Showing 93001 words to 96000 words out of 217237 words
daga kan gadon ya ce.
“Akwai drip hannunki ki zauna sai ya kare”
“A a ba zan iya ba ina son na ganta”
“Ba mu san inda ya kaita ba”
Ya amsa min fuskarsa ba yabo ba fallasa. Hakan yasa na koma na kwanta sai kuma na ji yana maganar hoto.
“Idan drip din ya kare Mama za ta kaita ayi mata hoto”
“Ba ni da lafiya ne?”
Na tambaya sai yai saurin ba ni amsa.
“Lafiyarki kalau”
Bayan ya amsa min ya cigaba da kallona kamar mai tunani.
“Ina son ganin yarinyar nan ina son ganinta ta mutu bata mutu ba ban sani ba i need to see her!”
Na fada a tsawace kamar ba a hayyacina ba.
“Idan ka san inda take a kaita ta ganta”
“Ban sani ba amman zan bincika”
Yana fadar hakan ya juya ya fice daga dakin sai sauran likotocin suka bi bayansa. Ni kuma na lumshe idona ban bude ba har sai da na ji motsin shigowar mutum, Hafiza ce ta shigo hankalinta a tashe tana sharar kwalla.
“Sannu Halimatu”
Haka take kirana yana da wahala ta ce min Anty indai ba mutane sai arzikin ke saman kanta ba.
“Yauwa, yarinyar ta rayu”
“Ance tana da rai, mahaifinta ya kaita wata asibitin aka ce”
Ban sake ce mata komai ba, har sai da Abdallah ya shigo da kansa ya karaso ya cire min drip sannan ya ciro wayarsa ya kira wani likita da ban san wanene ba ya ce.
“Zan dauketa na kaita ta ga yarinyar yanzu idan mun dawo i will call you”
Daga haka ya maida wayar aljihu ni kuma na sauko daga saman gadon na biyo bayansa, a harabar kofar shiga Ward din inda mutane suke shinfida tabarma suna zaunawa na hango Inna sai ta taso ta tare ni.
“Halimatu kin taso”
“eh zan kaita ta dubo Namra ne idan mun dawo sai a je da ita gurin hoton”
Abdallah ne ya bata amsa a madadina sannan tai mana Allah ya tsare ta bimu da kallo, yana gaba ina biye har gurin motarsa, da kaina na saka hannu na bude motar na shiga na zauna daga lokacin kuma ban sake sanin inda nake ba. Sai can na farka na ga yana kallona.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Shine abunda ya furta, kallonsa nai kamin na kalli titin sai a lokacin na lura da motarsa fake take a gefen titi kuma ba a cikin asibitin muke ba, Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya tashi motar muka hau titi, SJT hospital muka shiga, babbar asibiti mai zaman kanta a zamfara, asibitin masu kudi domin ko katin ganin likita kawai ya isa siyen wani maganin a yadda nake jin ana fada domin ban taba zuwa ba.
Agurin da aka tanada domin faka motoci ya faka motarsa sannan ya bude ya fita, ni ma na bude na fita sai wani irin sanyi baibaye ni sanyi ba na wasa ba, a take hakorana suka fara haduwa da juna.
“Koma cikin motar ki zauna”
Ya fada min sannan ya ciro wayarsa ya kira Hafiza yai mata kwatancen inda muke, tun da ya soma wayar na ke kallonsa har ya gama ya cigaba da latsa wayarsa, sak Abdulhamid nake gani a sura da hallitarsu sai dai shi ya dan fi Abdulhamid kwauri kadan, a hallaya kuma sun banbanta, tunawa da Abdulhamid sai ya haifar min da wata kalar damuwa a cikin raina.
“Abdallah”
Ni dai na san na kira sunansa har ya dago ya kalleni ban kuma san dalilin kiran nasa da nai ba, bayan ga wannan ban sake sani ko jin abunda ya fito daga bakina ba, kamar an min shocking dai na ji na dawo normal, amman a kasa nake zaune fuskarta har da hawaye da ban san yadda akai suka zubo ba, saurin tashi nai zaune na saka hannu na share hawayena a lokacin da na kalli Abdallah sai na ga idonsa cike da kwalla yana ta min kallon tausayi.
