Showing 189001 words to 192000 words out of 420383 words
Chapter 64 - SAI KA AURENI DOLE BY AYSHA A BAGUDU.txt
daga bayansa kar ka sake ka fara taba lafiyarta, karkayi kuskuren aikata hk domin ba yarda zanyi da hkn ba ..ahankali ya sauke hannuna yayi saurin waiwayowa ahankali yaga kowaye ya katse masa hanzari .
wata kyakkyawar mata yagani zaune tana kallonsa a wulakance, matsowa yayi sosai ya tsaya agaban umman yana kallonta tsab ,kawai rasa abinyi AK yayi sbd yadda yaga fuskar matar har lokacin tana watsa masa matsiyacin kallo sannan tana cikin wani yanayi daya kasa fassarawa, ko daganin hk sai shima ya xuba mata ido kmr yadda tayi masa yana kallonta sai daya gama kallonta tsab
" muryarsa a fusace yace wace ke....?
"sannan me ruwanki da marin da zan mata da har zaki dakatar dani ?
da ruwana sbd nice nan na kawota duniya tayi mgnr tana nuna kanta kakiye dan ban haifi jaka ba balle ka mayar min da "ya" abin wulakantawa ta bashi amsa da hk.
"ohh kice kece uwar wannan tantiriya shugaban yan jagaliyar data addabi al'umma?
ya juyo inda su'ad ke tsaye yana kallonta atsiyace lallai kin cika uwa aike ba uwa yakama akiraki ba.... dau.. yaji saukar wani gigitaccen mari a fuskarsa wanda yasashi yin shock atsaye tare da zaro idanunsa a matukar tsorace yana kallonta eye's to eye's ita ce maresa ko km wani ne da ban? yayiwa kansa tmbyr acikin zuciyarsa .
"tsaki ta ja tana kallon kwaryar idanunsa kul.. ka iya bakinka kasan me zaka gayawa mahaifiyata ita din ba kmr kowace uwa bace, ina sonta fiyye da komai, ina girmamata km ina son a girmama min ita duk rashin mutuncina bazan kalli tsabar idanun uwarka nace zan zageta dan hk kasan abinda za fada mata....
hannusa ya daga a zafafafe zai zabga mata mari tayi saurin dukawa kasa tare da matsawa baya,aiko ya dauketa da kafafunsa tayi sama ta dawo kasa tim ..yashiga dukanta , umma naganin hk tashiga kururuwa tare matsowa ta rike hannunsa gam tana yiwa commissionier nuni da idan yayi diyarta illa bazata yarda ba... ..
a wulakance AK "yace ki sakar min hannu tun ban hada dake ba yanzu bazan saki hannuka ba sai ka sakar min "ya" tunda ba jakar ubanka bace take office din commissionier ya hargitse da hayaniyarsu har sai da wasu police guda biyu suka shigo suka shiga tsakanin AK da su'ad datake rike a hannunsa ,da kyar commission yasamu ya shawo kansa ya hakura ya zauna yana huci dan cewa yayi sai ya mata illar da har ta mutu ba zata manta dashi ba ...
shi kansa commission ya dade baiga mace me taurin zuciya irin su'ad ba, ya sallemi umma yace ta wuce gida zai nemata .
"bazani koina ba commission duk abinda za'a yi ayishi agaban idona ,yarinyata tayi laifi km ta amsa laifinta har ta bayyana inda yarinyar take an daukota "me zai hana abani beling diyata na wuce gida daita?
"idan km zamu shiga koto ne to?
"duk mgnr bai kai ga hk ba amman yanzu zamu so musan sbd me su'ad din ta sace amaryarsa aranar kamunta sannan musan abinda yasa take bibiyar wannan yaron?
"ni nasan halin yarinyata hk kawai babu wani dalili bazata dinga bibiyarsa ba ,kai dai tmbyi shi wannan mara kunyar ko akwai abinda yayi mata..
karki fada hk domin idan kikace hk ya nuna ala'mun kina bin goyon bayan diyarki da daure mata gindin yin duk abinda tagadama which's bad..
