wannan abun kin san Aminu zai iya rabuwa da ke daman igiya daya ta rage”
Mama ta gyada kai
“Ko ma be sake ta ba, ai Mahaifiyarsa zata iya saka ya saketa tunda daman can ba sonta take ba”
Hawaye ne suke min zuba irin zubar da bazan iya misaltawa ba, gaba daya kaina na kulle duk wani kuzari na kwatarwa yata hakkinta da nake da shi sai na neme shi na rasa, lankwafar da kai nai ina kallon Mama da abokiyar zamanta Inna hawaye na min zuba na ce
“Mutuwar aurena kuke ji ba abunda akai wa yata ba?”
Inna ce ta dawo gefena ta zauna ta juyo da ni.
“Halimatu, duk wanda zai ce miki be ji zafin abunda akai wa Namra ba to makiyinki ne, sannan kuma duk wanda zai baki shawarar zama a gidan mijinki ki rike yayanki hakika masoyinki ne, Halimatu kanenki mata nawa ne a gidan nan suma neman rabuwa muke da su kai kuma sai ki ce zaki kashe aurenki ki dawo? Kuma kisan auren ma ya zama akan fyaden da akai wa yarki? Ki tonawa kanki asiri? Irin wannan maganar sasantawa ake sai a dauki matakin dan gaba, sirrinki ne wannan ki rike abunki ko yan'uwanki karki ba ri su ji, ki haka rame ki saka shi ciki ki rufe, ko a familyn mijinki karki ba ri kowa ya ji, ki yi hakuri karki ce za ki kai wannan maganar a waje, shi ma Abdallah da yaji ki yi magana da shi ki roke shi ki ce kar ya fadawa kowa kinji?”
Na gyada mata kai ina share hawayena.
“Na ji”
“Na ji”
Na sake maimaitawa ina gyada mata kai ido kuma suna ta yawo a tsakar gidan.
“Na gane”
Na fada ina cizon lisp dina, ni kadai na san abunda nake ji, ni kadai nake jin abunda yake min yawo a zuciya.
“Aminu ya san da maganar?”
“A a be sani ba”
Na amsawa Inna kamar ba ni ba.
“To a tsakaninku za ki yi wannan maganar karki nuna masa ma mun ji, kuma karki nuna masa kin kaita asibiti”
“To”
Na fada ina mikewa tsaye.
“Ina za ki je?”
Inna tace.
“Ai da kin zauna har a jima tunda yace zai kawo miki ita”
“Aa kara dai na je gida”
Na fada ina tafiya. Mama ta mike tsaye ta biyo bayana tana fadin
“Ki rike Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, kinji? Dan Allah karki fitarta da maganar nan Halimatu”
“To Mama”
Na amsa mata ba tare da na jiyo ba, tafiya na fara yi a unguwarmu hawaye na sauko min ina saurin saka hannu na share, har na isa titi na tari napep mai mutum biyu na shiga nice ta uku, mai napep na tafiya ina hawaye har muka hau babban titi, ni aka fara saukewa sai na fito na saka hannu a jaka na dauko kudin mai Napep na mika masa sannan na tura kofar gidana zan shiga sai na jita a kunne, da alama mai gadin ya rufe daga can ciki har sai da na buga sannan ya bude min na shiga yana min sannu da zuwa. Yadda na bar gidan haka na same shi daman da zan fita ban rufe ba domin na fita hankalina baya jikina. Lokacin da n shigo falon sai na zauna a saman kujera kamar wata bakuwa na saka hannuna na dama cikin na hagu na fashe da wani irin kuka, zuciyata na ayyana min na sha wani abun na mutu kawai na huta.
Hakika na ci kuma kuma kuka ya ci ni domin ya san da zamana a duniya a wannan yau, ina zaune a gurin ina aikin kuka har aka kira sallah azahar idona ya kumbura sosai har bana iya gani da shi sosai, tun ina kukan a zaune saman cushion har ta kai na fado kasa har na kwanta a gurin na mulmula na buga hannayena a kasa. Sai da na ji tsayawar mota sannan na tashi da sauri na leka ta window bata bakar motace da ban wayeta ba, sai dai hango mai kama da Abdallah ya fito cikin motar da shadda nai ruwan kwai yasa ni koma na dauki hijabina an saka na bude kofar falon na fita, ko da na fito ya doso kofar rumgume da Namra a kafadarsa.
