Showing 327001 words to 330000 words out of 420383 words
Chapter 110 - SAI KA AURENI DOLE BY AYSHA A BAGUDU.txt
matar agurinka?
Alhaji Adam "yace yar'uwatace uwa daya uba daya..
"tana da miji ne?
"a'a tare take zaune da yarinyarta"
"Ok bisa ga bincikenmu mun gano anyi mata amfani da wasu kwayoyin maganin bacci masu karfi ta hanyar raunata mata jiki gaskiya da bad'an anyi sauri kawota ba da bamusan abinda zai faru ba.
"magani bacci fa?
"eh "
"dan Allah Alhaji tunda kuna da halak'a me k'arfi daita ka taimaka kasanya idanu akanta dan irin wannan maganin zai iya kashe mutun kai tsaye Saboda anyi mata overdose dinsa .
Alhji Adam yashiga mamaki yana tinani ta yadda hakan zai faru kusan minti goma yana zaune baice komai ba yana sauraron bayanan likita har sai dayaji likita ya dasa aya, sannan yace gsky nayi mamakin yadda hakan ta kasance .
doctor yace "wannan bawani abun mamaki bane adai sanya ido sosai "shikenan zanyi kokarin yin haka inji cewar dady ya
mik'e tsaye yana mikawa doctor hannu tare da yi masa godiya "yace Insha Allahu zan saka ido akanta sosai .
Atakaice sai da mama tayi kwana uku a awurin likita sannan aka sallamota kai tsaye Alhaji Adam yace a wuce da ita gidansa domin ta dinga samun kulawa.
*bayan wata biyu*
Zaune Abdullabir yake akan kujerar kushin me zaman mutun uku system ne akan cinyarsa yana operating dinta cikin iyawa da k'warewa sanye cikin wando blue jeans da riga ash colour me gajeren hannu kayan sunyi masa kyau sosai ga wani sihirtaccen kamshi da jikinsa keyi tamkar ajikinsa ake sarrafa turaruka gaba d'aya id'an kashaki kamshin turarensa sai karasa takamaiman wani irin kalar turare yayi amfani dashi ,duk maitar mutun haka zai hak'ura matsawar bashine ya fad'a ba koina ka kalla ajikinsa abun birgewa ne fatar jikinsa tayi luwai luwai kwantaccen gashin jikinsa sun sake kwantawa abun sha'awa sosai yayi busy gurin aiwatar da aikinsa.
su'ad zaune agefensa cikin shigar wando baki da riga pich colour wace bata wuce cibiyarta ba, lallausan bakin gashin kanta sun zubo bisa kafad'ar ta ,tasashi gaba tana aikin kallonsa, sai dai ta cika tayi bammm sakamakon ganin yadda ya shareta yana cigaba da aikinsa tamkar ma bai san da wata halitta zaune agefensa ba, hakan yasa ta mik'e cikin fushi zata bar gurin zaraf taji ya riko laulausar tafin hannunta cikin nasa yashiga murzawa ahankali yace "ina zaki kuma?
yayi maganar batare daya d'ago ya dubeta ba, idanunshi still na kan system yana faman operating.
muryarta a shagwabe tace "zanje na kwanta ne zamana agurinan bashida wani amfani tun dazu ina zaune zaman jira gara naje nayi bacci.
"ki zauna nakarasa abinda nakeyi muje mu kwanta tare dan ko kinyi bacci sai kin tashi kinji dani.
"to to ni gaskiya nagaji bacci nakeji tun d'azu nake zaune amman gaba d'aya ma ka manta dani a zaune sai wani faman aiki kakeyi tamkar agogo...
murmurshi yayi tare da cewa"ni na isa na manta da sauraniyar mata, abinda bakisani ba kina cikin nan ya nuna mata tsaitin zuciyarsa da d'ayan hannunsa,ki d'an bani 10 minti yanzu zan gama.
gaba d'aya narke fuska tayi ala'mun shagwab'a taki ce masa komai jin tayi shiru taki cewa komai yasa ya d'ago a kaikaice yana kallonta taso kawar da fuskarta amman ta kasa saboda yarigada yasanya kwayar idanunsa cikin nata yana aika mata da wani shu'umin kallo me tattare da shaukinta wani abu taga suna fitowa acikin idanunsa suna shiga cikin idanunta suna narka da zuciyarta akan tsantsar kaunar datake masa.
