Showing 6001 words to 9000 words out of 217237 words

Chapter 3 - GOBE NA Compelet Book by Khadijah Candy.txt

24 Sep 2025

162

illa? Wallahi na gaji Haraja na gaji”

“Karki gaji da bautar Allah, ki dauki aure a matsayin idaba kuma ibadar da ta fi ko wace wahala, dan'adam be tana yin hakuri ya kasa cin ribar hakurin ba, idan rashin kyautawa Aminu baya kyauta miki amman ki yi hakuri wata rana za ki ji dadi”

“Yaushe zan jidadin? Tun da na haifi Adnan nake fuskantar wulakanci daga gurin Aminu har yau, haihuwa ta hudu kawai yake min wannan abun ime kike tunani a gaba? Ya GOBE NA zata kasance? Ina jin kamar babu wata matar auren da zata iya hakurin zaman auren da na ke da Aminu, shi ya min yan'uwansa su min ya zan ji?”

Dafani tai tana min magana a hankali

“Suna nan da yawa wadanda suka fi ki hakuri Halimatu, wasu ko abincin basa samu amman haka suke hakuri su zauna, ke ko har yana aje miki abinci ko da bashi da dadi ya dai baki lokacinsa ne kawai baya bashi da wasu hakokin, shin idan ba ki yi hakuri ba Halima so kike na ce ki kashe aurenki ki koma gidanku da zama cikin kannenki? Ya matan gidan ku a yanzu taskwas ne so kike a fara kirgawa da ke a zaurawan unguwarku? Ki tashi hankalin iyayenki da na yayanki? Kina da tabbacin shi wani mijin da zaki aura baya nema mata ko kuma zai baki lokacinsa? Ki bar yayanki su tashi a hannun wata wacce ba uwarsu ba? Adnan shekararsa goma sha daya kuma shine babba shi din ma kina da tabbacin zai iya yi ma kansa wata lalurar balle kuma sauran?”

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u.
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u.
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u.”

Shine abunda nake ta furtawa na dafe kaina.

“Ki yi taka tsantsan da aurenki Halima saki daya ya rage a tsakaninku, wani abun ko dan yaranki ai kya yi hakuri ki zauna da mijinki a haka, kuma ki gode Allah da har mijinki yana amfani da Condom din, wasu mazan kamar tumaki suke babu ruwansu da kariyar kai, kuma wani lokacin mu kan mu mata muna da matsala, Halima ko yan gyare gyaren nan ba ki yi su kuma maza basa son haka, mace sai da gyra ko da ko baki haihuwa ba balle kin yi haihuwa har hudu”

“Namijin da ba ya maka kallon sha'awa Hajara wani gyara zan tsaya yi akansa? Idan ma nace zan yi gyara zan bata kudina da lokaci na ne a banza”

Na fada ina share hawayena.

“Ba haka ba ne, ba jira za ki yi har sai shi ya kawo kansa gareki ba, ke ma zaki iya yin wasu abubuwan na wayewa da janyo hankalin mijinki izuwa gareki, su ma matan waje ai ai janyo hankalin mazanjenmu suke har su kao garesu”

Kallonta nai ina sauke ajiyar zuciya.

“Hajara yace na daina burge shi wai shi baya son mata masu kiba, kuma shi yanzu farar mace yake so ni kuma ba fara ce fes ba, kuma ina da ji ba siririya ba ce ni, bana ganin ina da wani sauran digon kyau da zan iya jan hankalin Aminu da shi a yanzu”

“Bayan jan hankali, zamantakewar aure tana bukatar tattauna da fahimtar juna, kin rigani aure Halima amman kamar na riga ki karanta halin maza, ki zauna da mijin ki bashi hakurin abunda ya faru dazun ki nuna masa ke ce mai laifi ko da kuwa shi ne da laifi kuma ki fada masa zaki kiyaye, abu na biyu ki lura da abunda zaki iya canjawa sai ki yi kokarin yi, yar kwaliyar nan t tarbon miji ki rikayi mana haba Halima sai kace ba wayayya ba?”