“Miyasa nai hawaye? Mi yake faruwa da ni...?”
Na tambaya ina kokarin fashewa da kuka, sai ya busar da iskar bakinsa
“Ba komai”
Da kansa ya kai hannunsa ya bude min motar.
“Shiga ciki ki zauna na ce”
“Ina son ganin yarinyar”
“Idan Hafiza ta zo zamu shiga ciki ki ganta”
Zaunawa nai cikin motar sai a lokacin na tuna da yata.
“Ko ina Namra take? Ko har da ita ta fada rijiyar? Kamar bata fada ba ko?”
Na tambayi kamar ya san amsar.
“Tana nan lafiya kalau”
Ban sake cewa komai ba, har Hafiza ta isa sannan na fito daga motar daman kafafuwa na waje suke, shi kuma ya rufe motar yai gaba muka bishi, mun yar tafiya mai dan ni sa sai dai ba sosai ba har muka isa bakin wasu dakuna, daki na hudu ya tura kofar ta bude sai ya tsaya be shiga ba yai min alama da na wuce. Ni na fara shiga sannan Hafiza sai kuma shi.
Baby Namra ce kwance saman gado tana bachi jini na ta shiga a jikinta. An saka mata wani abu a wuya an daure kafarta da hannu a gefen idonta ma bandeji ne.
Mutum hudu muka tarar a dakin ciki har da mahaifinta, kamar wanda ya ga bakin maciji haka yake kallona fuskarsa babu annuri, ban taba hada ido da wani naji firgita kamar yadda na ji a lokacin da na kalli Abban Baby Namra ba, a take na nemi natsuwata da karfin halina na rasa, na rasa sai fargaba da razana suka lullube ni, kamar wata karamar yarinya haka na zama na rasa sukuni har sai da na koma bayan Abdallah na tsaya.
“Kina da wani irin karfin hali, how dare you”
Babu wanda yace uffan daga mutane da suke dakin har Abdallah da Hafiza.
“And let me tell you Wallahi idan yata ta mutu i will make your life miserable, you will die in jail kina ji kina gani zan tarwatsa rayuwarki, you will pay for this, ba kin zabi kashe min ya ba?”
The word jail ta saka ni jin wani iri, is like kamar ban taba jin kalmar ba, kuma kamar ance min gunduwa gunduwa za ayi da ni. Ba tsoron gidan yari nake ko police ba amman ban san abunda ya saka ni tsoro ba har jikina ya fara rawa kamar wata bakuwar kalma haka na rika jinta a kaina, a take garin ya fara sauya min zuwa wani yanayin dabam, can na tsinkayo Abdallah nayi masa magana.
“Taya mace da ta haifa ta san zafin haihuwa zata dauki yar wani ta jefa rijiya? Ya kake magana kamar ba namiji ba”
Wani banzan kallon yai masa irin na sai a yanzu na lura da kai din nan.
“And who are you? Her husband?”
“No I'm her brother”
“Just?”
Ya tambaya da irin sigar rainin wayo.
“Just ne?”
Abdallah ya tambaya a fusace.
“Who do you fucking think you're? After all the slap da maganar da ka fada mata yanzu and you want to deal with me? Daga ganinka ba ka yarda da kaddara ba”
Sai ya daga wa Abdallah gira.
“Yes ban santa ba, saboda ban hada hanya da ita ba, akan yata?..... Hummmm”
Wata budurwa ce ta taso ma Abdallah budurwar da na tana gani a gidansu lokacin da naje.
“Excuse me man, yar mu aka taba kasan darajar ranta?”
“Hey young lady control yourself, and ban sani ba kuma ba na son na sani”
Juyowa yai ya kalleni.
“Muje Hafiza riko hannu”
Yana fadar hakan ya fice, a maimakon ya ta kama hannun nawa kamar yadda ya fada sai ta tsaya yi musu bayani.
