Showing 141001 words to 144000 words out of 186303 words
yaji cike da basarwa ya ce" Kar ki koma ki tsaya ku gaisa da Husain"
Yana gama fada ya fice a falon gaba daya, ita kuma ta ja ta tsaya tana kallon kofar da ya fita kirjinta na bugawa da wani haushinsa da take ji wanda ta tabata na abinda ya mata da safe ne ba komai ba
Yana fita Yumnah ta koma sama da sauri ta Kunno nata turaran itama ta sauko da shi, tana shirin ajiyewa ta dauke na Khausar din suka shigo Taufeek a gaba shi a baya bakin Husain da salama
Idannuwan TAUFEEK ne suka sauka a kan kasakan turaran wutar, a ransa ya ayana'To fah'
Su duka suka Amsa, Khausar ta yi kamar bata ga abinda Yumnah ta yi ba ta maida dubanta kan Husaini tan murmushi ta ce" Yau dai ga Besty, yaushe a gari?"
Yumnah kuwa sai ta wuce dan kawo masa ruwa a lokacin da Husain ke fadin" Aa a yi haka? Hajia bestyn besty ai ba zaki gane Ni ba jiya kai a lulube ana kukan ba za'a zo gidanmu ba bayan mu din nan mun riga mun rike kuma sai hakuri"
Da dan mamaki ta dago dan kallonsa jin bayaninsa sai ta ga TAUFEEK na kallonta, shi kuma sam bai wani tsareta da kallo ba magana dai yake yi normal , danma sun saba ne a da ya zamto a yau ya dan tsokaneta, basu taba irin haka da Yumnah ba
Kasa cewa komai ta yi ta sada kai cike da jin nauyi
Yumnah ta ajiye masa jus ta koma saman kujerar dake dan kusa da TAUFEEK ta zauna hankalinta a kan mijinta tana jin Husaini na mata godiya, ama kuma bai bude ba ya dai dauka ya rike a hannunsa , ita kuma a ranta tana ayana' Ni da ke a ga wanda zai fi samun shiga a fadar TAUFEEK!'
(Shi fa wani son, Allah ne ke halitarsa a ran bawa, ba dan an cika kyau ko isa ko matsayi ba, a'a, wani son kai dan adam sai ka ga mema aka gani na so din ne? To halitta ce da Allah ke halitarwa ya kuma hada da wanda ya ga ya dace, Allah ka sa mu so domin ka, mu kuma ki domin ka)
[7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: ๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
*DA CIWO A ZUCIYATA*
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 5๏ธโฃ4๏ธโฃ
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐๐
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐๐๐๐๐
A sanyaye Mama ta ce" Ka san yanzun ko babu abinda ya daga mata hankali abin na tashi, dan dai bai kai na yau ba dan idan ya tashi da na bata maganinta ta samu barci yake wucewa shi yasa baka Sannin ya tashinma"
Hajia Nawarah dake zaune a ranta gani take yi harda rashin godiyar Allah a wajen mijin nata da matarsa da kuma dansa, , ita dai bata jima sosai tare da su ba ama ko ita ta san cewa zuwa yanzu ai shekarun Hajia sun kai wajen ciwace ciwace irin na girma masu zafin nan
da ace bata samun kulawama da tuni ta kwonce ai, dan dai ga kulawa, ko abincinta ba irin na kowa bane, jikanta ya dora doka ko tuwon laushi za'a tuka mata da irin abincin masu diabete ake yi mata, sigan bangarenta na masu diabete ne, kai komai da ka sani yana taka tsantsan da shi yana kuma hankalce da shi baya yarda ko da wasa ta yi wasa da lafiyarta, sannan a dole ta saba da sport rawata kaffafuwanta dan a lokacin da ya ga ya dace ya sakata tafiyar shine ke fitar da ita cikin anguwa da duku duku sunna tafe sunna fada har Mai kwanoni shima yake binsu dan wani lokaci har dariya suka bata ita kam a ranta ta ayana' Rai dai ana sonka sai an rabu da kai, du abinku Hajia ai yanzun tana hararan kabari, du kaunar ku da ita kuwa ba zaku hanna ba'