A bakin kofa na tsaya shi kuma ya karaso kusa da ni, tun daga yanayin tafiyar da kallon na fahimci ba Abdallah ne ba, domin mutun daya yake min irin wanna kallon wato Abdulhamid domin shi komai nashi a natse yake, saboda kara tantancewa na ce.
“Abdallah....”
“Abdulhamid”
Da sunansa da ya fada yasa na kara tantance shi din ne ta hanyar kallon da nai wa bakinsa a lokacin da yake furta sunansa, domin shi haurensa na gaba ya dan kaure kadan.
“Ya fada maka?”
Ya gyada min kai.
“Naje yin wani abun ne sai yace na biyo da ita zai shiga theater”
Ya mika hannu na karbeta ina hade yawu.
“Ki yi hakuri Halimatu, ko wane bawa da irin kaddararsa, kuma ko wane gidan aure da kalar nasa kalubale, duk wanda ya fada miki aurena da dadi 100% karya yake, akwai kalubale a cikin aure da rayuwa kala kala, dan haka ki yi hakuri, an rubuto haka zai samu Namra so no matter what you did ba zaki iya tare jaddararta ba, rayuwa ko da yaushe tana cike da kalubale so dukan abunda za ki yi karki yi shi dan yau ki yi dan Goben ki, ina rokon Allah ya zama a tare da ke kuma ya baki juriyar daukar wannan kaddarar”
“Amin na gode”
Na juya ina hawaye kamar ba wacce aka tsamo daga kogin kuka na shigo ciki jikina na bani kallona yake har na shigo. A saman kujera na aje ta tana ta bachinta da alama allurar bachi yai mata domin ko motsi bata yi. Wani sabon kuka ne ya zo min tausayinta da nawa ya rufe ni.
“Al-hamdulillah Allah duk abunda kai dai-daine, idan ka ga dama sai ka akashe mu mu duka kuma daidai ne, da baka so ba, da komai be faru ba, kai ka kaddara min auren Aminu, kuma kai ka kaddarar abunda zai faru a yau, komai a cikin ikonsa da yardar ka ne Allah, ya ka zama gatana ka zama tare da ni Allah ya min mafita ka isar ka isar ma yata, Allah ka zaba min tsakanin kwato hakkin yata da igiyar aurena ya Rahamanin Rahim....”
Na karasa cikin wani irin kuka da ban san da zamansa a cikina na sai yau....
________________
Wane Halimatu zata zaba? Aurenta da Aminu wanda shine rufin asirinta da na yarta kamar yadda Mahaifiyarta ta fada?
Ko kuwa kwato hakkin yarta wacce aka lalatawa rayuwa aka maida babban mace?
#Abdallah
#Abdulhamid
#Aminu
#Halimatu
#ZawarcinHalimatu
#Gobena
#Freepage
#Twinbrother
*If you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
7️⃣
Hawayena na share na tashi na shiga dakina nai alwala na soma gabatar da sallah azahar, ina Sallah shiedan na ta kawo min wasu abubuwan da be kamata nai tunaninsu a lokacin da nake a gaban Ubangijina ba, sai dai na yi nasarar fadawa Allah bukatata kuma na kai masa kuka. A lokacin da na sallame sai addu'a ta subuce bakina saboda tunanin da ya taru yai min yawa. Ida har na hakura na bar rayuwar Namra ta tafi a haka ni tawa rayuwar zata inganta kuwa? Taya zata inganta bayan yata zata kasance cikin kunci? Kyale Baba Sadi zai canja mishi hali ne daga abun yake? No sai dai ya kara masa kwarin guiwar yin hakan saboda an kyaleshi, hakan kuma ba zai saka Aminu sauya halinsa ba, miye ma amfanin zama da mutumen da ke mu'alama da wasu matan a waje, wanda har ya zama silar lalacewar ta wa yar? Shin yin shiru zai amfanin wani abu ne? Jin bugun kofar falo ne ya dawo a ni daga duniyar tunanin da na tafi. Tashi nai sanye da hijab da nai sallah na nufi kofar falon, ina budewa na ga Abdallah tsaye rike da hannun Adnan dayan hannunsa kuma rike da leda fara irin babbar nan ta pharmacy, Aiman kuma na gefensa, sam na manta da zancen dauko su daga makaranta sai yanzu.
