Showing 69001 words to 72000 words out of 186303 words
kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Sunna cikin tashin hankalin wannan su su kadai a gida wani ya same su, domin tana cikin dakinta tana jan carbi wani yaro ya shigo yace ana salama da ita , da ta tambayi waye sai cewa ya yi wani ne wannan dake zuwa koda yaushe wajenta ne
Har ga Allah har gagawa take yi wajen mikewa daga saman salayarta ta cenza hijab da dan sauri ta leka ta sanarwa Mama sannan ta fito duda hasken gari ta fito hankali kwonce ta shiga duduba shi
Ai kam shi din ne, da farar jalabiya a jikinsa yana tsaye hannu daya goye a bayansa daya a cikin aljihunsa yana ta faman kada kai kamar wanda ransa ke bace
Da sasarfa ta gaishe shi bayan ta dan duka, sannan ta mike tsayinta tana kokarin yi masa bismillah kamar yadda suka saba idan ya zo wata mahaukaciyar mota ta nufo ta parker daf da tas har kamar zata gogi tasa
Irin tashin hankalin da ta ga ya shiga sai da cikinta ya so murdawa, a hankali ta mayar da hannunta da ta fitar dan yi masa bismillah zuwa cikin gidansu
Mata biyu ne suka fito, kamar yaya da kanwa haka
Wace ke taunar cingan din ce ta bude cikin motarsa daga gaba ta dauko wayarsa tana ci gaba da tauna cingan din ta danna wayar hannunta ta shiga amsawa kamar haka" Gamu gashi bobo, yanzu fada min yaya zan yi in kashe localisation din"
Daga dayan bangaren akai mata bayanin yadda zata kashe ainahin abinda ya basu damar gane inda ya zo daga fitowarsa daga gida bayan ta saka shi a kason kwana uku kennan
Tana kashewa ta juya wajen motar tasa ta maka wayar da jikin madubin motar, ji kake tartsatsa karar fashewar madubin motar kafin ta karaso inda yake tsaye mundil a gabanta jikinsa sai rawa yake sai wurna wurnatu yake kai kace in ya sha iska ya dauketa yana iya makata da kasa, domin ita dinma a ginne take koda bata kai Khausar din ba to fa ta kusa kaita ne dan ko a yannayinta ba siririyar mace bace
Kare masa kalo take yi tana taunar cingan din nan yana wani kas kas kas sannan ta juyo bangaren Khausar wace ke tsaye, ama kana ganninta ka ga wace ke shirye ta iya aukawa da gudu in ya kama dan kuwa abinda ya dakatar da ita ta yiwu maganar da yake yawan fada mata ne cewa shi din tsayayen namiji ne a gidansa da waje!
"Elhaji Mujaheed kennan, wai tsakaninka da Allah a tunaninka shikenan har ka sha bulus ? Kai yanzu a cikin kwakwaluwarka tunaninka nima irin sauran biyun cen ne da ka hade gida daya kake wulakantawa? Ai ina tunanin tun a lokacin da na ki ka hadeni gida daya da matanka ya dace ka san ni ba irinsu bace, ko nace tunda ka san me ka aura ya dace ka taka a hankali, kai yanzu har wani sankon dan daba ne a haka? Kai har dan jagaliya ne? Shine ka tarda babanmu kasuwa yana cinikin hatsinsa ka tayar masa da hankali a cikin jama'a kana masa ikirarin a min magana aure kace zaka yi ba ruwana a cikin maganar kuma gida daya zaka hadani da matar in ba haka ba daular da ake mora sanadinka tsaf tana iya tashi daga sunnanmu? To kai ai baka san da tsohuwar yar iska kake zaune ba sai yanzu, gidan nan da ka bada baka ga sai da aka baka nono ka sha ka kuka damuki abinda ka damuka ba kafin ka yi kyautarsa? Ai kyautar gida da ka yi tun kafin ka aure ni ne , a duniya muka watse ka bada kyauta dan ka yaba kuma sai da saurayina ya tabatar da sunnan gida sunnana ke sama kafin na yarda da kyauta ta zama tawa, kai yanzu kana tunanin dan kana da yan kudaden nan ka fini mutane ne ko wani haukan ke kada maka cewa kana iya kwace gida? Da nake ce maka daga ni ka rufe ka dauki maganar a tatsuniya kennan shine ka nufo wannan zaka kawo min mu jera??????" Ta fadi wannan din tana nuno Khausar wace idannuwanta suka yi waje tsabar tsoro da firgicin abinda yake faruwa, haka kuma kafin kace meye wannan an fara tsalakowa kallonsu, kuma an rasa mai cewa ufan domin fadan kamar mai digi ne da dadin kallo a lokacin har sai da matar nan ta nufota a tsayen da take bata ankara ba ta kama hijabinta ta aniya neman kwashe shi daga jikinta