zuciyarta da kirjinta ne suka hau amsawa da karfi sakamakon idanunsa dake cikin nata, narainarai tayi masa da fararen idanunta kamar zatayi kuka.
ya matse hannunta da d'an karfi wanda yasa ta saki kara mara sauti tana k'ank'ame jikinta tare da kokarin zare hannunta cikin nasa taji ya fizgota gaba d'aya ta fad'a bayan wuyansa ,take tashiga kissing din wuyansa da kwantanccen sumar kanshi tare da sakalo hannunwata ta wuyansa ta rungume kanshi akirjinta tana jin wani irin zallar shaukinsa dake manne ciki kirjinta bakaramin mutuwa zaune yayi ba .
amman yashare ya daidata natsuwarsa akan screen din system yacigaba da aikinsa ganin hk yasa tashiga bashi hot kiss takoina daga karshe ta ratsa ta kwanto tsakiyar laptop tashige jikinsa ta kwanta tana mutsumutsu har tana zungure zandariyarsa yana jinta sai dai shi gaba d'aya hankalinsa na kan sarrafa computer ganin duk abinda take masa baisan yayi concentrate akanta ba, yasa ta mik'e ajikinsa ta koma tayi tsaye tashiga jifansa da Teddy shi kuma yashiga kaucewa idanunsa ya d'ago ya kalleta yana murmushi sannan ya sake meidawa kan aikinsa ajiyar zuciya ta sauke da karfi tana jan numfashi sama sama kamar wace tayi wani aiki sannan tasamu guri gefensa takoma ta zauna tare da hade rai sosai tana turo masa baki tana cika tana batsewa.
gaba d'aya kishi take da wannan aiki d'aya tasa gaba yakeyi ,wanda take ganin kamar yana k'ok'arin mantawa ne daita arayuwarsa, ahankali tasa kafarta d'aya tana kawar da fuskarshi akan kallon system ya riko tafin kafarta da hannunsa while d'ayan hannunsa na cigaba da aiki yashiga yi mata tafiyar tsutsa a tafin kafarta wani irin zillo tayi saboda wani abu dataji ya tsarga mata tundaga tafin kafafunta har zuwa cikin kwakwalwarta da sauri ta cire kafarta ta zube gabadaya ajikinsa tana masa kukan shagwaba hannusa d'aya yasa ya zagaye cikinta yana mata cakulkuli tare da kissing every part of her ita kuma sai dariya take sosai ta mik'e ajikinsa tana dariya hannunsa ya kai ya shafa beauty face d'inta wanda kallonsa ke saka shi cikin natsuwa ahankali yasa hannunsa kan brest dinta ya d'agota daga jikinsa ya zaunar da ita gefenshi yana bata hak'uri "sorry heart yanzu zan gama sai kiji dad'in yin bacci nasan jarabata kike bukata shiyasa kika kasa bacci yakarasa fad'ar haka yana murmushi ....
Aiko ta sake d'aukar baby teddy ta dinga jifansa dashi ya kamota ta zube jikinsa ta kwanta ruf da ciki ta juyo fuskarta suka hada ido, idanunsu suka tsarke cikin juna dukkaninsu murmushine bayyane a saman kyakkwar fuskarsu tsawon minti goma suka dauka suna kallon kwayar idanu junansu cike da matsanancin shauki.
d'agota yayi ya sake zaunar daita tare da shafo kirjinta yana hadiyar yawu "plz hrt i wil be true now atare suka sauke naunauyen ajiyar zuciya d'aga karshe ta sake dauke teedyy tacigaba da jefa masa "ni ni ban yarda ba Allah ka'ajiye aikin ya isa hk.
shima yashiga ramawa sake fadowa tayi jikinsa tashiga kissing fuskarsa cikin kunnensa hancinsa ta gangaro bakinsa ta shiga tsotsan lips dinsa kusan minti goma ta dauka tana tsotsar bakinsa sannan ta zare bakinta cikin nashi "wayyo Allah ya sauke naunauyen ajiyar zuciya yana lumshe ido dole tasa ya dakatar da abinda yake ya turo mata bakinsa bata tsaya bata lokaci ba ta cafki bakinsa, laulausar harshensa tashinga sarrafawa cikin bakinta tamkar wace za'a kwacewa gaba d'aya gashin kanta yagama bajewa ya rufe masa fuska ya sanya hannunwansa duka ya tattara ya maidasu bayanta ya kamo fuskarta da tafin hannunsa yasanya idanunsa cikin nata yana kallon cikin kwayar idanunta yana tsotsar bakinta sosai suka shiga aikawa juna zafafan romance kafin daga baya ya dauketa cak sai saman italy bed d'insu daga nan suka fada duniyar Ma'aurata .