“Be kamata ace har yanzu kina barin kanen mijinki yana zuwa dauko yaranki daga makaranta ba, domin idan be samu mace ba mazan zai iya lalata su tun da duniyar ta canja ba maza ba mata”
Shine abunda ya fada min kai tsaye, ni kuma na kwara bude kofar falon.
“Adnan ku shigo ciki”
Da sauri suka shiga falon ni kuma na fito na tsaya bakin kofar falon na janyo kofar na rufe.
“Kin yi kuka da yawa Halima ga fuskarki nan ya nuna, kina tunanin kuka zan canja komai ne? Kina tunanin kukam zai saka Kanen mijinki nadamar abunda yai? Ko kuma mijinki zai fasa neman matan da yake ne yana gallaza miki? Haka zaki saka ranki a kunci kina ta damuwa?”
Kasa nai da kaina ina jin wasu hawayen suna kokarin cika min ido.
“Na je gida na kai miki yaran na yi tsammani kina gida, sai suka ce kin zo kin tafi, tun da na ji haka na san cewar sun karya miki kuiwa ko? Su baki shawarar rufe sirrin saboda kar wani yaji, Kanen mijinki ya ci bulus kenan? Bayan ya ci amanar dan'uwansa, rayuwar aure ba rayuwar kunci ce ba Halima, saboda kina neman lahirarki ko kuma kina son kyautata rayuwarki be kamata kullum ki yi zama da kunci kina tauye kanki ba, musulunci ma be yarda da irin wannan auren ba, yaushe rabon da ko kusantarki mijinki yai?”
Hawaye ya fara sauko min, tabbas Abdallah yana da gaskiya akan dauki wata daya biyu wani lokacin har uku kamin Aminu ya zo min da bukatarsa.
“Ba sai kin fada min ba na sani, namiji mai neman matar sosai kamar yadda Aminu yake baya iya kula matar gida, duk abunda zaki yi ba zaki burgeshi ba saboda idonsa sun bude akan wasu matan na waje kuma ya yarda sun fi ki komai, so baki da wata daraja da kima a idonsa, yana yawan fadar baya son mace mai irin siffarki halittarki bata burge shi, kuma kin tara masa yayana yana da kananan shekarunsa a lokacin da yake bukatar hutu ke kuma kika son hana shi jindadin rayuwa, shiyasa yake gallaza miki”
Dagowa nai na kalleshia fusace na ce
“Kana ta fadin karya da gaskiya akan mijinki, tsayawa a ina saurarenka ba shi yake nufin na yarda da kai ba, baka san komai akan mijina ba babu ruwanka da rayuwarsa”
“Kwarai na san komai akansa, da yawa daga abokansa ina hulda da su kuma kin sani mazinata basa da sirri, har jinjirin cikin da kike dauke da shi na sani Halima, babu wanda be san irin zaman da Aminu yake da ke ba a cikin abokansa, saboda mijinki ba shi da sirri, ban san taya akai ma kika auri Aminu ba Halima sam ba mijin daya dace ki aura ba ne”
“Baka isa ka shigo har cikin gidana ka ce zaka fada min wata maganar banza akan mijina ba, ka fice”
Cikin wani irin tsawa na nuna masa gate raina na bace, daman ya saba a duk lokacin da muka hadu da shi sai ya fada min wata maganar marar dadi akan Aminu. Murmushi yai ya tabe baki ya miko min ledar hannunsa.
“Maganin Namra ne, karki sake mata abunda zai tsoratata saboda kwakwalwarta a tsorace take a yanzu ya riga ya gama tsoratata so tsoron yana tare da ita har sai ta samu sakewa na wani lokacin kamin ta koma Normal, ki rika gasa mata da ruwan zafi. And idan kin ga dama ki dauketa ki kai ta riko gidan Kenan mijinki sai na yarda kin fi ganin kimar mijinki fiye da yarki, duk abunda kike idan saboda goben ki kike to goben ta fara lalacewa a yanzu tun da har zaki iya barin hakkin yarki akan aurenki......!”
Yana fada min haka ya juya a fusace ya sauka daga dan gudun stairs din dake gurin ya nufi motarsa ya shiga yai ribas da karfi alamun da ke nuna ransa ya bace sosai kenan. Bude kofar falon nai na shigo ya maida kofar na rufe na jingina jikin kofar ina fashewa da kuka mai karfi. Na rasa abunda zan yi maganar mahaifiyata zan bi ko kuwa abunda nake ganin yafi?