Nan fa hankalinta ya idasa tashi, jikinta haka yake rawa tana rikewa matar na ja
Da karfi makociyarsu ta karaso ta aniya shiga tsakani haka yayar matar itama ta shiga
Karshe dai da kyar makota uku suka hanna wannan lamari da tuni ya rikita hankalin Khausar ya kuma so ya zauta tunaninta,
Tunda take, tunda ta malaki hankalin kanta a anguwar nan bata fito ba fan kwali ba, sai gashi a yai za'a cire mata hijabinta daya da ya fi sutura a jikinta domin a kasan ba wani abin a zo a gani bane dan kuwa zani ne kawai saman yar ficiciyar riga ta shan iska
"Au, fadan area zaku mayar da shi ko ku din danginta ne?" Matar ta fada da tarin rashin kunya tana harar makociyar Mama
Makociyar Mama da suke abin arziki sosai ta tareta tana fadin" Eh mu iyayenta ne, da komaima, babu abinda zai saka ki cire mata hijab a banza a wofi, mema ta maki ne yarinyar da ba komai take cewa ba? Shekarunta nawa a anguwar nan bata taba yi da kowa ba, haka a makaranta da tana yi da koda sau daya ne an sani, to koma menene ba zaki ci mata zarafi a gaban kartin maza ba, ku kuwa su Isuhu kunna tsaitsaye me kuke jira ku gama gani kafin ku tsawatar ku hanna a zo har anguwa a wulakanta yar gidan mamuda? Ai kam ba adalci a lamarinku dan na tabata da shine walahi sai inda karfinsa ya kare!"
Sai da ta yi wannan maganar ne kuma samarin suka shiga hargowar rabiyar fadan da yannayi irin na dabacin nan sunna nuna ko ta bari ko su far mata, tuni aka samu aka sake matsa Khausar hanyar gida, da lalube ta juya tana son bude gidan ta shige ta ga mahaifiyarta ta ja kofar ta fito domin ta kasa hakuri zuciyarta sai harbawa take cike da tsoron menene wannan din kuma
Da wani yannayi na yan daba matar nan ta karewa makociyar mama kallo a lokacin da Mamanma ta fito ta ce" Mama, kina jina? Zamu tafi, ama ba hakan na nufin zan kyale yarki bane innhar bata fita daga harkar wancen mutumen ba, da kika ganshi a cen mijina ne, a yanzu dai a gidansa nice ta uku, a cikinmu duka haka kirarmu take dan yana sin manyan mata, Mama nima mun hadu a yawon ta zubar da shi ne ya aureni , ya bamu gida ya bani mota, wannan fa zan iya ce maki zaku samu , sai dai in zaku iya jure hali irin nasa da kuma nawa, dan na rantse maki har saman gadonta yana iya kawo mace ya warwareta sala sala bale idan ya rainata, wulakanci kala kala da gori zata ringa gani a rayuwa dan baya auren yayan masu kudi sai ya nemi yayan talakawa ya wankesu tsaf ya amshi yar ko me ta je ta fada a gida sai dai a bata hakuri a dawo da ita, ga kuma nawa a gefe, dan da kika ganni a nan mama abin kunya ne a cikin kawaye ace wancen ba wada haushin ya karro min wata, babu abinda na rasa shima ya sani, in bama masifa ba shi fa halitar da zai gamsar da matan irinmuma bashi da ita ama haka yake aurowa ya halaka a gida, ai na fada maka ni da kai shege ka fasa Walahi sau dubu zaka hau mace sai na samu jikeken Kato mai sunna kato na kawar da ƙishirwa haka kuma mun riga mun zamewa junna karfen kafa dan ba kari ko uban wa ya yi maka tsaye nice nan na fada, in kuma kun yi gardama ku aura masa ita , ke ki yarda ki aure shi ki zo ki sameni ina nan ina jiranki dan sai na.........".........................
........