Hajia dake sauraron zancen itama ta budi baki a matsayinta Na matar gida dadadiyar da ta rigayi kowace ta ce" To Elhaji ciwon zamani sai an tankwaloshi, ana gudunsa yana bin mutun bale masu ciwon hawan jinnin nan an ce ba'a cika so sunna yawan fada ba, Allah dai ya ba Hajia lafiya baiwar Allah du ta yi wani iri"
Elhaji ya amsa da amen, ya maida dubansa kan TAUFEEK wanda bai furta masu koda A bane
Jim kadan nurse da ta je da kayan aune aunen jinnin Hajiar ta dawo da result
Bata tsaya ba ta shige ta kaiwa doctors da Khausar dake zaune daf da gadon Hajiar tana rike da hannunta daya tana tofa mata addu'a dayan kuwa yana ษauke da karin ruwan da doctors ya jona mata
Sunna gama gannin komai Doctor ya umarce su kan sunna iya tafia
Ya zamto shine karshen fitowa sai Khausar dake bayansa rike da wasu takardun da ya bata da kansa haka kuma kaf likitocin sun yi mamakin gaannin Khausar din da Hajia dan babu wanda ya san matarsa take haka kuma basu san ko members din family din Professeur din bace
Su Baba ya fara tsayawa ya kwontawa da hankalin cewa ta samu barci da sauki kamar yadda likitoci ke sanarwa wa'inda ba likitoci ba
Sannan ya dawo wajen da TAUFEEK ke tsaye daf da Mama ya amshi result din Hajiar ya mika masa sai ya dora da fadin" BP dinta ya yi kasa sosai ne, haka kuma sigan jikinta ya yi kasa fiye da misalin mai cuta irin nata, ga kuma ciwon kan da zazabi, mun saka mata maganinta na da wanda ya shafi siga din, ama na hawan jinnin na saka mata sabon treatement dan wancen din inaga ya fara sakin jikinta ne , zazzabin kuwa na saka karin ruwa da allurar saukar da ciwon kai da kuma na zazzabin wace zamu ringa saka mata du tsakanin awa shida, sai dan tari wanda in sha Allah shima zamu saka nasa maganin idan wannan ya daidaita, yanzu zamu ajiye nurse din da zata zauna kusa da ita dole wace zata ringa kula da hawan jinnin nata kowani lokaci har mu ga yannayin saukarsa, in sha Allah zata samu lafiya Sir "
Taufeek ya hadiyi dan yawun dake tsakanin harshensa da makogwaronsa , a hankali ya ce" Zan zauna da ita Doctor"
Doctor ya dan dube shi, dama ya san yakan iya cewa shi zai zauna da ita ama kuma nurse din da za'a saka ta zauna kusa da Itan anya zata iya aaikinta yada ya dace kuwa? Dan idan yana waje sukan rikice ne wani lokacin idan ana gudun kar a yi laifin nan ake aikata laifin ba'a sani ba, dan haka sai ya ce" I'm sorry prof da ka yi zamanka a office idan ya so sai komai ya ringa samunka a cen ko kuma ka ringa saukowa kana komawa dan likitar ta samu filin yin aikinta a nutse"
Khausar dake tsaye dan nesa da su rike da takardun ta budi baki a sanyaye duda ta san ba itace da ษaukan wannan decision din ba , ama sai ta kasa hanna kanta fadin" Doctor, Please zan zauna matsayin nurse din tare da prof in sha Allah "
Doctor ya dan kalleta da mamakin yadda ta iya fadin haka a gaban TAUFEEK kanta tsaye
Tashi daya ya nuna ba zata yi ba dan ba ita ta saba kulawa da ita ba
Shi da kansa likitan ya fadi haka ne dan baya so ta jawa kanta fada, dan likitocin ba sunne suke da ikon yin hakan ba, uwa uba Khausar ba likitar jinya bace takardarta ya wuce nan
A hankali Taufeek ya dakata daga nufin nufar wajen Baba ya juyo a dakensa ya ce" zata iya zaman , *SHE IS MY WIFE*" Daga nan ya karasa yana fadawa Baba cewar su je gida kawai shi yana nan , kuma sun san harkar asibitinsa ba'a zama a yi jinya, shi dai zai zauna Khausar kuwa zata yi jinyar, dan ya hada kan matansa su juya baya son rigima da hayaniya a kai
