Showing 42001 words to 45000 words out of 186303 words

Chapter 15 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18771

dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃






Ajiyewar ta yi sannan ta juyo saman kujerar da yake zaune ta zuba masa ido
Murmushi ta saki a bayane ta rufe fuskarta da hannayenta biyu, domin idon da ya zuba mata sai da ta ji har kasan zuciyarta wani irin zirrrr mai kama da tashin tsigar jiki da kuma wani irin nauyin idannuwansa a fuskarta
Murmushi ya yi a hankali ya dan miko hannunsa kasa kasa ya ce" Zo "


Kamar jira take yi ta daga kafarta da sauri ta karasa ta fada jikinsa tana sake rufe fuskarta a kirjinsa ta saki ajiyar zuciya bayananiya


A hankali ya mayar da dayan hannunsa ya rungumeta a jikinsa shima nasa idannuwan a lumshe


Kasa kasa sosai ya ce" Na fa yi dati zaki gogi dati a kwaliyarki mai kyau"


Idannuwanta ta sake lumshewa a hankali ta ja numfashi kadan tana jin kanshin turaran jikinsa mai sanyin kanshi na shiga hancinta kasa kasa ta ce" Bana jin wani dati, Ya Taufeek i'm so happy today "


Hannunsa ya saka ya dago fuskarta ya zuba mata ido
Ya yi murmushi a hankali ya kai lalausan lebensa saman goshinta ya mana mata kisss din da ya sakata sake lumshe ido
Kasa kasa ya ce" Ina maki barka da shigowa rayuwana Yumnah, Allah ya bamu zaman lafiya"


"Amen ya rab" ta amsa ita dinma, sannan ta sake zubawa sajensa ido kamar ta sake rukunkume shi haka take ji


A nutse ya ce" Bara na koma"


Ido ta bude da sauri tarr ta dora saman fuskarsa
Ya koma? Ina?
Kasa hakuri ta yi gannin da gaske yake ta ce" Ama ina zaka je ne da daren nan Yah Taufeek?"


Da kula sosai ya ce" Ba zan kwana a nan ba sai an gama bukukuwa irin na al'adun nan, you see da kunya na ringa tsalake mutane ina shigowa kuma ina fita"




Wani irin makoko da dana sannin barin wadincen rubda rubdan rubabun banzan kwanar mata a yau ya sake shake mata wuya, innalilahi tafia zai yi ? Du irin wankin kwakwaluwar da ta sha na irin kulawar da zata bashi daga yau har karshen rayuwarta dan kar ya dubi kowace irin mace haka zasu wani wargaza mata niya? Wace ta yi mata gyara ta yi mata wankin ido mai matukar girma domin mahaifiyarta ta nemi hakan, an sakarwa matar kudi na mamaki da ya saka ta zage dantse ta yi mata dala dala cewar sai ta ki jikinra ta sakar masa jiki ta yadda babu wata banza da zata shiga zuciyarsa sama da ita, har fada mata ta yi kar ta saki dan tana budurwa tace zata masa raki, komai wahalar da zata sha ta jure ta mike kamar ba ita ba, kuma ta yiwa kanta alkawarin jurewar sai kawai yace zai kwana ba a nan ba?




Tana ji tana gani, mijinta ya yi mata salama bayan ya dauko ledojin da ta ajiye ya damka mata cewar na baki ne sannan ya fice ya nufi bangarensa cikin nutsuwa


Nan ta zubar da ledojin ta karasa saman shinfidarta da aka yane da farin abin shinfida mai tsada aka baza turaran girma da kannanun flowers masu kanshi sai daukan ido suke ta hau ta kwonta tana rintse idannuwanta hawaye suka shiga bin gefen kuncinta cike da bacin rai ta kasa koda komawa inda suke bale har ta wani kai masu abin ledar cen, hasalima itama yinwar take ji, ama wannan abu da ta shaka ya sa ta ji ta hakura da jin yinwar, ama da bakin naci sai da Basira ta tardota har nan tana faman tsokanarta cewa angon ya fice ya masu sai da safe ita kuma ta makale ko zumar soyaya aka lasa mata? Ta fito mana,
Cike da rashin walwala ta nuna mata cewar ta gaji ne barci take son tabawa ga sakon nan ta je masu da shi inji shi, ita ta kwonta sai da safe