haka kawai Ak ya dinga tsintar kansa cikin yawon faduwar gaba haka itama su'ad wanda ita kam har sai da ta kai ga gaya masa halin faduwar gaban data tsincin kanta ciki, shima bai boye mata ba yace" haka yake jinsa a duk kwanakin da suka gabata, wasa wasa fa faduwar gaba ta sakasu gaba yanzu haka zaune yake akan kujera yayi zurfin cikin tinani abinda ke sashi yawon jin faduwar gaba gashi cikin lokacin tinanin zeey ne ke yawon zuwa masa wanda yarasa dalili su'ad ce ta karaso inda yake hannuta rike da glass cup ta mika masa hollandia me sanyi ya amsa ya sha ta amsa cup din ta ajiye sannan
ta kwanta saman cinyarsa tana jansa da hira "Abdul takira sunansa..
"zuciyarsa na tsananta rawa gabansa na faduwa ya amsa atakaice "ya'akayi heart beat?
"ina ji ajikina wani abu na shirin faruwa damu amman ina addu'ar Allah yasa yazamo alkhairi ne arayuwarmu...
ya bude bakinsa kenan da niyyar amsawa yaji gabansa yayi wani irin mahaukacin bugu take kuma gabansa yashiga fad'uwa fat fat gabad'aya jikansa yashiga rawa ya dinga jin duniya na jujjuyamasa cikin k'ank'ani lokaci yanayinsa yasauya jikinsa na rawa ya ture su'ad dake kwance a saman cinyarsa sai dimm kakeji a kasa yayi zunbur ya mike tsaye yana kallonta yana kallon parlour 'n dayaji yana jujjuya masa, hankalinsa a matukar tashe ya nufi d'akinsu .
su'ad wace ke rike da gefen cikinta tana yatsina fuska tana kallonsa saboda taji zafin jefar da ita dayayi cike da matsanancin mamakinsa ta mike tsaye tabi bayansa tana kiran sunansa Abdul Abdul!!! d'an ji tayi gaba d'aya ta daina jin zafi.
tana karasa shiga dakin ta isa gareshi tare da kai hannunta jikinsa zata tab'asa yayi saurin buge mata hannu yaje ya kwanta gaba d'aya hankalinsa da tinaninsa yakoma kan Zee daya rufe idonsa Zee yake gani gabad'aya ya haukace acikin d'akin daren ranar bai runsaba haka su'ad duk inda yayi tana binsa tana kuka da kokarin kamoshi jikinta .
Hankalinta yayi k'ololuwa tashi takoma kamar wata zararra hawayen majina duk sun wanke mata fuska gashin kanta ya watse ya baje cikin k'ank'anin lokaci tafita haiyacinta koma kamar wata mahaukaciya.
Kuka take wiwi tana bin AK duk inda yasa k'afa tana faman cewa.
"Abdul " meke damunka ?
"dan Allah kagaya min idan wani abu nayi maka nabaka hakuri sbd banason ganinka cikin damuwa takai hannu zata tab'a shi yayi saurin buge hannunta ya sake wurin zama sam baya k'aunar tarabe shi .
a halin yanzu idan AK na k'aunar mutuwan shi to yana k'aunar su'ad tarabe shi.
Daf da asuba AK zaune abakin gado ya zuba uban tagumi Zee kawai yake tunani hade da buk'atar son ganinta.
A hankali su'ad ta lallabo tafad'a saman k'irjin shi a matuk'ar zabure AK ya mik'e yayi cilli da su'ad jikake k'ummmm muryarsa cike da hargagi yace "kina hauka ne ko kin sha wani abu ne?
jikinta na rawa ta sauko daga kan gadon ta durkusa gabansa ta kamo kafafnsa "dan Allah mijina farincikina duniyata karka tsiro min da abinda zuciyata bazata iya dauka ba idan ka nemi nisanta kanka dani komai na iya faruwa dani..
ko bi takanta AK beyi ba, su'ad wace ta buga goshinta a jikin gado zunbur ta mik'e dafe da goshi domin tabugu sosai har wurin yatashi amma bata bi ta jinkita ba taci gaba da bin AK sukaci gaba da zagaye d'akin.