Likitan kuwa sosai ya yi mamakin jin Khausar matar Doctor ce, sai dai bai tsaya ya wani nuna mamakin nasa a fili ba ya yi gaba yana fadin " Madame bismillah mu je na baki dukkan abubuwan da ake mata da takardar "
Khausar kam tunda ya fadi cewa ita matarsa ce sai ta ji dama ba a gaban Doctor din ba tace zata zauna, sai ta ji kunya da nauyin su Mama da suka ji maganar, ta bi likita shina cike da jin nauyisa ta je ta amso magungunan
Ko da ta dawo ba kowa ta shige dakin ta kai komai ta ajiye ta juyo inda yake zaune rike da hannun Hajia yana kallonta
A nutse ta dauko kujera ta ajiye daf da shi a hankali ta samu kanta da dora hannunta saman nasu a hankali ta dan matsa nasan kadan sannan ya dan bubuga a hankali ta ce" in sha Allah, zata samu sauki, ka kwontar da hankalinka Please"
TAUFEEK ya juyo yana kallon fuskarta, a hankali ya dago hannunta ya kai gefen fuskar tasa ya shafa gefen fuskar nasa da hannunta na dama yana kallonta kasa kasa ya ce" Allah ya sa "
Daga nan Khausar ta yi shiru suka ci gaba da kula da Hajia da dukkan motsinta
Sosai take barci mai daษin gaske, sunna nan direba ya kawo suturar TAUFEEK wanda ya yi kira ya saka Yumnah ta dauko masa sannan ya fada mata ba sai ta zo ba dan ba barin jinya ake yi ba domin ta nuna tana son ta zo din itama ( wani lokacin, idan da rabo , mai hali irin na Yumnah na cenzawa idan ya samu abokin kwaikwayar halayar nasa mutun ne mai aikata aikinsa domin Allah ba dan a yabe shi ba ko dan ya saka dan uwan nasa jin haushi da kishinsa ba.)
Office dinsa ya je ya yi wanka ya cenza sannan ya shigo masu da abinci
Sallah kadai ke fidashi, Khausar kuwa tunda ta shige bata fito ba dan idan bayin ne akoy komai a ciki, kawai dai kayan jikinta take jin sun kai cenzawa dan kuwa ita rage acn nan ta yi sosai ta kuma kashe panka dan TAUFEEK har fifitu yake yi wai zafi ita kuma ta nuna tarin da Hajia ta fara in ta farka cikin sanyin nan da mura zata tashi,
A haka har aka fito daga sallar isha i, zuwa lokacin sosai jinnin Hajiya ya daidaita sai dai kasancewar bata farka daga barcin da take sha ba ba za'a iya tantance irin aikin da magungunan suka yi mata ba, ama ko a yannayin saukar numfashinta da sauki sosai
A hankali ya mike daga daf da Hajiar ya zubawa bayi ido
Kasa hanna kansa shiga ya yi a hankali ya bude ya shiga yana wani irin fatan da bai dace ya yishi ba a zuciyarsa a matsayinsa na abokin Khausarar Aba
Allah ya taimaketa tana tsaye tana alwallah ne, sai dai duda haka ta wanke pant dinta kennan ta shanya bayan ta yi wanka sama sama sannan ta yi bruch ta maida rigar da take yin datinta yanzun sosai a ranta guda ba wani dati da ta yi ta shiga yin alwallah hankali kwonce dan tunda take nan ta ga babu wanda ya shigo bale a ga paant dinta
Da sauri ta kai dubanta inda ya zubawa ido, a rikice ta kwalalo ido ta budi baki zata yi magana ya tako da saurin da bata yi zato ba ya janyota jikinsa lokaci daya ya dago kanta ya hade bakinsa da nata ya shiga kising cikin saurin da ya saka ta jan numfashinsa ta hadiye a huhunta sannan ya sake juyawa da ita ya hadeta jikin bangon nan a hankali hannunsa na damkar cinyarta ya ki bata damar kwace bakinta sai da ya gaji dan kansa sannan ya saketa yana fitar da numfashi da sauri da sauri ya janyota jikinsa ya sake rungumeta tsam har sai da ta kwontar da kanta dan dole a kirjin nasa tana sauke numfashi
A hankali ya dan yi kasa da bakinsa daf da kunnenta
Cikin kwarewa a aikinsa ya ringa sinsinar kunnen nata yana dan sauke hucin numfashinsa a nan, kasa kasa sosai ya ce" Ba'a magana a bayi, kin ga kin saka na maki abin nan da bakya so ko?"
