Showing 120001 words to 123000 words out of 186303 words
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 4๏ธโฃ6๏ธโฃ
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐๐
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐๐๐๐๐
' Matarsa bata da lafiya, cikine da ita? Wauh, masha ALLAH , to ama me yake nufi da yana tsoron Laifina ne? Bayan wannan a kan me zai rufeni ya yi tafiyarsa? Me yasa wai ya cika takura min da shigata bayan ina shigar kirki? Walahi TAUFEEK yana da damuwa, me yasa ya cika haka ne? Ni ga abinda nake nuna masa'
Kasancewar wayar da ya ajiye mata ba wani damunta ta yi ba, batama san yaya zata yi aiki da ita ba sai ta bar masa abinsa nan saman table din ta koma saman cafet ta zauna tana ta tunanin rayuwa da abinda ke zagaye da ita, tun tana iya rike yinwar dake kwakular hanjinta har ta ji kuwa na dibanta, a hankali ta silale ta yi kwonce ta yi matashi da hannunta tana lumshe idannuwanta da Adu'ar Allah ya sa aikin da zai yi ba mai daukan lokaci bane
A kala sun dauki awa bakwai, dan tun karfe tara na safe sai hudu da rabi na yama kunnayenta suka ringa tsinkayo mata alamun bude office din
A hankali ta bude idannuwanta da suka fada ta bi takun sawayensa da kallo har zuwa hannunsa mai dauke da wasu manyan ledoji biyu
Idannuwanta ne suka hango mata saukar rigarsa da sauri ta maida idannuwan nata ta rufe ta juya ta bada baya tana Turo baki cike da haushi da takaici
Sai da ya maida kayansa sannan ya dauko ledar mai abincin ya karaso inda take kwoncen nan a Nutse ya zuba mata ido
"Sai na tsumata iya tsumi, sai na bata tsumi ta yadda du wanda ya dauka zai san ya dauki mata, sai na......" Da sauri ya cire kansa a wajen da idannuwansa suka sauka yana a'uziya a kasan zuciyarsa sakamakon tuno magangannun HAJIA a lokacin da take bayanin KHausar din
A hankali ya ce" Tashi mana kin fa san na shigo ko?"
KHausar ta sake hade baki tana ji inama zata iya jan mahaukacin tsaki jama'a ko zai fahimci kololuwar bacin ran da take ciki, sai dai ta san ko firar arziki suke baya son tsaki , dan haka ta masa banza tana tunanin ta yadda zata iya mikewa ta je ta samu dan abin sakawa bakarta dan tana kyautata zaton tsaf take iya faduwa idan ta mike tsaye
Murmushi ya saki ya yi zaune , irin zaman nan na mike kafa, hankali kwonce ya fitar da manyan kwalayan pizza din da docter ta amso masa ya ajiye da jusss masu dadi ya ajiye , hankali kwonce ya bude guda , kanshin abin kaicop din da naman kazar nan da nan suka je hancinta, ba wata damuwa a tare da shi sai tarin sakewa kamar yadda ya saba, idan har yana tare da ita a inda take yana iya zama koda kuwa a dandar kasa ne ba tare da ya share wajen ya ko damu ba, shi dai tun bai iya cin awara da dambu ba itace ta koya masa kuma a leda a daure na arba'in da tarin yaji da mai, tun idan ya dandana yajin na goge masa lebe har ya zama ษan gari ya iya ci hankali kwonce, a yanzu haka yana fitowa kafin a fitar da wanda aka yiwa aikin ya da docter ta amso abinci, aiki yake yi ama ya san cikin Khausara na cen yana kugi
Hankali kwonce ya saka yar wukar ya fitar da gefe guda ya dauko a hannunsa ya dan sake yin wajen fuskarta da shi kanshin ya shigi hancinta da kyau sannan ya janye ya kai bakinsa ya cira yana lumshe ido da gangan kasa kasa ya furta" Dadihhhhh"
A zabure ta dago kanta , tun tana Hanna kanta juyowa har ta mike zaune idannuwanta a kan hannunsa da kuma kwalin pizzar
A hankali ta samu kanta da hadiyar yawu tana kallonsa , ta ga ya sake saka yar wukar ya yanko wani dan mitsil ta kai bakinsa
A hankali ta gyara zama ta tana kallon dayan kwalin, sai kuma ta kalle shi tana kai hannunta wajen kwalin
Murya a raunane ainun ta ce" TAUFEEK wancen nawa ne?"