Kalaman da kunnayenta suka iya ji kennan ta samu ta karasa dakin Aba da gudu ta zube nan saman kujera ta rufe kanta da hijabinta tana rizgar kuka tamkar kanta zai rabe biyu
Wasa wasa Mama ta dauki minti talatin kafin take shigowa, ko tace take shigowa tare da Aba, wanda idannuwansa suka gama kadewa suka yi jajajir har hada hanya yake yi wajen karasawa inda Khausar din ke kwonce
Murya a tausashe bayan ya zauna ya ce" Kuka kike yi tun dazu? So kike yi ki hadawa kanki ciwo ne? Tashi mana autana, ya isa hakanan"
Tunda ta ji muryarsa a farko kukan ya tsaya , tana jin me ya fada ta fashe da wani kukan mai karfin gaske ta dago fuskarta da ta yi jajajir gashin idonta ya hade ya yi wani irin luhu luhu da shi ta zubawa Baba idon tana girgiza kai a raunane ta sake mayar da kanta ta dukunkune a cikin hijabinta cike da jin kunyar baban da kuma tarin kunyar kalaman da matar nan ta ringa fada a gaban su Mama wa'inda ita dai a kankin kanta tunda Allah ya haliceta babu inda ta tsaya ta ji kalamai mararsa da'a irin wadinnan, sam bata tare da mutane masu gurguwar yare, haka a anguwa bata shige shigen yaren mata masu sakin harshe sunna maganar mazajensu a bayane ba dan raha ba, shi yasa abin ya wani irin daketa ta kasa kallon kowa a dakin
Auta ne ya karasa ya zauna yana kama hijabin nata ya ce" Aunty, kin ga kuwa yadda aka musu? Aba fa ya je har gidan da ni yace to kar ya kuma gannin kafar kowa a gidanmu, in fada maki harda shi uncle din Aba yace ya rabaku kar ya kuma ji, kuma sai ki ringa yin kuka? Tunda Mama ta yi kiran Aba muka fito daga kasuwa muka zo fa"
A birkice ta dago, ta dubi Aba, har lebenta na rawa rawa ta ce" Aba, kar ya kuma zuwa? To wa zai aureni in bai zo ba Aba?"
Mama dake share hawaye a kofar dakin ta shigo kamar an sanyota ta zubawa Khausar ido
Muryarta a raunane ta ce" Ke? Kina da hankali kuwa?, Ko tunanin kin gaza samun mijin ya fara taba kwakwaluwarki ne? Kina nufin in akace ya zo ya aureki zaki iya yarda bayan duka kaf abinda kika gani kika kuma ji? Yau ba dan Allah ya sa ana mutunci da makota ba ai da sai sun gama wulakantaki tsaf sai dai ki mutu in mutuwa zaki yi dan kuwa da y'ar bariki ta hado ki fa Khausar!, Ke wai shekarunkima nawa ne? Ko hamsin ne da ke sai aka yi me? Ko mun mutu mun barki ke daya a gidan nan sai aka yi me? A kanmu farau ne? Ke ba yar bariki bace, ke ba mai wulakanta mazan bace, kadararki ce fa ta zo a haka kuma shikenan sai ki dauki ciwo mai tsanani ki sakawa zuciyarki? Khausar ina sane da halin da kike ciki na ki baki dama ne kar abin ya zama shirme ki kasa rike kanki a cikin gida, ama tunda haka ne ya isa haka, ya isa hakanan khausar, miji idan ya samu to in bai samu ba babu yadda zamu yi, abinda na sani daya ne tak shine idan kika wulakanta kanki ta hanyar bin maza kin cucemu kuma kin cuci kanki, ki ci gaba da kula da mutuncin kanki da namu har yadda Allah ya yi!"
Daga haka Maman ta yi gaba ta barsu da binta da Kallo, Baba ne ya tausasa muryarsa ya yi mata nasiha sosai , kafin shima ya tashi ya fice masalaci
Da raunin zuciya da komai ta karasa wajen salaya ta samu ta yi sallah sannan ta kwonta a nan har dare ya fara yi
Kiran da wayarta ke yi ya sakata laluba ido har yana rufe mata dan abinda ke ranta ta daga bayan ta ga sunnan mai kiran ta yi masa salama a sanyayen da yannayinta yake
Kasancewarsa mutun daya kwalin kwal dake saurin cenkar yannayinta, hakan ce ta kasance yanzunma, harma kamar ya mike ya fice daga cikin mutane ne ko menene muryarsa a tausashe ya ce" Me yake damunki? Dazu ance baki je aiki ba baki da lafiya, wht hpn?" Ya karashe hapn din yana gagawar dakatar da nurse din da ta shigo da nufin yin magana kan list din wani magani da aka rubuta za'a ba wani patient a asibitin, domin du a rikice suke tunda ya masu dirar ba zata sai guje guje suke dan kar ya kama su da wani laifin domin ya samu abinda ba daidai ba yana cikin fadan ne ya ce da su ohk tunda haka ne da shi suke maganar, kuma sun san me hakan ke nufi shine fa du suka rikice yana office din docter Ibrahim sunna maganar abinda yake faruwa a asibitin ne ya danna mata kira
Rabewa Nurse din ta yi kanta a kasa , shi kuwa ya saurara yana son jin amsa daga Khausar
A hankali ya furta" Khausar? Ko kin yi barci ne?"
