Showing 30001 words to 33000 words out of 186303 words

Chapter 11 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18797

dawo gida nan suka baje ana ta raraba abincin ana mikawa makota sunna ta maida kirki da datako na wannan ahali, lalle abin ya ba makociyar Mama mamaki kuma irin yadda ta ringa maganar cewa take yi ai komaima sai a yiwa bayin Allan nan sun san darajar dan Adam........ Su Kausar kam kowace na nata uzurin ama kuma sunna jin firarakin su Maman har dare ya yi sosai ta mike ta shafa sabulun nan na wajen FUSAM ta barshi ya dan huta a fuskarta sannan ta wanke tana shafa fuskar ita da kanta cike da mamakin irin santsin da fatar nata ke yi, wannan dan fari farin na fatarta du ya fita yanzun sai wani sheki da fatar take yi ko bata shafa mai ba bata mata futu futun nan


A nutse ta kwonta a wajenta zuciyarta cike da farin ciki da fatan gannin babar ranar amini, dan uwa, aboki, yaya a wajenta, lalle wannan rana tana daga daga cikin ranakun da take fatan gani a duniya na alkhairi,


Murmushi ta yi tana dafe kitson da kai mata na hannu kora baya kannanu rass tana tunanin wai atach irin na kitson nan suka siyo rauda rauda za'a saka masu a keya, ita kam bata san ko zata iya yarda da wannan bidi'ar ba, sai kuma ta sake sakin murmushi a hankali ta furta" Gobe dai in sha Allah zan raka ka dakinka Besty, ina farin cikin hakan, Allah ya nuna mana ya da matarka ce har aljanna"....


A'isha ta yi murmushi itama tana jin Adu'ar yayar tata, a hankali ta lumshe idannuwanta tana tunanin gobe, watau gobe idan da rai da lafia sai sun kafawa yayarsu tarihin da bata shirya ba, domin sai sun yi mata kwaliyar da bata taba yi a fuskarta ba, har fata take yi safia ta yi a yi ta ga yaya fuskar zata dawo, har aunawa take yi a zuciyarta shin yaya kwaliyar zata amshi yayarsu? Ta tabata wanda baya kwaliya idan ya yi yana yin kyau, to ama ita yayar tasu zata amince ne?.....haka dai kowa da irin zumudin dake zuciyarsa suka yi barcinsu sunna dan tsinkayo firar mahaifinsu dake ta murnar an yi murnar kyautarsu duda ba wani taka kara ta yi ta karya ba..............






Da safe kusan karfe tara Aba ya fice a gidan da nufin wucewa wajen daurin auren direct, Mama kuwa ta gama kimtsawa ama jira take yan matanta su gama hada kayansu su fita tare ita zata je da yan anguwa ne su kuwa zasu wuce wajen kwaliya ne




Karfe tara da minti arba'in da yan kai suka sauka a gidan Usaina da akwatin kayansu madaidaiciya mai dauke da suturun da zasu cenza suka ajiye kayan sunna kallon yadda dakin kwaliyar nata ya kawatu masha Allah kamar ba a kasar hausa ba, har sai da KAUSAR ta ji tana sha'awar malakar dakin kwaliya




Rukaya ce aka fara dandasawa kwaliyar, KAUSAR na kallo tana jin anya zata iya kuwa wannan hoda haka? Ana tsaka da yin kwaliyar ta lalubo wayarta gannin karfe goma ta gota sosai ta shiga gwada neman layin TAUFEEK tana tunanin zuwa yanzu ai ta yiwu har sun dawo gida dan karfe tara ne daurin auren


Kiran farko ba'a daga ba, sai a na biyu ne aka daga


Muryarsa a hankali, cike da kamala ya furta" Asalamu alaiki wa rahamatullah"


Cike da murmushi ta furta" Wa iyaka, Sanar min abin farin ciki Ango....."


A hankali ya yi dan murmushi yana dan tare hularsa da abokinsa amininsa kuma bakonsa ke son ja dan tsokana , ya ce" KAUSAR...."


KAUSAR ta yi dan tsai jin muryar nasa wata iri, a hankali ta ce" Lafiyarka kuwa? Ko kukan angwaye ka yi da aka daura?"