"ga ta nan agabanka ka tmbyeta tunda nake da su'ad ban taba cewa ta aikata mugayen ayyuka ba, kullun fada da addua nake mata, duk uwar arxiki bazata so diyarta ta dinga abinda su'ad takeyi ba ,nasan bata da gsky acikin lamarin amman tunda ta amsa laifinta ai ina ganin komai zaizo da sauki tunda ko koto akaje alkali zaiyi saurin zartar mata da hukucin da yadace .
"ok yanzu dai kije gida domin musamu muyi binciken dayakamata akan aikinmu kina kallo tun awa uku nake fama daita amman taki bani hadin kai.
babu inda zani commission zan dai tsaya a kasa najira har lokacin da zaku gama sannan matsawar wannan dake huci kmr maciji ya illata min yarinya zan shigar da kara koto .
"reacting dinsu irin daya banbacin kadan ita uwar batayi kama da yar ba sannan yanayinsu ba daya bane inji commission wanda yayi mgnr cikin ranshi.
"ok kije waje kijiramu ,umma ta nufi kofar fita tare da budewa ta fice.
commissionier ya numfasawa yana kallon AK dake huci kmr kumarcin maciji sannan ya kalli su'ad dake girgiza jikinta ya nuna mata kujera da hannunsa ala'mun ta zauna kusa da AK .
"karka damu ranka ya dade barni a hk kawai AK ya kallota a kaskance yana jan tsaki da karfi dan har ranshi yasoma tafasa akan yadda commission yayi mata .
tsakin daya ja yasa su'ad sakar masa harara tare da cewa kallon km fa?
ak yayi mata banza dan bai ga abin bata bakinsa wajen bawa amsa ba,
shi kuwa commission bai damu da jin abinda tace ba yasoma mgn kmr hk muna son ki sanar mana ko akwai wani abu dake tsakaninki da abdulkabir wanda yasa kike bibiyarsa duk inda yaje, akaro na karshe..
sannan meye hujarki na sato masa amaryarsa aranar kamunta?
murmushi mugunta su'ad tayi tana duban commission a kyakyace sannan tace babu komai ranka ya dade...
"karya kike ina jin ba wannan ne Karo na farko da abdulkabir ke kawoki gurinmu akan matsalar kina takurawa rayuwarsa ba dan hk karki kuskura kice mana babu komai domin wannan karon ina tabbatar miki ko shi bai dauki mataki akanki ba hukuma zata dauki mataki da hannuta ,dan hk tun wuri ina umartarki ki sanar mana da gskyr lamari ,sai mu sakeki salin alin batare da an taba lfyr jikinki ba.
amsar data bashi da farko ita din ta sake gaya masa wato babu komai ,yayi juyin duniya daita akan tasanar masa amman taki ta tsaya akan babu komai har suka shiga exchange word da commission yayinda AK yazama dan kallo agurin cike da mamaki.
commission ya rasa ta ina zai bullo mata yayi nasara akanta shr yayi kawai yana kallonta can km wani idea yazo masa.
yayi saurin gyara zamansa "yace idan baki gaya mana gskyar lamarin abinda yasa kike bibiyar abdulkabir ba zamu tsareki tare da mahaifiyarki har sai mun gama bincikenmu akanki .
"a wani dalili? ta tmbyeshi "naga a dokar kasa babu dokar data bada wannan damar tsare wani akan wani ya aikata laifi ,nice nan nayi laifi ni yakamata ku tsare ba mahaifiyata ba sbd ita bata muku komai ba.
"za'a soma wannan dokar akanki matsawar baki gaya mana gsky ba.
,duk inda ran AK yake yayi matukar baci, da iskancin yarinyar . commission ya dubeshi abdulkabir ko zaka iya tuna ko wani abu ya taba shiga tsakaninka daita ko ta cacar baki ne?
AK ya dago idanunsa dake cike da tsantsar bacin rai ya zubawa commission yana kallonsa, sannan ya bude bakinsa da kyar "me zai shiga tsakanina da wannan yar iskar yarinya wallahi ina tabbatar maka ko hanya ban taba hadawa daita ba idan ba'a dan wannan lokacin ba....
commission ya dauki waya yasoma daddanawa , can aka dauka "yace asp ganiyu,yakira sunan yana jujjuya kujerar dayake kai zaune "bangare asp ganiyu kuwa kamewa yayi sosai tare da cewa yes sir..