“Namijin da baya dawowa sai 12 ko 1 na dare shi zan yi ma kwaliya? Kuma ya riga ya furta cewar bana burgeshi a yanzu duk wani abun da zan yi aikin banza ne Hajara”

“Ki gwada dai, akwai wasu kayan mata masu kyau anjima za a kawo min zan aika miki ki gwada amfani da su, ki maida komai ba komai ba Halima dan Allah ki yi hakuri ki zauna ko dan yayanki”

“Da ma kin bar kayanki, rabon da Abban Namra yai mu'amala da ni tun daga lokacin daya fahimci ina da ciki, daman can ba bukatana yake ba balle kuma yanzu”

“Ba daga nan take ba, ke dai ki yarda da ni ki gwada dan Allah, wanna kam ba mota ba ko jirgi kika ce kina so sai ya siya miki”

Kai na gyada mata ina tabe baki gare da sake share hawayen da suke min zuba, jin motar mijinta yasa na mikewa tsaye, kamin mijinta ya shigo falon nai mata sallama na fita da sauri domin ba kasafai na ke son yana ganina a gidan ba, ba dan komai ba sai dan tsaron mutuncin aurena.
Daga gidansu Hajara kai tsaye gurin aikinmu na nufi, sai dai ban shiga Office ba sai da na biya ta gurin masu printing na cikin company nai printing documents din sannan na shiga cikin office din.
Na shiga a lokacin da wasu sun dade da shigowa ma'aikatar wasu kuma yanzu suke shigowa a yayinda wasu kuma sai anjima za su shigo kowa da yanayin aikinsa da kuma lokacin shigowarsa. A inda muke zaune mu uku ne a Office din daga ni sai wasu abokan aikina biyu duka maza, daga ni sai Kabeer sai kuma Emmanuel wanda yake ba bahaushe ba. As usual idan na shiga ina gaishe da duk wanda na tarar a office din, idan kuma su suka tarar da ni suna miko min gaisuwa cikin mutunci da girmamawa.
Yau kam Kabeer kawai na tarar na office din hakan na nufi ya riga Emmanuel shigowa kenan.

“Good morning Kabeer”

“Morning Halimatu”

Na mika masa gaisuwar a lokacin da nake kokarin zaunawa, shi kuma ya amsa min yana baro bangarensa zuwa inda nake zaune.

“Kamar kina cikin damuwa yau kin karya kuwa?”

Haka yake min a lokacin dana shigo office din yana kokarin kula da ni kamar matarsa duk kuwa da na san kular bata Allah da Annabi ce ba, na san yana da wata manufar akaina
Hannu ya kai zai taba jikina sai nai saurin buge masa hannun na mike tsaye cikin bacin rai na ce.

“Miye haka Kabeer taba ni za kai? Ka manta da ina da aure ko me? Wai miyasa kake min wasu abubuwan kamar baka cikin hayyacinka ne?”

“Halima kenan, ni da ke mun zama daya a nan fa? Miye laifin dan na na taba jikinki?”

“Idan a gurinka ba laifi ba ne ni a gurina laifi ne, ina da aure har da yara hudu abunda ban aijata shi da budurcina ba ba zan aikata shi da aurena ba”

Ina fadar hakan na dauki documents din na wuce zuwa office din ogan mu, na yi zaton yana cikin musamman da na ga ya kirani jiya yace na shigo da takardun nan a zaton ko da saffafe zai duba su amman sai gashi ban same shi a office din ba. Hakan yasa na dawo nawa office din na zauna na soma aikina, gaba dayan ranar Oga Dahiru be shigo ba, haka ma wunin ranar Kabeer be ga wata sakewa a tare da ni kamar yadda ya saba gani ba. Har muka tashi daga aikin ban sake ce masa komai ba shi ma kuma be yi kokarin yi min magana ba.
Kamar yadda na saba bayan na taso daga aiki na wuce gidansu Baban Sadi wato kenen mahaifinsu domin dauko yarana daman yana daukarsu tare da yaransa ya kai su gidansa idan an tashi scul har sai idan na taso aiki na biya na dauko su a Napep mu dawo. A bakin kofar falon muka gaisa da matarsa sannan na kirasu suka fito banda Namra.