Murmushi ne ya subuce masa jin abinda ta fada, sai kuma muryar abokin nasa na fadin" Bani ita, KAUSAR yaya aka yi kika yi wannan rashin kirkin kika ki zuwa ki rakamu wajen daurin auren bestynki? Bestyn kennan? Gayanan yana ta kuka muna rike shi wai ango ne shi"


Yar dariya ce ta subuce mata tana zarro ido ta ce" Lah, ka zo? Na shiga ukuna yau da tsokana, ai ganinan na fi so in ya dawo na wuni inai masa nasiha sannan da ni za'a rakashi dakinsa danma kar ku cutar min shi"


Kasancewar sun saba dama, idan sun hadu ko a waya ne sai sun yi ta tsokanar junna sunaiwa junna neman rigima mai ban dariya shi yace shine bestyn TAUFEEK, ita tace yaushema ai shima ya sani ya kauce ya bata waje bata son rigima dai da sauransu , hakan ce yanzunma , tana ta murmushi ta ce" Gaskiya ni ka bashi wayar sai nake jinsa kamar a takure, me ka masa ne dan bana nan?"


TAUFEEK dake kallon titi direba na tuka su shi da Alhhusain ya yi murmurshi ya sake zubawa hanyar ido har suka karaso yana jin rikicin amininsa da aminiyarsa ya amshe wayar a tausashe ya ce" Ki tabata na ganki in ba haka ba ina iya yin fushi KAUSAR"


Zata bashi amsa ya katse kiran yana kallon kiran YUMNAH dake shigowa


Murmushi ya yi ya ki dagawa saboda sun karaso gida ne ana ta busa ana hayaniya kala kala idan yace zai daga ba zata ji shi ba sai ya soke wayar a aljihun rigarsa ta ciki a nutse ya ringa shiga jama'a murmushi kwonce a saman fuskarsa yana cikin shiga irin ta danyan yadi mai laushin gaske, wanda laushinsa ne zai nuna maka karkonsa da kudinsa a ido, mai dan duhun haske ama ya dauki zubi madaidaici a babar rigar, sai hula nutsatsiya mai yannayi da suturar jikinsa




Daria take yi bayan ta kashe ta yi ido hudu da Aisha


Haba ta dafe ta ce" Wannan abin na idannuwanki bakya ji ya maki rumf A'isha? Innalilahi wannan ni a titi ai ba zan shedaki ba, uw awara jarumar indian film dai wannan hanci an sake janshi haka?"


Aisha ta saki murmushi itama ta ce" Aunty saura ke taso ki ga a maki mu tafi kar a cinye miyar kari fa"


Kausar ta mike tana cire katon hijabinta ta karasa tana sake kallon kitson yadda aka boye shi a bayan daurin dan kwalin kamar ba kari ba, sai dai yadda ya malalu ai mai hankali dai ya san ba gashin bahaushe bane


Tana kallon Usaina dake hada kalolin hoda dan ta fitar da kalar fuskarta ta ce" Ama Usaina ni ba zaki saka min abin karin ba ko? Ni dai gaskiya kin ga wannan katon ribom din nake so nawa yake shi? Ni karin gashin nan sam bana so"


Usaina ta yi murmushi ta ce" Aunty, tsaya mu gama sai mu ga in ribom din zaki fi jin dadi a jikinki sai a saka shi, shima ai yanada girma sosai kuma kasa kasaa muke saka shi sai dauri ya hau kansa ya zauna, ama shi daurin da ake masa simple ne irin na zahrah buhari dai haka"


Ita dai sarautar Allah ta zubawa ido aka ringa juya fuskarta nan a juyo nan, ama ta ki a saka mata abin saman ido mai kalolin nan, sai dai sun ci karfimta gashin ido sai da suka saka mata madaidaici daidai da yannayin fuskarta, haka kuma jan bakin Nude ne aka saka mata ba mai karfi bane kuma ba'a yi mata barbada kumatu ba, kwaliyarta dai simple ce, kwalin nema ya so tsayar da su domin da kyar idon ya daina hawaye aka diga mata abin wanke cikin ido idon ya yi haske sosai sannan ta mike ta dauki nata lesh din itama ta zagaya baya dan sakawa domin sai ta saka za'a daura mata dan kwali


Hankali tashe ta yaye labulen dake karewa ta ce"
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”β€β€πŸ©Ήβ€β€πŸ©ΉπŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”β€β€πŸ©Ήβ€β€πŸ©ΉπŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 1️⃣2️⃣



LITATAFAN MARUBUCIYAR


Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicΓ©
Lait de nuit
Parfums dΓ©sodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*WaΙ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwaraiπŸ’ƒπŸ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuΙ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan MataπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ






Hankali tashe ta yaye labulen dake kare mai saka kaya ta fito tana fadin" A'isha wannan rigar fa? Ji fa yadda ta min daga nan?" Ta fadi nan din tana nuna wajen cinyoyinta irin yadda rigar ta dameta ta fitar da yannayin kirar jikinta