Da wannan ta yi kwonciyarta ta barsu da surutu tsakaninsu da baje bajajar suka auna a tumbinsu sannan suka kama wajen kwonciya dan hutawa


A nutse ya karasa bangarensa


Kamar yadda yake jin har wani mintsininsa datin jikinsa ke yi direct bayi ua wuce da babaan tawul dinsa a kafadarsa bayan ya cire rigar jikinsa


Ya dauki lokaci a ciki sosai kafin ya fito a nutse ya karasa wajen wrdrn dinsa ya ciro jalabiya ya saka sannan ya saka gajeran wando ya karasa wajen salaya dan gabatar da shaf'i da wuturi


Yana gamawa falo ya koma da laptop dinsa, da kuma wayarsa baba sai dan abin rufa da ya janyo domin niyarsa a cen zai yi barcinsa, dan dole sai ya duba laptop din ya yi yan aiyuka masu mahimmanci sannan ya kwonta


A lokacin da ya zo dan cin abinci kamar wayarsa ta fado cikin ransa


Tsam ya yi yana tunanin inda ya sakata, domin gaba daya ya manta da ita a cikin kwakwaluwarsa


Rigarsa da ya cire har ya ajiye saman mashine din wanki ya koma ya lalube, sai dai babu


A hankali hoton wayar a hannun KHausar ya shiga dawo masa idannuwansa


Idannuwansa ya lumshe ya koma falon sannan ya dauki wayarsa baba ya saka numbar sekatarinsa ya yi kiransa
A nutse ya sanar masa cewa kar a tura sakon komai a karamar wayarsa ta fice a hannunsa
Sakatarin ya sanar masa cewa ba'a rigai aka tura wani baban sako ba, wanda aka tura na marar lafiyar nan da aka dauko daga kauye ne kawai, ana iya nunin an bacewa lamba idan yana so?


Dan shiru ya yi, kafin ua girgiza kai yana fadin kar a ce komai, sannan ya kashe wayar ya karasa wajen cin abincinsa ua zauna dan cika kulunsa




______________________________________




Washe gari da wuri wuri Khausar ta shirya ta fice a gidansu bayan babanta ya bata dari biyuntata nufi cen wajen da ake kafa sunnayen wa'inda zasu iya zuwa su amshi takardunsu da wajen da zasu amsar


Sai dai tunda ta je din hankalinta ya nemi rikicewa sakamakon rashin gannin sunnan TAUFEEK a layin wa'inda aka tabatar cewa sun samu din bayan ga sunnan du wani wanda ta ji ance ya samu ciki harfa ita


Takardar nan ta mata karantawa ta fi a irga har sai da ta fara shanye sunnayen dake laye ta hakura ta juyo gida ido sai zubar da ruwa yake tana tafe tamkar zata tashi sama, uwa uba yau din hijab din Mama nema ta saka du irin kwaliyar da aka sha jiya kamar ba a fuskarta ba fuska tana neman sinkime mata dan shiga rudani da tunanin me kennan?


Tana shigowa a lokacin har karfe goma na safe ta gota ta nemi waje ta shiga rusawa Mama kuka kan ai Besty fa da alama bai samu ba, dan bata ga sunnansa ba


Itama Maman hankalinta ya tashi gaskiya, dan harma ta rasa to me kennan?
Aisha ce ta ringa kwatanta masu to ko dai an mance ne, ana samun irin haka fa kar su yi hahawar rikicewa, ama ina Khausar kaffafuwa baje a tsakar gida kukanta take kashirban da kyarma ta iya cin maka yar murden da Aisha ta silala tana faman bin Aishar kan ta zo ga dari biyunta nan ta siyo kati a kireshi


Mama ne ta hanna hakan, cewarta jiya fa yake ango, kar su kireshi bata so
A dole Khausar ta hakura da maganar kiran, sai dai nata sunna da ta gani gaba daya zumudinta da farin cikinta suke neman bacewa bat, abinda ya fi damunta in har bai samu ba fa yaya zai ji? Yaya zasu yi? Sam ta manta fushin da take yi da shi, burinta ta ganshi su je su sake dubawa su ga ta inda zasu bilowa al'amarin