" matar data fito daga office dina yanzu ku tsareta ku kaita cell dan... ai su'ad najin hk ta birkice tasoma kuka muryarta na craking tace pls commission kar saka mahaifiyata cikin cell bata cancanci shiga cell ba ,ita din me daraja ce ba kmr sauran iyaye ba.
"tunda baki son asaka mahaifiyarki cikin cell why not ki gaya mana gsky "akwai matsalar ne commission........
" ita gskyr da kake bukatar sani akwai matsala akanta idan na fadeta .
"dan girman allah commission kar ka bari na fadi ita wannan gskyr fadar abinda ke tsakanina da abdulkabir daidai yake da fadawata cikin halaka ...
"kenan dai akwai wata a kasa kenan ?
"AK dake zaune yace ka daina wani lallabata daday dan nasan babu wani abinda na taba yi mata arayuwata.
" kawai dai tsabar iskanci ne irin nata .
"aiko yau zata ga karshen iskancin daya fi nata matsawar bata fadi gsky ba.
yakarasa mgnr tare da cewa kai asp ganiyu ka aiwatar da abinda nasaka kawai, dan har lokacin yana kan layi.
"jikin su'ad na rawa tace zan fada commission.... "zan fada da dai a saka min uwa cikin cell na gwamaci na fadi koma meye tsakanina dashi idan yaso duk abinda zai sameni na yarda yasameni, takarasa mgnr tana kuka wiwi.
ta juyawa musu bayanta ahankali tare da hade hannuwanta duka waje daya ta rufe fuskarta hawaye nabin kuncinta...... commission ya dakatar da asp ganiyu sannan ya fuskance da kyau.
"uhm muna jinki ?
ta juyo ahankali tana kallonsa kawai wasu sabbin hawayen na sake gangaro mata, sannan ta bude bakin da kyar zan tasoma mgn "zangayi komai dake tsakanina da abdulkabir wanda yasa nake ikirarin sai ya aureno dole da bibiyar duk inda yaje amman sai agaban iyayensa da mahaifiyata.........
mmn sudais ce
💗💗💗💗💗💗
SAI KA AURENI DOLE
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~NA~
*AYSHA A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
HAUWA A USMAN
JIDDARH
*bissimillahir rahmanir rahim*
*hasbunallahu wani'imal wakil*
page 48
yadda suke kallonta cike da matsanancin mamaki sbd da furucin datayi, hk itama take binsu da kallo daya byn daya most especial AK dake zaune wanda gbdy ya tattara hankalinsa kacukan akanta byn ya tsareta da mayatatun idanunsa yana kallonta.
wani birkitaccen yanayi ya shiga kafin daga baya ya dawo cikin haiyacinsa ya sake ware idanunsa sosai akanta bakinsa mgn yake son yi amman ya kasa sarrafa harshensa.... .
ita kuwa wani bakinciki ne ya tokare mata kahon zuciyarta wanda yasa hawayen idanunta tsananta gangarowa bisa kuncinta .
"batason bayyana wannan sirri dake tsakaninta da abdulkabir, wanda yake daidai da tarwatsa rayuwarta a karo na biyu matsawar tayi kuskuren fadarsa . amman babu yadda zatayi da rayuwarta ya zamemata dole ta bayyana wannan sirri kodan martabar mahaifiyarta .
tayi hkr ta jurewa kaddararta data samar daita balle wannan damuwar......tayi imani duk abinda ke tafe da shafukan rayuwarta daga Allah ne.
tayi mgbr imani da hukuncisa gareta tare da yarda da kaddararta me kyau ko akasin hk .
abubuwan dake faruwa daita kaddara ce wace bata isa ta canzawa kanta ba.
commission dake zaune ya sake gyara zamansa lokacin dayake jin wani irin tausayin yarinyar yana bin Jinin jikinsa.
ya tabbatarwa kanshi tabbas akwai wani sirrin boye dake tsakaninta da abdulkabir.......adduarsa Allah yasa ba abinda yake tunani bane ya taba shiga tsakaninsu....
muryarsa ahankali ta fito gurin cewa "ki natsu ki dawo cikin haiyacinki nima tmkr mahaifin abdulkabir ne duk abinda kika san yana tsakaninki dashi ki sanar min dan ina tabbatar miki tmkr yaje kunen mahaifinsa ne.