Khausar ta lumshe idannuwanta, a hankali wasu zafafan hawaye suka shiga bin gurbin idannuwanta, muryarta a shake ta ce" Aa, ban yi ba"
"Kuka kike yi ne? " Ya fada a sanyayen da ya saka nurse din nan da mahaukacin mamaki satar kallonsa, domin tunda take bata taba jin dai ya yi doguwar fira da su ba in ba shafar aiki ya yi ba, ama kuma in ya kamaka da laifi a kan marar lafiya yadda ka san zai cinyeka danye haka yake damkarka, a ranta ta ayana' ta yiwu da Hajia yake' watau Mama, dan kuwa du duniya ita kadai ce suka san ko asibitin ta zo idan zai mata magana to fa a sanyaye muryarsa take, dan kuwa hajia kakarsa su caku be tace ba'a yi yace sai an yi, matarsa kuwa basu taba ganninta ba, basu san yaya mu'amalarsu take ba
"Rashin lafiyar ne yau ake yiwa kuka? Yayama aka yi baki da lafiya ama baki sanar min ba? Kin sha magani ne????" Ya sake fada a hankali sosai a kuma sanyaye sai dai kuma abin auna zafin zazabin jikin marar lafiya dake hannunsa ya masa riko mai karfin dake nunin da shiru shirun da yake yi ta yiwu wani abin ya hanna shi fido ainahin abinda ke ransa a irin wannan lokacin
" TAUFEEK, Mujaheed ne....." Sai kawai ta saki kukanta a raunane har tana dan dafe gaban kirjinta dake mata zafi.....dan sai ta ji inma bata fadawa TAUFEEK ba ai an gama cutarta, dole ya san damuwarta dan bata da amini abokin sirri sama da shi
A hankali ya lumshe idannuwansa da suke karra girmama bacin ransa, a saman lebensa ya maimaita sunnan yana hangen Mujaheed din a idannuwansa
Khausar ta dora da fadi " Babu irin abinda bai ce ba a tarayata da shi, har cewa ya yi idan ya aureni ba ni ba kai, haka na so masa biyaya dan aure akace darajar aure na gaba da komai kuma mijina zai zama wanda aljanata zata kasance karkashin kafafuwansa, TAUFEEK babu abinda ban gani ba na tijara a tarena da shi ama na sakawa raina zafin kishi ne idan dai na shiga gidansa ai shikenan, ashe ashe wani abin ke jirana a zamana da shi??????, Taufeek ya min aalkawarin karshen watan nan zai turo, dama shiru maganar bata motsa ba ashe ashe da abinda ke tare da shi? Yau matarsa tamkar zata zane ni, har hijabina ta kama zata cire min a kofar gida, ta zazageni tass a gaban su Mama da kyar aka rabani da ita, TAUFEEK ni na ga tashin hankali karshe dai yanzu baba ya min tsakani da shi wai kar ya kuma zuwa, kuma yanzun ko ya zan samo wani????"
Magangannunta babu wanda bai narka masa zuciya ba, a tarin tashin hankalin da take ji zai iya cewa a yanzu da take fada nasa babu wanda baya ji
Hankalinsa ne ya nemi tashi sosai
What????? Shine abinda zuciyarsa ke maimaita masa a matsayin tambaya
Mikewa ya yi daga zaunen ya nufi ficewa a office din dan sai ya ji ya masa kadan dan bacin rai
Sai da yya fito filin Allah ya iya budar bakinsa ya ce" Matarsa? Ta cire maki hijabin ne?"
......a tarin tambayoyin dake harshensa bai san dalilin da yasa wannan ta fi tsaye masa a ransa ba, ko dan ya san khausar da kafa kafa da mutuncin kai ne? Ya kuma san anguwarsu yadda ta tara tarin maza kala kala ne? Sai kawai ya ji ya fi son jin bayanin nan fiye da kowane
A hankali ta fitar da huci mai zafi ta ce" Sun dai dan ja ama su Maman Abdul Rahman suka rike, kai dai kokowa kamar tashin duniya sai da su isuhu suka kama fa...."
"Suka kama me?"ya fada a dan hanzarce har yana dan saka hannunsa cikin aljihun farar rigar dake jikinsa ya dan jimke hannun nasa yana sauraronta
Khausar