Showing 138001 words to 141000 words out of 186303 words
a kanta tana saman salaya da farin carbinta tana ja
Kai ta sake sinewa tana jin wai ita da ina zata fara da abin kunyar nan jama'a? Ya karaso a hankali bayan ya dauko karamar wayarsa ya zauna daf da ita, bai ce mata komai ba ya janyo hannunta ya rike cikin nasa hakan ya sa ta sake sinne kai shi kuma ya ki yin magana har sai da ta gaji da kyar ta iya budar bakinta yana rawa rawa ta ce" Ina kwana"
Murmushi ya yi ya ki amsawa, sai da aka jima ya ce" Lafiya, "
Wajen ya sake daukan shiru, a hankali ta dan dago dan yin magana wayarsa ta katse mata maganar ya daga a tausashe ya yi salama a nutse ya gaisar da Mama ta hanyar fadin" Barka da safiya matar mai kwanoni"
Mama ta amsa shi ita dinma a nutse sannan ta ce" Dama, dan na ji ne idan da hali ka zo ka duba min Hajia da na zo gaishe da ita na sameta ba lafiya "
Wani irin firgita ya yi daga yannayinsa na nutsuwar nan yana wara idannuwansa da dan sauri ya ce" Hajiar? Me ya sameta? Ganinan zuwa"
Daga nan ya mike da gagawa yana fadin" Ina zuwa Hajia ce ba lafiya"
Mikewar ta yi itama ta take masa baya tana fadin " Subahanallah yaushe?"
Shi kam gaba daya magana ya kasa saima da ta tuna masa bai dauki abin dubata ba sannan ya nuna mata dakin nasa kan ta dauko dan sai ya kasa komawa saman
Da saurinta ta karasa bangaren Hajiar a lokacin TAUFEEK na zaune a saman kafet ya dora kan Hajia saman cinyarsa yana rike da hannunta daya cikin nasa yana tofa mata addu'a, gefe daya kuwa Baba ne ke kai kawo da carbi a hannunsa kana kallonsa zaka gane hankalinsa a kololuwar tashe yake, sai matansa biyu dayar na ba yaronta nono dayar kuwa tana zaune da carbinta a hannunta
Khausar ta shigo ta gaishe da kowa a jimulce daidai lokacin da Mama ta fito daga dakin na Hajia ta gyara shi tsaf ta dubi TAUFEEK da yan kurumcin suka tashi sakamakon ciwon Hajiar ta ce" yauwa dan gyara mu maidata ciki sai ka dubata "
Taufeek ya sake kallon fuskar Hajia, wace idannuwanta ke rufe a hankali ya dago ya kalli mamansa ya ce" *Mama*, ba zan iya barinta a nan ba , kin san da ba hutawa zata samu ta yi ba, bayan mai dauke da ciwo irin nata yana da bukatar hutu lokaci zuwa lokaci na kirki"
Mama ta gyada kai ta ce" To tashi mu kamata a je asibitin ko"
Ajiyar zuciya ya sauke ya sauke kanta a hankali yana kallon KHausar ya ce" Tana da diabete da kuma hawan jinni, nd tana da wani ciwon kai dake tasar mata lokaci zuwa lokaci"
A hankali Khausar dake gyara mata hijabinta ta gyada kanta ta gyara Mama ta karaso sosai suka kama Hajia wace kuwa ke kwasa idannuwanta kuwa a rufe saboda ciwon kai suka talabata ita da Khausar shi kuwa ya shige ciki dan daukar mata abubuwan da ya san bata rayuwa sai da su dan tana iya dawowa da zarar Allah ya sa ta dawo a hayacinta saboda su
Yana daukowa Baba na amsa ne har suka gama fidowa suka shiga Mota daya shi da TAUFEEK din suka nufi asibitin domin tuni su Mama sun yi gaba da direba
Sunna isawa ya tarda tuni an karbi Hajiar an rufu a kanta domin akoy litafinta a nan komai a rubuce da abinda ke kawota asibitin, shi suka fara aunawa sannan aka shiga wasu aune aunen dan haka sai ya samu waje ya yi tsaye kawai yake addu'a zuciyarsa na rawa ainun
Baba dake zaune shima kansa a dafe ya dago ya ce" Wai wani abu aka yi a gidan da ya daga mata hankali ne? Na ga ta jima rabonta da wannan ciwo?"