“Ina Namra?”

“Tana can part dinsa ai kin san indai yana nan to tana can part dinsa, ko fita zai yi da ita yake fita Allah ya hada jininsu”

Cewar Safiya matarsa. Ni kuma nai murmushi ba tare da tunanin komai ba na kalli Aiman na ce yaje ya kirata na saka Amal da Adnan a gaba muka nufi gate da zimmar Namra da Aiman su cin mana. Kamin mu fice daga gate din gidan sai gasu sun ci mana Namra na ta sharar kwalla idonta ya yi ja sosai.

“Ke lafiya?”

“Cikina ke ciwo”

“Oh wannan ciwon cikin ya matsa miki, bari yanzu idan muka muka je gida su Adnan suka wuce Islamiya sai na kai ki asibiti”

“To Momy”

Ta amsa min cikin kuka har sai da ta bani tausayi. Napep na tara na saka yarana sannan na shiga muka nufo gida. Indomie na fara dafa musu suka ci sukai shirin islamiya sannan na dora tuwo na shiga nai wanka nai ma Namra na shirya ta, sannan na fita na kira Kausar wata kanwar makociyata wacce budurwa ce daman na kan kirata ta rika min wasu abubuwa. Ita na barwa girkin sannan na ja Namra muka nufi Asibitin Yarima ganin likitan yara na maraice.
Ba mu tararda jira kamar safe ba, daman da maraici ba a cika taruwa ba, a lokacin da muka shiga dakin likita ya tambaye ta komai ta fada masa yadda take jin cikin nata yana mata ciwo, sannan na rubuta mana hoto da awon fitsari sannan na rubuta mata magani. Sai da na kaita akai mata hoton fitsarin kuma suka ce a kawo na safe wanda zata fara yi kamin ta ci komai. Maganin ne kawai ban siya mata ba muka dawo. A saman kujera ta kwanta ni kuma na shiga kitchen na dora miya domin ko da muka dawo Kausar ta toke mana tuwon.

Daf da magariba Adnan suka dawo daga makarantar islamiya, daker na tattara su sukai sallah sannan na kwashe miyar na zuba musu nasu na sako nawa ni da Amal muka ci Namra kan ko ruwa kasa sha tai, hakan yasa na dauki wayata na kira shi. Sai da ta dade tana ringing sannan na daga.

“Ya akai?”

Shine abunda ya far tambaya, ni kuma na mika masa gaisuwa

“Ina wuni?”

“Lafiya Kalau”

“Namra ce bata da lafiya tun jiya cikina na ciwo shine na kaita asibiti dazun suka bamu awon fitsari da hoto kuma suka rubuto mata magani”

“Wa kika tambaya kamin ki fita? Da izinin wa kika fita?”

Sai na kasa amsa masa domin na san bana da gaskiya a nan, be kamata na fita ba tare da na tambaye shi ba, sai dai na san idan na tsaya tambayarsa ba lallai ne yace na tafi ba domin duk wani abu daya fito daga bangarena baya daukar sa da muhimmancin wata kila ma zai ce kashin kudin ne zan ja masa.

“Ka yi hakuri dan Allah”

Be amsa min ba yaja tsaki ya kashe wayar. Ji kuma na sauke ina jin raina ba dadi a take abincin ya fita raina daman da safe ban iya karyawa ba.

“Adnan je ka kira min Kausar ta siyo ma Namra magani a chemist”

Da sauri ya tashi daman dan son yawo ne shi da Amal a take ta rufa masa baya har da gudunta. I decided na aiki Kausar din na bata kudin da ke hannu ta siyo mata maganin kamin shi ya gama fushinsa ya siyo mata. Adnan na fita sai ga Afrah ta shigo wato yar Hajara da bakar leda a hannuna.