Ido da baki da hanci Usaina ta saki tana mamakin Kausar, kai subahanalah, da haka yannayin jikinta yake take fama da zumbulelen hijab kamar zata kifa? Haka yannayinta yake yanzunma ta zo da wata riga ne bubu zumbuleliya wace bata kama ko'ina na jikinta ba sai yawo take a ciki ashe ashe abinda ke kasa kennan? Su sunna yiwa Aisha kallon masha Allah mai manyan mazauna ashe ga wace tace kau bani waje, eh lalle Kausar tanada tumbi wanda da ace bayanta ba pankameme bane haka da tsaf zai iya zamewa matsala a kwaliyarta, sai dai yanzun haka kadan ne ake ganninsa sakamakon yannayin halitar da Allah ya yi mata, sosai suka taimaka suka rufe mata yannayin tumbinta saima su da suke bugon idannuwa


Nan fa aka shiga rikici, domin firr ta ja ta tsaya kan ba zata saka rigar nan ba, sai dai bata sani ba tsiya ce kannen nata suka shirya mata domin kaf kayan lesh din shine dama dama wanda ya dan rufe mata sutura


Tamkar zata yi kuka haka take sake maimaicin ba inda zata iya fita a haka, ba zata iya ba


Gannin rikicin na gaske ne Usaina ta je ta dauko wata alkyabarta baka mai shara shara, shara shara ne da ita sosai alkyabar dan yan mata ke yawan sakata sai yan gayun matan aure , itama irin shigarta kennan , Alkhyabar ba wani abu da take boyewa sai dai ta dan kare dai , sunna ne domin gwarama mayafi da ita , nan ta dawo tana budewa ta ce" Aunty, kin ga wannan alkyabar sabuwa ce sau daya tak na sakata in har zaki iya sakawa mu gama daurin ki saka ki ga zata rufe fa"


Kausar dake zaune ta harde hannu ta gama kutuntumawa Aisha da rukaya ashar sai huci take kan bafa zasu fitar da ita tsirara ba jiki a sanyaye ta ce" Usaina ni da a je a daukon sabon hijabina na sallah da muka yi sai na rufa, yaya zna rabaki da kayanki kumaa bayan wannan nauyi da muka dora maki?"


Usainar ta ce" Lah, aunty walahi ba wani maganar nauyi, kuma ba maganar aro tsakaninmu, kin ganta in dai zaki saka din ni zan ji dadi, yanzu yaushe aka koma aka dauko maki hijab aka dawo inace yanzu Mama ta gama fadan baku karaso ba?"


Shiru ta yi, du nauyi ya damu zuciyarta, haka aka daura mata daurin da ya idasa fitar da sirrin kwaliyar sannan ta saka alkyabar wace ita da kanta sai ta tsaya gaban madubin a hankali tana shafa yan kannanun walwalin gaban alkyabar farare karkar ba masu yawa ba tana gannin yadda alkyabar ta hau yannayin dinkin har kasa da irin yadda kwaliyar ta hau kalar fatarta tamkar ba ita ba


A hankali ta daga idannuwanta ta kalli kannenta da suka sakata a tsakiya sunna kallon madubin su dukansu


Wani ni'imtacen murmushi ne ya kwace mata a fuskarta a hankali ta ce" tabarikalah masha Allah"


Aisha ta saki murmushin itama a hankali ta ce" Tsarki ya tabaka ga ubangijin da ya halici samai da kasai da dukan halitun ciki, Aunty kwaliya tana maki kyau sosai haka dama?"


Rukaya ta yi murmushi itama a hankali ta ce" Tamkar ba aunty ba, kalli yadda ta yi? Inama Elhaji ya ga kwaliyar nan na tabata yau zai ce a daura aurenku"


Da yar dariya ta mintsini hannun Rukaya sannan suka juyo Usaina ta ringa kashe masu hotunna sunna faman fadin ta ajiye masu zasu zo su amsa a wanke a fitar masu tunda babu mai babar waya a cikinsu


Sai bayan sha biyu na rana suka fito daga gidan kwaliyar suka shiga adaidaita wace Rukaya da kyar ta samu waje dan wajen matse masu yake sai sun jijirga suk dauki hanyar gidan su TAUFEEK da akwatinsu