Kusan karfe biyar na yama sunna zaune su uki a tsakar gidan ya shigo bakinsa dauke da salama


Mama ce ta fara amsawa fiskarta wadace da fara'a tana sake rufe jikinta da hijab dinta sosai tana masa maraba da zuwa


Dukawa yayi kamar yadda ya saba ya gaishe da Mama sannan ya yi zamansa saman tabarmar da Aisha ta sake kabewa ba wani kyankyami ko wani dari dari yana duban kwanon dake gaban Kausar tana dibar awara ta kudinta na safe ya mika hannu ya ja gabansa shima ya shiga ci hankali kwonce a lokacin da Mama kuwa ta mike ta yi ciki dan bata cika zama idan sunna nan ba, ba dan komai ba sai dan akoy yan matan, a tare da su baki daya


Khausar ta nemi sake dauko rikicewar fuskarta tana kallonsa ta ce" Wai freind daga ina kake? Ka kuwa san tunda safe nake nan ina sheka kuka ina nemanka?"


Kumatunta da suka dauki abin man awara ya bi da kallo, sai kuma ya tabe baki kasa kasa ya ce" Haka fa, gashi kina dirkar awarama "


Awarar ta kalla, ta kalli hannunta, sai kuma ta kalli Aisha ta ce" Aisha, dan Allah ban yi kuka ba?, Awarar nanma da ka gani ji na yi juwa zata makani da kas ne na yi hakuri nake ci, ama ni dake cikin tashin hankali, zuwa fa na yi ban ga sunnanka ba , ka san me hakan ke nufi ai ko?"


Cikin halin ko in kula ya ce" Eh"


Hakan ya sa ta zuba masa ido, wani abu na dan mintsininta a zuciya, EH? EH fa yace ko?


A dan yannayin fusata ta ce" Eh?, Wani irin eh? Hakan fa na nufin baka samu ba ko kuwa an cinye maka ne, dan ai da aka fada an fada ka samu ko?"


Banza ya mata, maimakunma ya bata amsa sai ky din mota da ya mikawa aisha ya umarceta kan ta dauko ambulop a motar


Jim kadan ta dawo Lhausar ta cika yadda ka san an saka mata balan balan a kumatun an hura sai hararensa take yi, shi kuwa har awarar tata ya kama sai cinyewa yake yi ko damuwar abinda ta fada bai nuna ba


Ambulop din ya yiwa Aisha nuni da ta bata
Tana budewa ta ga takardarta, watau diplomanta ta kwalin bama ta takardar ba, wace in kana son amsarta bayan ka yi takarda ka ajiye sai ka yi jira har Allah ya fitar maka da ita, dan kuwa kai tsaye ba zaka je ka amsa ba, Bama wannan na, a yau aka kafa masu cewar suna iya amsa, hakan na nufin daga gobe masu hanya zasu iya zuwa su samu ta takardar, ya su ya su kuwa sai sun bi layi har layinsu ya iso, sai takardar dake nunin an nata damar zuwa koyon aiki a babar hospitall din garin har na tsayin wata uku da albashi du karshen wata na kudin abin hawa da abinci


Galala take rike da takardar baki da hanci da ido a bude a lokacin da Aisha le zuba masa ruwa yana wanke hannunsa sannan ya dauki piyawatan dake gefenta ya huda ya shiga sha hankali kwonce


A dan tsorace da shi ta ce" TAUFEEK? Me nake gani haka ne?"


Hannunsa ya dan daga mata har sai da ya kare ya wani lumshe ido kamar ya sadu da kaza lafiyayiya yankan hausa silalar murhu sannam ya dubeta a nutse ya ce" Ina cin abincin kike so na maki magana ko me?"


Khausar ta sake dubansa, sannan ta miko masa takardar kamar ba san meye ba tan kallonsa ta ce" Kalli fa, takardana ne, a in ka samo? Kalli Wannan fa, hospitall fa?"