Hannun nata ya riko ya dage daga saman kwalin kafin ya girgiza kai , na hannun nasa da ya ciro ya kawo wajen bakinta da shi yana kallonta ya ce" Wannan ne naki"
Pizzar ta karewa kallo, karama ce fa, to wannan ai ba haka take loma ba ita, ama kuma gudun kar ya cinye abinsa sai ta budi bakin ta amsa
Dan murmushi ya saki yana sake binta da kallo ya ciro wani irin wancen
Wannan karon ido ta zubawa pizzar sai kuma ta shiga takwaf takwaf da fuskarta ta Ce" TAUFEEK, ban fa karya ba na zo, kuma yanzu karfe biyar , dan Allah bani wancen din ko in je in samo wani abin in ci ni dai"
A ransa yake dariyarsa, dama ya san da wahala fushin ya yi nisa, dan haka ya miko mata
Hankali kwonce ta bude ta saki wani murmushi kafin ta mika hannu ta dauko jus din ta ta gyara zama a Nutse ta shiga cin abinta tana jin ruwan jikinta na dawowa, sai da ta kusa rabi ta dago dan yi masa maganar da ta fado mata a ranta, sai ta ga ita yake kallo da kwalbar jus dinsa a hannunsa, shi baima wani ci da yawa ba ya tsaya yana Binta da kallo
A hankali ta dan dauke kanta kasa kasa ta ce" Wai me yasa yanzu kake son daukan dabi'ar kallo bayan ba dabi'arka bace?"
Shiru ya yi mata, maimakun ya dauke duban nasa sai yake dan basarwa ama kuma yana sake dubanta
Gaba daya ta ji ta shiga hali na takura da wannan yannayi
Baki ta Turo ta dago ta zuba masa ido ta ce" Wai MEYE wai? Ni fa Bana son kallo ka fi kowa sani, kaima ai Inaga abinda ke cikin tsarinka ba kallo Ni ka daina kallona"
Murmushi ya yi ido cikin ido ya ce" Ina kiyaye duban abinda yake haramun a Wajena ne ai KHAUSAR"
Sai da ta ji tamkar ya gwaura mata mari ne
Da sauri ta so juya idannuwanta dan jin abin na neman fin karfinta, sai dai ta kasa tana kallonsa ta ce" Me yasa kake sha'awar gannin ka dagan hankali ne? Bama wannan ba MEYE yake damun Yumnah kace laifina ne? Kuma TAUFEEK dan Allah mu daidaita yadda zamu fuskanci su Aba kan maganar nan ka ji?"
Sai yanzu ya dauke dubansa a kanta, maimakun ya bata amsar tambayoyin nan sai ya mika hannu ya janyo dayar ledar ya bude yana ciro wani yadi mai nuni da hijab ne manya biyu, milk da baki
Bakin ya miko mata yana fadin" kin kuwa san wannan zai fi maki kyau?"
Hijab din ta amsa bayan ta tura wata pizzar a bakinta ta goge abin fulawar kadan ta bude hijab din tana kallonsa sannan ta dago tana kallon TAUFEEK din ta ce" Na MEYE wannan?"
TAUFEEK ya ce" Naki ne, na zuwa aiki "
KHausar ta tabe baki ta nade ta ajiye masa a gabansa ta ce" Ka ga Ni na kurce fita da ire irin Wadinnan ko aure na yi, dan rufe jiki ai ba dole sai da hijab ba, Larabawa hijab irin namu suke sakawa ne? Abaya ce da nikaf"
"Auren banda wanda aka miki yau kwana biyu?, Kuma larabawa kika ce, mu a nan ai sai da wannan ko KHausar?" Ya fada a tausashen da ya saba idan sunna musu
KHausar ta tsatsareshi da ido, sai kawai idannuwan nata suka fara cika da kwallah, gata dama da saurin zubo da su a gabansa, dan bata iya rike rauninta in dai a gabansa take
Muryata na neman shakewa hawayen na balewa tana dubansa ta ce" kai ba ruwanka da lokacin tsokana da lokacin da ba na tsokana ba, babu ruwanka TAUFEEK, haba dan Allah yaya ina maka tambaya kana jina ama sai ka ringa zagayewa? Dan Allah ka bani amsa".....
TAUFEEK ya dan dantse lebensa, hakan yannayinsa ne na rike kansa idan abu na neman daga masa hankali
A Nutse ya fuskanceta ya ce" Rashin lafiyar matata tace na zaba ko ke ko ita shi yasa take kwoncen"
Ido ta zarro tana dafe kirji ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, wayo ba shiga uku yarinyar nan ta ji wannan abin? Dama ta fara min abubuwa na raini ai yanzu sai ta yi da huja, dan Allah ina fata ka fada mata Bama za'a kai ga maganar zaba ba, itace uwar gida kuma amarya dan ko Ni ba zan bari ka mata kishiya ba!"
Dan murmushi ne ya yi na gefen baki kadan sannan ya mike yana ajiye mata jus din a nan ko sha bai yi ba, dama ya bude zai fara sha ne ta fara magana sai ya dakata
KHausar ta hade sauran pizzar tasa da Tata ta rufe ta mike tana daukan dan kwalin abayarta tana dubansa ta ce" TAUFEEK, yaya maganar yadda zamu fuskanci su......"