Haka suka kwana babu wanda ya runtsa shida ita har gari yawaye.
Gari nawayewa AK ya hau shirya kayansa tsab ya dauko passport dinsu yasoma shirya musu tafiya zuwa gida nageria.
acikin jirgi kuwa zama ne akayi shi babu ruwan wani da wani tmkr wasu kurame suka dawo sabanin lokacin da zasu baro Nigeria suna manne da juna tare da nuna tsantsar kulawa .
yanzu kam kallo daya zakawa fuskokinsu kagane cewar suna cikin damuwa me tattare da tashin hankali kowanensu da abunda ke damun zuciyarsa sai dai damuwar su'ad ta ninka ta AK dan tun da suka baro kasar spain kuka take har sanda jirginsu ya lula samarin samaniyya shi kuwa ko ajikinsa asalima toshe kunnuwansa yayi da earpiece.
misalin karfe shida daidai na safiyar laraba jirginsu ya sauka a murtala international airport .
mmn sudais ce
💗💗💗💗💗💗
SAI KA AURENI DOLE
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~NA~
*AYSHA A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
HAUWA A USMAN
JIDDARH
YA MUSAWWIR
THE FASHIONER OF SHAPES.
page 73
suna gama fitowa daga cikin jirgi yayi gaba abunsa yabarta abaya ,tabiyo bayansa cikin hanzari har suka karaso inda motocin kafaninsa ke zaman jiran karasowarsu bai juya yaga a wani hali take ciki ba.
direbansa na hangosa yayi saurin bude masa gidan baya yashiga ya zauna yana jin kmr ana zuba masa wuta ne agabadaya ilahirin ajikinsa Allah Allah yake ya isa yaga zeey dinsa, wannan shine Karo na sau ba adadi dayake ja tsaki yana shirin bawa direba umarni tada mota takaraso cikin sauri tashiga motar direba ya meida murfin mota ya rufe, yana ganin tashigowarta yayi saurin kawar da fuskarsa gefe dan baya kaunar kallon fuskarta, ta juyo ahankali ta saci kallon inda yake duk da bataga fuskarsa ba ,tasan ran nan nasa a hade yake tmkr wanda aka aikowa da sakon mutuwa har suka dauki express din da zai kaisu ikeja a long tsaki ya dinga ja yana jijiga kafarsa daya, hannusa daya km na saman cinyarsa yana shafawa ahankali .
kai tsaye yabawa direba umarnin ya nufi gidansu zeey dashi ,su'ad ta juyo a firgice ta kalleshi zuciyarta na wani irin harbawa da karfi amman babu fuskar dazatayi magana haka yasa takoma ta kwanta jikin kujerar motar tana sauke numfashi sama sama take tashiga karanto addu'oin samun natsuwa cikin ranta.
gudu direban yake sosai amman gbdy ak ganin yake tmkr ba gudu yakeyi ba ,dan haka yace"kule ka sake taka mota sosai , "sir ai karshe gudun motar kenan.
minti goma kacal ta kawo su unguwarsu zeey, koda suka isa kofar gidansu zeey direba yayi parking a kofar gidan , ya fito cikin sauri ya nufi karamin get din gidan batare daya jira direban ya bude masa jikinsa na tsuma yashiga buga get da iyakacin karfinsa, me gadi yataso ya bude yana gaidashi cike da girmamawa, zai shiga cikin me gadi "yace ai babu kowa acikin gidan gabansa yaba rasssssss tare da zaro ido waje muryarsa na rawa yace "ina sukaje?
me gadi yace "sun d'an jima basa gidan suna gidan alhaji Adam lumshe mayatattun idanunsa yayi bai sake cewa komai ba ya juya cikin sauri.