“Wai ga shi Momy tace a kawo miki”

Karba kawai nai na aje ba dan ina tunanin amfani da shi ba, domin na saba amfani da irin abubuwan nan ban taba ganin ribarsu ba, sai dai na ji wasu matan suna labarin abu kaza yana da kyau ko yana yi, ni dai nawa mijin bayan nuna min idan ma na sh wata kila kuma ni tawa hallintar bara karbar irin waennan abubuwan. Afrah na fita sai aka sake turo kofar falon aka shigo wannan karon Sa'adatu ce kawata.

“A a maraba da manya”

Na fada ina dariya.

“Ah ai kune manya kuna cikin irin wannan gida haka ga uwar daula ai kukan ku kukai dacen auren mu mata kawai muka rako duniya”

“Uhmm”

Kawai na iya fada domin yawancin mutanen da suke zuwa gidana suka ganin kyakkyawan falona da gidan sai su tai min kallon kamar na fi kowa dacen aure.

“Bari dai na kawo miki ruwa”

Na fada ina nufar kitchen, ita kuma ta hau tambayar ina Amal da sauran yaran.




__________________

Anya da gaske akwai mata irin Halimatu kuwa? 🤔
7/20/21, 8:28 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy


4️⃣

“Sa'adatu kenan, kwana biyu ma kin daina dan lekowa, ko ya fara hana yawo ne?”

Na fada bayan na mika mata ruwan sai ta wara ido.

“Tab ya isa? Ai a hannuna yake sai yadda na ga dama na juya shi”

“Too kaji manya a bamu sirrin”

“Sirrin mai wuya ne Halima,amman Wallahi da ni nake da kyau ki da irin wannna jikin na ki sai na more”

Kallon rashin fahimta nai mata.

“Kamar ya ba?”

“Ka more rayuwa mana, kai ta sha'aninka kana zuwa duk inda kake so”

Ta fada tana janye mayafinta daga jikinta a take kirjinta ya bayyana, daman irin dinkin nan mai bayyana maman mace daga gaba.

“Ai kin san halin wani namjin ba daya ne da wani ba, kin ga ke idan mijin ki mai sauki kai ne baban naki ba shi da dama”

Na fada tare da kiran Aminu da babanta kamar yadda take kiransa kasancewar sunan mahaifinta ne.

“Babu namijin da yake da dama Halima, ni kin ga mijina Wallahi zan iya tafiya wani garin na kwana iya kwanakin da naji sun min na dawo be isa ya ce min komai ba”

“Too ku manya ne Sa'adatu”

Na fada cike da sha'awa da kuma jinjina abunda ta fada, ko bata fada min da bakinta ba na san zata iya domin ta saba zuwa wani gari da sunan biki ko ganin yan'uwa ta bar masa yaransa sai ranar data ga dama ta dawo kuma ba zai yi komai ba. Abun har burgeni yake ni da wani lokacin ko makota sai Abban Namra ya hana ni zuwa.

“Wai ya kika ba ni ruwa zalla a tsirara ba masu kala ne?”

“Baban na ki ne be siyo masu kala ba”

“Aa Babana fa komai kawowa yake karki cutar da shi, daman kin saba bakin sherinki ni bari ma na tashi daman bankwana na zo nai miki zanje Kaduna gobe In-Sha-Allah”

“Kaduna kuma? Gurin me?”

“Wallahi wani abun bikin ne ya taso mana zanje na kwana hudu ko sati ma a can”

“Da yaran zaki je kenan”

“Aa ni kadai zanje na shakatawata abuna yara su zauna gurin Babansu”

“To indai baki yi hankali ba sai ya dauko miki wata”

“Ai be isa ba Wallahi wa? Ni? Hmmmm ai na bashi wannan ya shanye”

Ta fada tana wani turo dankwali tare da nuna min kasan kafarta.

“Haka fa, na ji ance ana yi ko?”