“Ku fahimce mu, Halima ba zata kama yar wani ta jefa a rijiya ba, ko da kau bata santa ba balle ta santa, yanzu haka ba a hayyacinta take ba amman ta damu sai an kawo ta ta ganta, tun daga lokacin da ka mareta bata sake zama mutum kamar kowa ba, daga ni har ita ba mu san yadda akai yarka ta fada rijiya ba.... ”
“Aljanune da ita kenan? Shiyasa ta dauki Baby ta jefa rijiya, daman ai ba tai kama da masu hankali ba, ita aljannu take takama da su ni a kaina rauhanai ne, na fita hauka”
“Ba haka nake nufi ba...”
“Idan baki min shiru ab har da ke zan daure fita ki ba ni guri”
Ita yake ma masifar ni ce da jin tsoro sai hawaye nake kamar domin hawayen kawai aka hallaci ni. Hannu ta rika muka fice daga dakin ita hawaye ni hawaye har muka isa gurin motar Abdallah. Gidan baya muka zauna ni da ita, kamar uwa da ya haka kanwata ta rumgume ni a jikinta sai na fashe da kuka mai tsanani.
“Gida nake so dan Allah ka kai ji gida... ”
Na furta cikin kuka, shi dai be ce min uffan ba har muka bar asibitin.
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣1️⃣
ABDALLAH POV.
Tukin motar kawai yake zuciyarsa na sosuwa da kukan da Halimatu take yi, on the other part kuma maganar da Ahmad yai ta tsaya masa a rai. A iya tunaninsa duk mai kokarin cin mutunci Halima yana yi ne saboda yana ganin bata da mai tsaya mata kuma ana ganinta a mace mai rauni.
“Wata kaddarar, ta kan zabi wasu mutanen ta tare musu ko wane irin fada, ta tsaya musu ta hana ni ganin abun ki ko damuwa. Wata kaddarar kuma jefa wasu take a damuwa da bakinciki ta saka har duniya ta juya musu baya, mi yake damuna ne? Miyasa komai ni ce komai ni ce? Na gagara samun farinciki ko dan kankane dan kannen kamar haka...”
Ta nunawa Hafiza yatsanta tana hawaye.
“Komai ni ce, komai ni ni din dai Halimatu na fi kowa shiga cikin matsala, mutane gasu nan ina ganinsu suna farinciki amman ban da, kin gansu?”
Hafiza ta kasa ce mata komai sai kuka take yana rike mata hannu.
“Ga su nan fa ina kallo ke ba ki gansu ba?”
Ta fada tana nuna gilashin motar, da gaske mutane take gani kwakwalwarta na kawo mata abubuwa da yawa, ciki har da rayuwarda tai a baya duk abunda ya zo daga bakinta fada take, abubuwan da take fada ba komai ba ne sai damuwarta. Kuka take tai dariya a lokaci daya kamar wata tabbabiya.
Ta kalli Hafiza dake mata kallon tausayi tana hawaye.
“Wacece ke? Na baki labarina? Ni wata mace ce mai haduwa da abubuwa kala kala”
Sai kuma tai shiru ta sake kallon Hafiza ta kalli kanta.
“Wacece ni?”
Abdallah na jin hakan ya busar da iskar bakinsa ya faka motarsa gefen titi ya fita be dade ba sai gashi ya dawo rike da gorar ruwa ya bude motar ta gafen da Halima take ya cire murfin gorar ya kai mata ruwan a baki, a Hankali yake bata ruwan tana sha sannan ya cire gorar daga bakinta ya kai bakinsa ya kumda ruwan a bakinsa ya fesa mata a fuska, runtse ido tai na yan dakiku sannan ta bude kyakkawan idanuwanta sukai arba da na fuskar Abdallah.
“A ina muke miya faru?”
“Babu abunda ya faru”
Mikewa yai tsaye ya bayan ya bata amsa ya rufe motar ya zagaya ya shiga side dinsa ya tashi motar.
“Miya faru miyasa na jike ina zamu je?”
“Asibiti”
“Ka kai ni gida”
Ta fada kai tsaye.