Sunna karasawa suka tarar gidan dinke da al'uma, babu kalar da babu tun daga tsofafi har zuwa yara kannana, kai yan matan dake gidan tamkar gida mai yan mata bayan yan matan gidan basu wani girma ba, yan matan cikin gidan ne dangi ne da ango dinsu na safe, sai dai ba irin lesh din su KAUSAR ba domin wannan su Mama ne suka yi shi iri guda sai makusantanta da ta ba ita da kanta, lesh ne mai daraja da tsadar gaske hakan ya sa har suka karasa bangaren Maman akan bisu da kallo ne ga tsararen kwaliyarsu ga lesh din jikinsu sai a yi tunanin wasu makusanta ne wa Hajia watau mahaifiyar TAUFEEK din


yinin biki kawai ake yi ba ji ba gani, biki irin na manya masu hannu da shunni


Kokarin dukawa take yi dan gaisar da Mama da ta nufota tana murmushi hakoran makarta biyu na walwali ta saka hannayenta ta tareta tana fadin" Oyoyo yarinyata, koda yake fada ya dace na rufe ki da shi, ama ba yanzu ba sai mun salami baki zan maki tass a gidan nan, zo maza ga abincin TAUFEEK dauki yana bangaren Hajia dan Allah kai masa ki dawo ku je da yan uwanki bangaren cen na amarya ku kai na baki ance zasu iso su yi gyaran dakinta dan yau za'a kawota"


Baban faranti mai dauke da kula biyu masu marfin kwalba rantsarsu ne Mama ta saka aka miko mata, a dan gagauce Maman ke bayanin dan yannayin taron kuma dama zata fita ne ta samu wanda ta yarda da shi ya kaiwa TAUFEEK abincin sai ga KAUSAR din, hakan ya sa ta juya da abincin su kuwa su A'isha suka bi bayan Maman domin ta ja su ne tana fadin" Ku zo ku kuwa yayana kafin ta dawo a shirya na bakin, ga mamanku cen a dakina da baki idan mun gama kwa gaisa"






A nutse take nufar hanyar bangaren Hajiar har ta karasa ta saka kafarta a hankali ta bude tana ta Adu'ar Allah ya kaita lafia domin takalmin kansa da take kai da kyar take rike kanta a sama, ga alkyaba ga kuma kwaliyar da take jin kunya kamar me wace tana ji a jikinta da wahala ta iya wuni da wannan hodar a fuskarta da sauransu


A hankali ta saka kanta falon tana yin salama




Jin salama ya saka Hajia dakatawa wace ke shirin shiga kicin sai fada take yi tana yadda hannun anma rainata a kan me za'a bar mata jika da yinwa har sha biyu? Lalle zata iya sabawa uwar Ι—an nan, shine fa zata shiga ta ga abinda zata sama masa koda danwake ne kafin a jima a bashi tuwo sai ta ji salama


Da farko furkar ta zubawa ido, sai kuma ta shiga binta tun daga kanta har zuwa inda ya fi tsole mata ido da sakata zarro ido kamar zasu fado kasa


Da sauri ta yi ribasss ta juyo ta karasa shigowa ta zo inda TAUFEEK kw zaune da Alhhusain sunna dan zantawa ta zauna daf da shi hadi da riko hannunsa na hagu ta jimko da bakinta ta shiga nuna masa abinda take ganni yau ra'ayne da ayne


Alhhusain ne ya amsa salamar a bayane sosai yana juyowa, sai kuma shima ya dan zarro ido kadan dan har ga Allah da farko bai gane fuskar ba da yannayin har sai da ta saki murmushi tana idasa shigowa gaba dayanta ta nufo falon bayan ta cire takalman ta ce" Ka ga abokin ango, menene nake gannin ka yi wani laushi ko yinwar ne kaima?"


Hajia ta saki hannun TAUFEEK da ya irin cire kan nan ya ki kula KAUSAR ko kallonta bai yi ba shi kam wai fushi yake yi sai yanzu zata zo aurensa dan wulakanci, ta tafa hannayenta tana tare gefen kuncinta ta hade da dan kunnen zinarin dake kunnenta ta ce" Na ga annabi in na yi hali na gari, yar nan Ke ce? Dama haka kike ama kike lumbukewa a hijabi bakya ko shafa fankeke? Lah ha ila ha ilalahu muhamadu rasululahi sallalahu alaihi Wa salam ku duba ku ga halitar ALLAH a yanke masha Allah kamar kamar lah kamar mema zan ce ke ama kina kokari haka kike tafia ras irin nawa.......?"




KAUSAR wani irin tsuru tsuru ta yi tana kallon Hajia, TAUFEEK ya zubawa hajia ido kafin ya juyo da dubansa dan gannin meye wai ya saka hajia magana haka?, Alhhusain kuwa sai ya mike ya amshi farantin dan yadda ta yi sai ya so bashi dariya ta yi tsuru tsuru kar ta saki abincinsu , shi da kansa mamaki ya kasa barinsa haka kuma idannuwansa sunna matukar son kare mata kallo duda ya san

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login