“Momy mi kike kuka?”
Adnan ya tambaya daga shi har Aiman kallona suke.
“Ba kuka na ke ba”
“Gashi nan hawaye yana miki zuba”
“Kaina ke ciwo”
Na fada ina kirkiro murmushi tare da share hawayen. Hannu na mika musu sai duka suka zo na zaunar da su kusa da ni na shafa kansu sannan na daga kaina na kalli Namra da ke bachi saman cushion. Yayana na daya daga cikin babban kyautar da Allah kan yi ma bawa, wasu nema suke yi saboda Allah be basu ba, da ana siya da kudi da sun siya ko nawa ne, wasu kuma Allah ya basu mazan be basu matan ba, suna ta son mata ba su samu ba, wasu kuma matan Allah ya basu be basu maza ba, amman ni Allah ya hada min duka biyu ya bani maza biyu mata biyu a cikin shekara 11, sai dai ya bani su a inda ni kadai nake masa godiya da kyautar da ya ba ni, ni kadai na ke kallonsu na jidadi, mahaifinsu kan ganin yake na tara masa tsufa, har yana guduna saboda su saboda haihuwarsu ta canja min halitta na tashi daga buduwar zuwa mace mai yaya hudu da ciki na biyar, cikin da yake cewar na zubar baya bukatarsa.
“Allah ya raya ku ya sakawa rayuwarka albarka ya tsare min ku”
Na fada ina kara shafa kansu, sannan na mike tsaye na nufi kitchen na kunna gas na hada musu tea na gama musu da sauran biredin safe da yai saura na mika musu, ni kuma na shiga dora girkin rana duk kuwa da ina jin cewar ba zan iya ci ba amman dole na dora saboda yarana. Komai saboda su ne, zaman da nake da Aminu saboda su ne, idan na fita na barsu ban san wace irin rayuwa za su shiga ba, ban san wace macen ce zata raine su ba, fatar shiriyar da nake masa ko bana aurensa ina masa ita saboda na riga na haihu da shi. Ina cikin wanki shimkafa na ji yara suna murna.
“Oyoyo Anty Hafiza”
Kanwata ce wacce muke uba daya da ita, sai dai Allah ya hada jininmu kamar yan daki daya, bata boye min komai ni ma bana boye mata damuwata.
“Yar aljanna... Da aka fada miki kuma sai kika ji kika dawo gida har kina girki, Allah mai ikon, da ya tashi sai yai mu uba daya amman hali kowa da na shi”
Juyowa nai na kalleta da idona da suke kumbure, sai na ga hawaye na mata zuba mayafinta ma a hannu yake tare da jakarta.
“Da ace ko wace mace zatai irin zaman auren da kike da mijinki, da maza sun huta da korafin matansu, kuma da ko wane yaro mai uwa da uba a raye be girma ya ga uwayensa a rabe ba, kina da hakuri Halima fiye da kima, sai dai hakurin idan yai yawa yana cutarwa, abun ya wuce kanki a yanzu rayuwar yaranki ake neman lalatawa, be kamata ki yi hakuri a nan gurin ba”
Sai da na hade yawun bakina sannan na ce.
“Inna ta fada miki abunda ya faru?”
Sai ta matso kusa da ni tana kallon irin kallon nan na tsantsar tausayi.
“Mama ce ta fada min, na rasa gane dalilin shirun da za ki yi, ban san mi yake damun iyayenmu ba, dukansu tsoron mutuwar aurenki suke ji, mu kuma da muke gida suna matsa mana akan lallai sai mun yi auren, suna matsa mana akan auren ko wane irin miji saboda mu bar gabansu mu kaucewa maganar mutane, ku kuma da kuke da aure suna son ku yi da zama auren ko da babu dadi saboda gudun magana, sun kasa gane aure rai ne da shi, idan lokacin mutuwarsa yai dole sai ya mutu, idan kuma lokacin yinsa yai sai anyi ammn sai su dauki damuwar duniya su sakawa kansu, yanzu so suke ki zauna da mutumen da be san darajarki ba kuma ki kyale kanensa ya ci bulus kenan? Idan ma bakinciki kashe ki zai yi sai dai ya kashe ki? No ban zan goyi bayan wannan abun ba, ba za ki kyale