“Kina da bukatar ganin likita”
“Bana bukata Abdallah bana bukatar kowa ya rabe ni a yanzu balle har ni na rabi wasu, duk wanda ya rabe ni sai wani abu ya faru da shi....”
Bata gama fadar abunda take fada ba ya daka mata tsawa.
“Ya isa haka kike sakawa kanki tunani kala kala har abun yana taba kwakwalwarki, I'm sure idan level din gushewar hankalinki ya wuce iya nan ko yayanki ba za su zauna da ke ba....”
Ta dago kanta ta kalli Abdallah ta madubin gaban mota idonta cike da kwalla.
“Ba ni da hankali kenan? Shiyasa na ke jin kamar ina bachi kamar na suma, ashe gushewar hankali ne? Kenan haukace ta kama ni?”
Ta lumshe ido ta a hawayen da Abdallah yake jin zubarsu har cikin zuciyarsa, har yaji ina ma be fada komai ba ina ma furta komai ba!
Har ya kai ta kofar gidan ta bude mota ta fita ta shiga gida be daina kallonta ba, sai ta shige gida sannan Hafiza ta bude motar ta fita sai ya kirata.
“Hafiza dan Allah a kula da ita, bana son nai mata cilas a zuwa asibitin ne yanzu, amman zuwa gobe zan turo direba ya maida ita kin ga ai ba su bata sallama ba kuma tana bukatar kulawar likitoci, and karki barta ita kadai pls shi ke kawo yawan tunani ku rika yi mata abunda zai sauke mata hankali”
“In-Sha-Allah, mun gode Ya Abdallah”
Be ce mata komai ba yai ribas ya dauki hanyar gidan Hajiyarsa zuciyarsa cike da tunani kala kala. Sai da ya faka motarsa harabar gidan maganar Halimatu ta fado masa a rai. Tabbas sukan kaddarar kyakkyawa ta musu rumfa ta tare musu ko wane fada, ta musu gata, bayan kuma ba zabin su ne ba hukunci na Allah. Idan auna yadda rayuwa ta shimfida musu kyakkyawar rayuwa da kuma rayuwar Halima sai ya ji imani da tsoron Allah ya kara kama shi, lallai ba yin kansa ba ne, domin yana da tabbaci da bawa ne yake zabawa kansa irin rayuwar da yake so da Halimatu bata zabi rayuwar da take a ciki ba a yanzu. A duk takunsa sunan Halimatu ke yawo a kansa, ko ina zai motsa tausayi ya mamaye shi, ya kasa ganin laifinta ya kasa samun hanyar rabuwa da ita a kullum kaddara kara kusanto masa da ita take.
Ko da ya shiga falon idonsa ya canja kala saboda damuwa. He got lucky Hajiya ce kadai a falon tana kallon wayarta. Sai da ya tsaya ya cire takalmin kafarsa sannan yai sallama ya shiga cikin falon, a kujerar da ke fuskantar ta Hajiya ya zauna yana gaisheta. Ta amsa masa tana aje wayar a gafenta domin ta hango damuwa a fuskar danta kamar yadda ko wace uwa mai kula take gane idan danta yana cikin bacin walwala ko kishiyar hakan.
“Husaini lafiyar ka yau kuwa?”
Dagowa yai ya kalleta a hankali.
“Ban san yadda za ki ji idan na tambaye ki ba, ban san ya zaki dauki tambayar ba, amman Hajiya kin taba tambayar kanki ko ki yi tunani miyasa Allah yai mu masu rufin asiri kamar haka?”
Sakin baki tai tana kallonsa kamin ta amsa.
“Ah Ah daman can Allah ya kaddara mu din masu arziki ne”
Ya gyada kai.
“Haka ne da yai mana arzikin kuma sai ya hada mana da farinciki, wasu kuma ya ba su arzikin ya hana su farinciki, wasu kuma ya ba su farincikin ya hana su arzikin, wasu kuma ya hana su arzikin ya hana su farinciki yadda ya so haka yake haka yake kasancewa, duk a cikin ikonsa ne”
“Wai miya faru ne, ban gane wannan maganar ba?”