Khausar ta dago da sauri ta zubawa fuskarsa ido, a rashin shiri ta ce" Kai TAUFEEK walahi da gangan ne ba gashi ba ka yi maganar ba?"
TAUFEEK ya dan zarro idannuwansa da hannunsa ya mata alamun ta yi shiru mana kafin ya nuna mata pampon wai ta yi abinda ya dameta tana yi
Ajiyar zuciya ta sauke ta koma ta bude ruwan ta daura alwallar tana kiyayewa kallonsa dan gudun kunyar dake nukurkusarta ta kayar da ita har ta gama cikin dabara ta janye pant dinta ta dauki hijab dinta ta nade shi a ciki da nufin in ta faki idonsa zata maido ta shanya ta yi gaba sai turo baki take yi ta bude bayin ta fito shi kuma yana baya yana kwasar ganima wa idannuwansa yana kashe kwarlwatar idonsa
Idannuwanta ta mutsitsika tana sake dubansa daga zaunen da ta kama ta zaunar da kanta da kanta ta sake rage girman idannuwanta tana dake tabatarwa kanta abinda take gani ta dauke kai ta ce" Uhum ikon Allah, dubun munafukai dai ta cika, dama karya fure take bata ya'ya, to Ni du wanda ya kuma min iskancin kukan baya son auren nan sai dai mu daku da ubansa koma waye, aikin banza a asibitin zaku shige bayi to uban mema kuka yi?"
Sai da cikin Khausar ya motsa, a rikice ta kalli magidanci wanda farin cikin gannin Hajiar zaune ya kasa barin fuskarsa da sauri ya zagayo Khausar ya karasa yana fadin" Yaushe kika tashi tawan?"
Hajia ta sakar masa harara tana leken Khausar ta ce" dole ai ka tambaya tunda kun sumar da Ni kun shige kun aikata aikin da ba shikenan ba, Allah dai ya sa ba a bayi zaka min jika ba kai marar hakurin tsiya, dilla dubaka kamar ba kaine ke min rashin daga a kan auren nan ba, to da mai kwanoni kake, sai ku kuncen abin nan mu je gida ka samu filin baje kolinka a mutunce kar ka haifon dan bayi ya ringa kantara min mari, ke kuwa kya karaso ko sai na taso na tardo ki, ashe haka halinki Khausara? Baki kamar agwaluma kina ihun bakya son auren magidanci shine zaku munafunceni a bayi bayan kun sumar da Ni?"
A rikice Khausar ta rarumi hijabinta gaba daya ta manta da pant din ta zurma hijab din ta karaso tana yadda hannayenta ta ce" Hajia, walahi walahi ba abinda kike zato bane, hasalima babu abinda ya hadani da shi gayanan ki tambayeshi Hajia"
TAUFEEK ya tabe baki yana mikewa ya ce" ai kuma sai ku yi" hankali kwonce ya karasa ya dauki pant din ya shiga ya shanya ya dawo ya zauna yana kada kafa Hajia na mitar su je gida ya dubeta ya ce" Ke kam wai wace irin mutum ce, kin farka zaki dagan hankali kuma ko? Babu inda zamu je sai kin warke sumul , kuma maganar tafia babu ita, dan babu inda zamu je kina rashin lafiya "
Hajia ta yi tsuru tsuru tana kallonsa, sai kuma ta kalli Khausar ta ce" Khausara kin gama sallar ne?"
Khausar ta juyo tana gyada kai
Hajia ta ce" Je aro mana waya ki amshi numbar mai kwanoni a wajen wancen mu buga masa waya kin ji? Ba da Ni ba wannan rashin kunyar tana tafe kana lekenta kuma bayan wannan Madina ai Garin Manzo in Allah ya taimakeni kasata a cen shikenan sai ka ki kaini dan son kai? Ni sai mun je bana "
A hankali suka zuba mata shi da Khausar din
A sanyaye ya tashi ya karasa bakin gadon ya zauna daf da ita ya kamo hannayenta yana dubanta ya ce" Dan kina son tafia gida ne zaki daga min hankali ko?"
Hajia ta sauke ajiyar zuciya, sosai jikan nata ke bata tausayi idan ta masa maganar mutuwarta ko me suke yi sai ya sakar, nan da nan ka ga ya zama wani iri, tamkar yaro karami ko kuma tamkar