“Au tsayawa ji kikai? Ba ki ma aikata ba”

“Ina ganin kamar akwai rashin dacewa a haka”

“To yar sarkin Malamai”

Dariya nai zan sake magana sai jin tsayawar motar Abban Namra mu ka ji, a take gabana ya fadi domin na san zai tambaye shi yaransa gashi tun da na aikasu basu dawo ba, kamin ya shigo falon hankalina ya tashi sosai saboda aiken da nai musu ga kuma fita kai Namra asibiti da nai ba tare da izininsa ba na san zai iya yi min fada a gaban kowa, ni kuwa abunda na tsana kenan ayi min fada a gaban wani musamman kawayena.
Fuska a hade ya shigo falon ni kuma nai saurin mikewa tsaye na nufi inda yake ina masa sannu da zuwa tare da kai hannu na karbi jakarsa.
Da kamar ba zai amsa min sannun da nai masa ba, sai dai yana gada ido da Sa'adatu sai ya sake fuskarsa.

“Yauwa, a a diyata ce da kanta a gidan?”

“Nice Babana ya garin ya gararin garin?”

Ta amsa tana wani karkada ido, na yi zaton ko zata ja mayafinta ta rufe kirjinta ne kuma ta gyara ture kaga tsiyar da tai na dankwalinta amman ba ko daya, zama yai a kujerar da ke facing din tata yana murmushi.

“Fatar kin zo lafiya?”

“Lafiya kalau matarka ta bani ruwa masu sanyi amman ba masu kala na yi magana tace Babana be siyo ba”

Sai juyo yai ya kalleni ina kokarin zama kusa da shi.

“Ah ah drinks ya kare ne daman? Ai baki fada min ba”

Kasa ce masa komai nai bayan kallon mamaki da nake masa rabon da ya siyo mana wani abu mai sunan lemu mu sha a gidan har na manta, amman yau saboda ya nuna yana siya har yake tambayar yaushe ya kare? Haka yake min idan ya ga mutane ni kuma bana iya karyata shi.

“Jiya ya kare”

Na fada ina hade yawun bakina.

“Okay bari sai gobe a siyo ai ban sani ba, ina fatar kin ci abinci?”

Ya karasa yana naida dubansa gurin Sa'adatu.

“Aa ban ci ba”

Sai ya juyo kaina.

“Miyasa ba a bata abinci ba? Ko ba a gama ba? A kawo mata abincin mana”

“Aa ni tafiya ma zanyi”

Ta fada tana janyo mayafinta ta rufe jikinta tare da gyara dankwalinta. Sai shi ma ya mike tsaye da sauri yana ta kallonta.

“Bari na rage miki hanya, ina takardar maganin take?”

“Tana daki”

“Je ki dauko sai na siyo daga can”

Har na bude baki nai magana ganin da gaske yake zai wuce da ita sai kuma wata zuciyar tace nai kawaici na kyale shi. Dakina na shiga na dauko takardar maganin na kawo masa sai ya karba yana duba sannan ya kalleta ya ce.

“Muje”

“Matar Baba sai wani gamon kuma”

“To Allah ya kiyaye hanya”

Na fada ina binsu da kallon zuciyata na mugun tsoyuwa. Sai da suka fice daga falon na koma gurin windows din ina hangensu har suk shiga motar yaja sukai gaba, ajiyar zuciya na saki tare da sakin labulen falon sannan na dawo saman kujera ya zauna, na san Sa'adatu zata dauki hankalin Aminu saboda bata da jiki kamar ni kuma ita fara ce sosai kamar dai yadda yake yawan fada min yana son mace fara marar jiki ba irina ba. Tunanin yadda zan yi na rage kibar ne ya fara zuwa min a rai shi farin na san mai sauki ne zan iya siyen mayukan fari na shafa nai fari amman rage kibar ne zai ba ni wahala domin na gwada abubuwa da dama na rage kibar har yau ban dace ba, sai a yanzu na tuno da wani maganin rage kibar da na siye, tashi nai na nufi upstairs, ina shiga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login