dan hk karkiji komai zaki iya sanar dani komai .
girgiza kanta tashigayi tana kuka wiwi tare da daura hannuwanta duka bisa kanta alamun tana cikin tashin hankali sannan muryarta cike da kuka tace "kmr mmahaifi kace ,kmr mahaifi kuwa bazai taba zama mahaifi ba, dan hk ka kirasu zuwa nan kawai, ko muje gidansu tunda na rigada na amince zan fadi komai ......takarasa mgnr tana sake sakin wani Sabon kuka me taba zuciya sbd tuna makomarta da zarar ta bayana komai dake tsakaninsu.
juyin duniya commission yayi daita akan tasanar masa amman fafur taki tace zatayi mgn amman sai agaban iyayensa ,dan hk ran ak yayi matukar baci ya zabura ya mike tsaye ilahirin jikinsa na kirrma ya damki hannunta cikin nasa cikin matsanancin fushi yasoma janta commmission na masa mgn ,yayi banza dashi ya nufi kofar fita daita, kafin commission ya ankare tuni har ya fice daga office din.
janta yake tana biye dashi abaya tana kuka kmr ranta zai fita har ya iso farfajiyar police station , kai tsaye inda yayi parking din motarsa ya nufa daita ya bude mata gaban mota ya watsata ciki ya Rufe murfin motar da Karfi ya zagaya yashiga mazaunin direba ya tayar a fusace.
tun daga nesa umman su'ad ta hango yadda AK ya sauko daga saman commmission janye da hannun su'ad yana janta har ya sata cikin motarsa.
cike da matsanancin tashin hankali tasoma kokarin cima masa amman ina har ya tada motarsa, dan hk ta kurma ihu da kururuwa neman dauki tare da daura hannuta saman kanta tana kuka daidai lokacin da commission yakarasa saukowa yace ta bar kuka tabiyo bayansa suje.
tunda ya fita daga harabar police station din ya figi motar a guje duk wanda yaga irin gudun dayake dole ya bishi da kallo, wani irin gudu yake falfalawa akan titi na fitar hankali har suka iso unguwarsu bai ce mata komai ba itama hk batayi yunkurin cewa wani abu ba bayan sheshekar kukanta daya tsananta karfi ,yayinda AK yashiga tunani yadda zata kasance atsakaninsa daita agaban iyayensa gbdy tunaninsa ya tafi ne gurin son tuna baya ko ya taba wata mu'amula daita ko wani abu makamanci hk, amman har ya iso kofar tafkeken get din gidansu 'kwalkwaluwarsa bata hango masa komai daya taba shiga tsakaninsa daita ba.
hon yashiga dannawa da iyakacin karfinsa wanda ya firgita securities din bakin get yayinda take jikin baba me gadi yashiga rawa. cikin hanzari suka isa suka bude masa .
yasanya hancin motarsa xuwa cikin farfajiyar gidan yayi parking yasoma fitowa yana gyara zaman rigarsa ko rufe motar bai gamayi ba yace karamar tantiriya sai ki samu fitowa gamu agidanmu , kin fitowa tayi tacigaba da rera kukanta me taba zuciya, ganin zata bata masa lokaci yasa yazagaya ya fixgota daga cikin motar yashiga tafiya daita yana zaginta har zuwa parlour'n ammi inda ya tarar da iman da wasu daga cikin family's dinsu .
yana karasa shigowa parlour'n yayi wurgi daita wanda kadan ya rage kanta bai bugi glass din center table ba, ita km sai kuka take kmr ranta zai fita muryarsa a hargitse yace "sis ina ammi? yaya lfy dai ko? "ina ammi da dady yayi mgnr cikin karaji...? ta zubara ta mike tsaye cikin gigicewa ta nufi kitchen amadadin ta nufi bedroom din ammi. ya bude baki zai sake mgn kenan yaji sautin muryar
ammi.
abdul gani lafiya km na ganka hk duk a hargitse ?ammi ki zauna ina dady da kowa da kowa wannan karamar karuwar tantiryar shugaba yan iskan ce ke son gayamuku wasu banzanr magana wanda ni bansan dasu ba yakarasa mgnr yana nuna inda su'ad ke durkushe tana risgar kuka...fuskar nan nata yayi jawur.