Takardar ya amsa shima ya duba kamar bai san me aka rubuta ba, sannan ya kade tunanin ta hanyar dubanta ido cikin ido ya ce" Eh , Aba ne ya bani dazu, Khausar nima Allah ya nunan an amso min tawa haka, jibi rubutun yassss yasss masha ALLAH "


Dubansa take yi kamar bakon halita a gabanta, maganarsa da Hausa yake yi sai dai sam tana neman shige mata, ABA? eh lalle ta san mahaifinsa baban mutun ne mai dama sosai a duniya, sai dai haka kawai take ta tunanin ta yaya? Aban nan fa jiya ya yi taro na mamaki a gidansa, yau sai kawai ace ya amso mata takarda? Bayan wannanma to Aban ko dai yanada wani mukami a fannin asibiti ne? Ko tace siyasa ne? Dan abin ai kamar ya shafi baban wajen ilimin asibitin ne kai tsaye ba wai kasa kasa ba


"Rashin gannin sunnana ne ya saka shi dan bincikawa har cen, daga nan ne na fada masa a biyo da naki takardun" ya fada yana dauke dubansa a yannayinta, a zuciyarsa kuwa yana tunanin me kennan yake fada? Ya zauna yana fadin magangannun da gasunnan dai? Koda yake yana da hujarsa


Farin ciki ne ya mamaye gurbin wasi wasin da ta nemi shiga, harma ta dafa ta mike da dan gudu ta nufi dakin Mama tana fada mata abinda yake faruwa


Murmushi ya yi kasa kasa ya dauke dubansa a kanta ya maida kan wayarsa har Maman ta fito sai godiya take masa shi kuwa ya nuna a daina godiyar haka


Karshe dai kamar yadda ya saba share kafa haka ya yi zamansa , har sai da ya fito daga sallar magariba sannan ya shige mota da niyar tafiya
A lokacin ne da kula ya ce" Besty, ni jiya baki ga wayata karama ba?"


Khausar ta dan zarro ido, sai kuma ta ce" Lah, tana dakin Aba, bara na dauko maka, nama manta da muna fada da kai, yanzu tsakani da Allah Taufeek fada ne ka yi a titi da mutumen da kana ganninsa ba a cikin hayacinsa yake ba? Haba dan Allah wannan sam ai ba wani anfani, bai dace ba, gaskiya kar na kuma jin haka gaskiya"


Wasu hannayenta mundil mundil da take juyawa tana masa kashedi yake kallo, kafin ya tabe baki a ransa ya ayana' To Mama, ke da hajia ban san waye ya fi wani neman kaini bango ba'
A bayane kuwa sai ya yi murmushi yana kallonta har ta shige ciki




A lokacin da ta dauko wayar haka kawai ta samu kanta da dannanwa, daidai tana fitowa take karanta sakon dake saman wayar, sako ne kamar haka *ASALAMU ALAIKUM INSPECTOR, MUN DAUKO MATAR DA KA BADA DAMAR A KAWO ZAKAI MATA TIYATA WACE HAJIA KHADIJA TA KAWO MAGANAR TANA SON TALAFIN NAN TA KUNGIYAR TAIMAKO, MUN MATA GWAJE GWAJEN DA ZAKA TAMBAYA, MUNA JIRAN JIN RANAR DA ZAKA SAKA DA KUMA TREATEMENT DA ZAMU YI MATA KAFIN KA SHIGAR DA ITA DAKIN TIYATAR*




Message din take kallo kamar tana son sake aro yaren ABCD dan ta fara fahimtarsu kafin ta durmiya a duniyar yaren turanci uwa uba ta kai yaren dake saman wayar


A hankali ta dago daga dokin kofar gidan da take tsaye ta zuba idannuwanta a saman fuskarsa, a lokacin shi kuwa jikinsa ya bashi abinda ta gani, sai ya dauke dubansa ya yi alamun ita yake jiran nan


Dan juyowa ya yi da alamun a dan kagauce yake ya ce"










*ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA*


Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu.
Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu.
Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda.
Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500


bokiti 1litter.
Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba.
Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726


Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO*


💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔




*DA CIWO A ZUCIYATA*




💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 1️⃣7️⃣



LITATAFAN MARUBUCIYAR


Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login