Bata san cewa ta kure masa waje ba, batama san cewa sunna iya yin daf da daf ba, sai dai ganni ta yi ya juyo sunna kusa da junna sosai ya saka idannuwansa a cikin nata a kausashe ya ce" Wannan maganar itace ta karshe da zan nanata maki, Ni ba fitsarare bane, ba zan iya duban Baba da Aba na musu rashin kunya ba, idan na yi hakan ba zan hadu da rahamar Ubangiji ba, dan iyaye ne, ko wa suka bani Ni din mai biyayya ne koda bana so, idan har ke wuyanki ya isa yanka, babu ruwanki da abinda za'a ce, babu ruwanki da abinda Allah zai miki ki je ki bijire in sun bani umarnin YANKEWA zan yanke, ama a yanzu sunnanki *MRS TAUFEEK KHAUSAR*, bana son maido maganar, KHausar bana son rigima , ki dauki hijab ษinki ki saka , kin ga wanda baya bin umarnin mijinsa wuta ce makomarsa ko?, Matata kuma zaki bata hakurin aurar mata miji da kika yi, ki je direbanki na jira ni sai na dauki Yumnah"
"lah ha ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahi alaihi Wa ahlihi wa salam, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, lah lah wayo Allahna cikina , na shiga uku , Taufeek haba TAUFEEK, wayo allahna......" Dawurwura take yi, idannuwanta na marmarmar tana neman wajen da zata zauna, kamarma wace ke jin gudawa a irin yadda take son zagaye, haka kuma ta kasa kuma dago kanta bale ta Dube shi, tsoro ne? Kunya ce? Mamaki ne? Koma menene kalamansa sun hadasa mata wani irin abu mai girman da ya hannata sakewa ko ta sake dubansa
A tsayen da yake binta yake yi da kallo har aka kuma neman izinin shigowa
Allon tvn haska camarar ya kuma duba , ,kafin ya karasa wajen hijabin ya dauka ya karasa inda take tsaye ba tare da ya jira cewarta ba ya zura mata hijabin bayan ya janye dan kwalin
A kaikaice ya dan bi wajen da ya fi komai birkita masa lissafi saboda rashin sirinsa a jikinta, kwarai ya ji haushinsa dan da hijab dinma ana ganninsa, ko dan hijab din mai rabar jiki ne irin hijaban yan matan zamani?
Fuskar hijabin ya gyara mata sosai bayan ya rike fuskar da hannu daya ya zamo ta kasa kwacewa , sai kuma ya sauke dubansa a kan lebunnanta dake rawa rawa tana kallon fuskarsa da sajensa
Dan murmushi ya yi, ya matse mata waje sosai ya rage amon muryarsa ainun ya ce" Kin san a kan shigar ki, ina iya toshe zuwa aikin nan, dan bana tunanin Akoy abinda zai iya daidaita bacin raina a kan hakan!"
Magana besty ke yi iskar bakinsa na dokan leben KHausar jama'a
Magana yake yi yana furuci kamar na yan giya jama'a
Shin shi din nan ina kunyarsa ta je ne?
TAUFEEK ne fa, kuma KHausar ce fa?๐ญ๐ญ๐ญkashhhhh
Wannan bayanai sunne suka fi komai daga mata hankali har ya cika ta ya bude kofar docter ya shigo dauke da hoto da dukan bayanai ya gaishe da TAUFEEK sannan ya zauna ya shiga masa bayanin dukkan abinda suka gani a tare da Yumnah sannan ya tabbatar masa cewa sunna iya zuwa gida dan YANZUN ba risq na zubewar cikin
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
*DA CIWO A ZUCIYATA*
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 4๏ธโฃ7๏ธโฃ
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐๐
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐๐๐๐๐
Sai da ya gama masa bayani ya masa godiya sosai tamkar ba shine gaba da shi ba sannan ya tafi
Yana tafiya KHausar ta karasa wajen da ta ga wayarta ta dauka ta juya ta nufi fita
Har ta kama kofar ta juyo tana huci ta sake dubansa sannan ta fice hijab din yana yi kamar zai tadeta dan ya mata yawa fa
Murmushi ya yi yana girgiza kansa, shi ya sa za'a sha rigima , bale irin yadda take tunanin ita ta haifi duniyar nan, ama ba komai Bara ya je gidan ya tarda wata rigimar kuma domin Mai kwanoni ya yi kiransa cewar ya yi kokari ya sauko da wuri Mahaifin Yumnah yace masa yana so zasu zauna
Dan murmushi ya sake yi ya dauki abin bukatarsa ya yi kiran vigil dinsa ya zo ya kwashe ya kai mota, ciki harda sauran pizzar da KHausar ta rage, jus din ko sha bata yi ba, ya san ba koshi ta yi ba kawai ya daga mata hankali, kai shima baya jin magana sam..........๐
A lokacin da suka karaso gida tuni magariba ta kawo kai, hakan ya sa ya taimaka mata ta sauka sannan ya wuce masalaci
Sai bayan sallar isha i suka dawo daga masallacin
Direct bangarensa suka nufa da mahaifinsa, a ransa yana mamakin to wai a nan iyayen na Yumnar suke ne ko me?
Mamaki bai idasa kamashi ba sai da suka shigo suka samu taron irin na asibiti, harda kishiyoyin Mama, wanda hakan ya matukar ba harta mai kwanoni mamaki, dan bai ga dalilin da za'a zo ana zama irin wannan a kan abinda ya isa da shi har ya yi yawa
Zaman kansa kaure biyu suka tarar, su su HAJIA Fatahiya sunna bangare guda da su Yumnah da mahaifiyarta, ita kuma Mama tana