zama ammi tayi a daddafe tana kallon inda su'ad ke durkushe gbdy takasa samun natsuwar zuciya hk kawai taji Gabanta na wani irin bugawa da sauri sauri tayi saurin runtse idanunta gam tana karanto addua acikin zuciyarta .
karasawa yayi har inda su'ad ke durkushe tana rusa kuka ya damki wuyanta ta baya wanda yabawa fuskarta daman bayyana sai daya gama kare mata kallon tsab sannan yashiga janta bisa gwiwowinta yana matso daita zuwa inda ammi ke zaune tana jin kmr ana fixgar rayuwarta .
sannan muryarsa a zafafe yace ammi ki bude idonki ki kalli idanun wannan tantiriyar mara kunyar da zantuttukanta ya kasa tsayawa akaina har sai ta dangana da iyayena.
ahankali ammi tasoma kokarin bude idanunta kirjinta na bugawa daf... daf ...tare da daurasu kan fuskar su'ad dake durkushe bisa gwiwowinta ai da wani irin sauri ammi ta dafe kirjinta sbd yadda taji gabanta yabada rassssssee .....tsoro da matsanancin firgici AK yaga ya bayyana a saman fuskar ammi dake zaune jikinta har rawa rawa yake yayinda shi km zuciyarsa tashiga bugawa da karfi.
ita km su'ad numfashinta ne ya soma barazanar daukewa sbd kukan datake cikin tashin hankali, da km yadda ya damki byn wuyanta.
cikin sanyi jiki Tasoma kokarin raba hannunsa da wuyanta ,amman ta kasa kwatar wunyata daga hannunsa .
zuba mata ido ammi tayi sosai tana karewa fuskar su'ad kallo tsab tare da jin zallar faduwar gaba . take kwalkwaluwarta tashiga caji akan wannan fuskar da take kallo agabanta .
ahankali ammi ta kai hannuwanta duka bisa fuskar su'ad ta kamo tana mata wani irin kallo zuciyarta na tsananta bugawa da karfi..
kafin daga karshe tasoma shafa fuskar su'ad jikinta na sake daukar rawa... shi AK km har lokacin yaki sakar mata wuya sai huci yake kmr wani kumurcin maciji.
yadda jikin ammi ke rawa hk murya take rawa gurin cewa "abdulkabir a ina kasamo wannan fuska?
wannan fuskar duk inda take nasanta, fuska ce wace bazata taba bace min ba har illa yauminl kiyamati..
ammi wannan fa itace mahaukaciyar yarinyar dake bibiyar rayuwata.....
a matukar tsawace ammi katse shi ta hanyar cewa "ubanka wannan fuskar ta wuce ka siffantata da mahaukaciya... ....dan ubanka ka sakar mata wuya.... wani irin yammmmmmm yaji ajikinsa tare da cire hannunsa a wuyar su'ad yana kallon ammi cike da matsanancin mamaki..wani abu yaji yashiga bin jikinsa tunda yatsun kafafunsa har zuwa cikin kwalkwarsa idan wani ya gaya masa ammi zata iya zaginsa akan wannan tantiriyar karuwar zai ce karya ne, sai gashi da kanta km agaban yarinyar datake kirarin bata son ya aureta take zagin ubansa.
cikin rawar jiki ammi ta mike tare da mikar da su'ad dake wani irin kuka yarinyar ya sunanki....? menene sunan mahaifiyarki da mahaifinki? a ina gidanku yake? ajere ammi ta shinga yiwa su'ad tmby wanda ita km kwata kwata takasa bude bakinta balle ta amsa mata.
cikin kuka ammi tace dan girman allah ki gaya min wacece ke da sunan iyayenki?
sill su'ad shiru tayi taki cewa komai.
ammi ta juyo a firgice tana kallon AK afirgice "maza maza kaje gidan minister kuzo tare yanzu yanzu ,yau ranar ce mafi dadi da farinciki arayuwata , byn wasu shrkaru da suka wuce " ammi wai tsaya menene hkn kike yi nifa bangane nufinki ba?
a think yau ne rana ta farko da kika soma ganin wannan yarinyar kin santa