“Halima Hajiya”
Yana fadar sunanta sai yai shiru kamar ba zai cigaba ba, Hajiya kuma ta gyada kai.
“Zancen kenan Halimatu Halimatu, ka kasa cire matar nan a ranka”
“Hajiya ta ya zan cire abunda ba ni na sakawa kaina shi ba? Da ina da iko da dama da ban bar zuciyata ta kamu da son Halimatu ba tun farko”
“Dan Allah na hada ka da girman Allah ka bar yarinyar nan, ka daina shiga zabgarta ka manta da ita a rayuwarka”
“Idan umarni ne zan bi, idan kuma shawara to zan amsa miki da cewar Wallahi ba zan iya ba Hajiya, Soyayyar Halimatu a zuciyata kaddara ce, Hajiya na san Halimatu tun kamin tai aure, amman Allah be dora min kaunarta sai da tai aure ta haifi yara biyu, da igiyar aurenta na kamu da sonta Hajiya, shim ba ki yi mamaki ba? A yanzu na tabbatar ba son ne kawai a kaddarar da ke tsakanina da ita ba, har da taimakon rayuwarta da tsaya mata a wasu abubuwa, kamar yadda Allah yake bawa wani bawa abinci a karkashin wani bawa, ko yai maka kyauta da hannun wani bawan”
Taso yai ya baro kujerarsa ya zauna kasa yana kallon mahaifiyarsa da duba irin na yaro mai neman dauki a gurin mahaifiyarsa.
“Dan Allah karki hana ni yi mata ko wane irin taimako Hajiya, yarinyar tana cikin damuwa tana bukatar mutane a kusa da ita”
“Halima ba yarinya ba ce, ka daina mata kallon yarinya, duk mace da zata haifi yara hudu ta san me take”
Hajiya ta fada tana kallon wani gurin fuskarta a hade.
“Yarinya ce Hajiya haihuwar da taima ta sauri ce, har yanzu Halimatu bata haura 26 ba, tana da rauni da yasa Hajiya, damuwa ta mata yawa yanzu har rasa tunaninta take, damuwarta kawai take iya karantowa idan tai losing memory ta”
“Ba damuwa bace matsalar Hassan ya fada ai, tana shaye-shaye kuma duk mai shaye-shaye dole ya hadu da irin wannan matsalar gasu nan muna gani sai haukacewa suke, ni ina mamakin wace irin damuwa ce da ba za abar wa Allah ba, damuwar me ma? Idan bayan cin amanar da tai Hassan ya sake ta... ”
Bata karasa Abdallah ya tafi numfashinta.
“Hajiya da gaske kin yarda Halimatu ta aikata abunda Abdulhamid yake zargi? Na rasa gane dalilin tsanar Halima da kike a yanzu, mace da za tai aure ba ta dace ba, ayi ma yarta fyade mijinta ya saketa saboda haka, ta dawo ta bar yayanta da aikinta ta auri d'anki da bashi da lafiya wata kaddarar ta fada mata a keta mata haddi da aurenta, kuma d'anki yai mata sakamako da saki a lokacin da take bukatarsa ki kasa ganin tausayinta? Wallahi na tabbatar da Abbah yana da da Abdulhamid be isa ya saki Halimatu ba, domin yana yawan fada yayansa ba su isasu taba masa yan'uwa ba, yan'uwan ma Baba Dahiru mutunen da be a shi da amini irinsa, duk inda Abbah ya saka kafa kafarsa tana nan, ina tuna lokacin da Abbah yake mana wasiya da son zumunci da taimakon masara shi, musamman Baba Dahiru, babu irin neman arzikin da ba su yi tare da Abbah ba, amman shi Allah be bashi ba, daga karshe ya koma ciwon kafafuwa ya tare a gida, sannan Allah be ba shi yaya maza ba sai a lokacin da tsufa ya kama shi balle su taimake shi, matan kuma babu wata mai tsiyayar sana'ar da zata iya taimaka masa sai Halimatu da take aiki kamin ta rasa aikin nata, yanzu macen da ta taso a irin wannan rayuwar bata baki tausayi ba?”
Tsawa Hajiya