********
suna isa gidan ammi dake zaune a parlour ita da mahaifiyar zeey da eiman sai hannutu me aiki ta mike cike da murna ta tarbesu cikin farinciki ganinsu ta rungume su'ad ajikinta, jiki a sanyaye su'ad ta rumgumeta itama tana murnar sake ganinta .
cikin tsananin farinciki ammi tace "shiyasa na dinga jina cikin yanayi biyu ashe diyata ce tafe sannu da zuwa .
dumin jikin su'ad yasa ammi zareta daga jikinta tare da tsura mata ido sannan tace "Bakida lafiya ne naki jikinki kamar garwashin wuta?
kai kawai su'ad ta iya daga mata batare da tace daita komai ba dan koda tace zatayi magana kuka ne zai biyo baya .
kusan eiman tafi kowa murna dawowarsu ta janyo hannu su'ad suka shiga dakin ammi suna rungume da juna.
shi kuwa ak sai baza idanu yake yaga ta inda zai ga zeey kawai yake amman bai ganta ba , ita kuwa zeey tunda taji dawowarsu tashige kuryar dakin da suke zaune da mahaifiyarta ta kulle kanta ta dinga tikar rawa tana dariya da murnar burinta zai cika, wahalarta tazo karshe zata samu abinda takeso muradin ranta ya dawo ta aiyana aranta bazata bari yasanyata acikin idanunsa ba har wahala gurin nemanta .
takira kawarta bolaji tana gaya mata zance dawowar ak murna tayi sosai "gsky dole kiyi murna kawata wannan daukar hutu da kikayi batare da an yi miki savices me kyau ba, nasan gurin na can yayi giress ina nan zuwa gobe da lemun tsamina na wanke miki gurin tsab dan ak yaji dadin caccakarki, suka saka dariya atare .
"wallahi bolaji bakida kirki to waya gaya miki tun wannan lokacin zaune nake ba harka?
bolaji tace "wai da haka nayi tinani ganin mama bata barinki fita koina.
"tab ai in gaya tunda muka dawo gidan na koma ruwa tsumdum nida akil dina muke cin duniyarmu babu tsinke .
"allah kawata"
"wallahi ke ko sherajiya mun hadu dashi a citedal hotel dake nan underbridge din dake kusa da gidan nan ai bazan iya zama babu harka ba ,ai naga kokarina ma danayi cikkaken wata uku babu harka .
"gsky kinyi kokari sosai dan banyi tunanin zaki iya hakurin hakan ba a yadda nasanki kmr kura inji cewar bolaji tana kwashe mata dariya daga karshe suka zarce da hira batsa .
shiru2 ak baiga fitowar zeey ba tun yana dauriya har yashiga bulayin nemanta, yashiga wannnan dainin ya fito yashiga wacan dakin ya fito yana hauka kiran sunanta wanda hakan yabawa duk wani wanda ke cikin gidan mamaki, kusan awani goma kenan da dawowarsu amman har zuwa wannan lokacin bai sanya zeey acikin kwayar idanunsa ba , wannan dalilin dayasa ya haukace musu agidan tausayinsa ne yakama maman zeey ta tashi da kanta tashiga daki inda zeey ke kwance cikin kuryar daki, ta kwankwasa kofar tana kiran sunanta "zainab zainab !!
"waye?
"nice dan Allah malama kixo ki bude min keda waye zaune a dakin dazakice waye mama takarasa mgnr tana jan tsaki.
zeey dake kwance ta tashi ta bude mata kofar takoma ta kwanta abunta mama takaraso ta zauna kusa daita "ki tashi kije tun safe abdulkabir ke bulayin nemanki acikin gidan nan banga dalilin wannan wulakanci ba alhalin nasan abukace kike da ki koma gidansa "ni dai shawara zan baki wannan itace damarki ta karshe, kin dai san halinsa sarai ba sai nagaya miki ba.
"nifa mama babu inda zani, wata nawa ni nayi ina hauka akansa amman yayi burus dani wallahi sai nima na gasa masa aya a hannu "nidai tashi kije kada uwarsa taji babu dadi aranta dan bakiga yadda hankalinta ya tashi ba.
"naji mama zanje amman kafin na zan roki wata alfarma guda daya duk abinda zai biyo baya atsakanina da abdulkabir bana son kice komai matawar ba bayana zaki bi ba.
mama ta tabe baki tana dubanta a dan atsorace saboda batasan dalilinta na fadar haka ba sannan tace "kinji shirmen banza ni
19, September 2025
Aisha Auwal
Wow