Mama ta juyo inda yake zaune, sosai take jin damuwarsu a zuciyarta, sai dai ita dinma a cikin damuwar take na ciwon Hajiar, domin Hajia ita uwa take a wajenta Bama sarakuwa ba, a sanyaye ta ce"
[7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: 💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 5️⃣2️⃣
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Da mamaki Alhusain ya ce" what? Babu abota tsakanin mace da namiji? Abokina ama baka da mutunci, ai kai ka yi?"
TAUFEEK ya kare masa kallo ya dauke kai yana duban abinda ake watsowa a tv ya ce" Haramun ne ai, kuma Ni ban ce abota nake yi ba ku kuka ce, man tashi mu je mu dawo mana kar na bar amana ita kadai"
Yanzun kam Alhusain rasa bakin magana ya yi, ya mike ya bi bayansa yana tunanin babu wanda ya raina shi kamar TAUFEEK, ama ba komai shi ya san in dai a kan lamarin Khausar babu wanda ya bari
Sosai TAUFEEK ya wuni cikin sukunin zuciya , sai da yama ta yi likis suka dawo Alhusain da niyar zai wuce ne karfe goma sha biyun dare zuwa kasarsu, dan haka suka yi da amininsa idan suka fito daga wajen su Hajia zai shiga ya yiwa su KHausar nasiha
Sun tafi wajen Mama ya yi mata salama, ta bashi sako ya kaiwa matarsa , daga nan ya yiwa su Hajia salama wa'inda suke falo sunna kallo
Sunna fitowa suka yi bangaren Hajia , wace ke zaune tana gyaran asuwakinta
Sosai suka taba fira ta dauko masa turaran wuta na jiji tari guda ta bashi tana kallonsa ta ce" Kai ashe mace daya ce da kai ko? Ka ga raba biyu kawon rabi kai mata rabi, da su biyu ne sai ka kai mata su raba ama daya kwal uwa rai ina Ni ina dumbuza wannan turare mai albarka?"
TAUFEEK ya karbe yana sakar mata harara ya ce" Bani nan, ke kam Hajia ban san yaya zan yi da ke ba, sai an kai mata dukan , wannan abin mai kauri mema zai yi da shi amshi abinki!"
Alhusain ya rike yana girgiza kai ya ce" Turaran Hajiar ne mai kauri? Ni tunda nake na taba jin turare mai albarka irin wannan? Kanshinsa fa in ya shafi suturarka har a wanke yana nan daram babu inda yake zuwa bani ina son abina"
Hajia ta wani saki murmushi tana kallon Alhusain ta ce" ka ji na Allah mai fadin abu domin ALLAH, kai shima fa sunnan an masa auren ne dazu da na kaiwa Khausara tuwon kari ras ta zo ta ansa ta shaki tuwona , haushi yadda ka san in dagawa magidanci nono kowama ya huta, wannan mugun hali da me ya yi kama, a baka y'ar a wanke tasss a gyare tana kanshi tana MUSMUS komai a wadace yana aiki irin wanda basa jin tsoron Allah, ka masa nasiha in kuma bashi da lafiya ne a sanar min in tashi tsaye dan da ka ga magidanci gaba da baya makiya ne da shi, matan uban nan kamar su kashe shi suke ji, kar su harbi lafiyarshi in shiga uku!"
Fada take yi tamkar ta ari baki, Alhusain kunya da dariya kamar su kashe shi kansa a kasa ya dantse lebe, TAUFEEK kuwa ya zuba mata ido yana kallo kamar wata sabon gani sai da ta dasa Aya ta sakar masu ledar turaran jijin tana turo baki hadi da gyara hijabinta
TAUFEEK ya girgiza kai cike da haushi ya ce" idan na kuma gannin kafarki a bangarena tabas sai na san yada na yi da ke, ke kam Hajia sai addu'a kuma, kar na kuma ganninki a wajena dan tsaf kike iya zige min mata , ku ji hijab har kasa kamar wata Malama , kuma da yake cewa turaranki dadi yana nufin kaurinsa idan kika turarawa mutun har ya yi wanki basa fita Ni koma kar ki biyo mu meye kike saka takalmi?"
Alhusain ya zarro ido yana fadin" kai da Maman Baba kake? Lalle baka da kunya, kuma bestyn kake kira matarka a gaban Hajia? Sai ta bi mu ai nasiha zamu yiwa matanka nasiha kuma da manya ta fi , mutumen kawai Hajia ai babu malamin da ya kaita kake wani yi mata rashin kunya"
Hajia ta ce" Gaya masa, gaya masa dan nan, Ni banma san me na masa ba da magaribar nan yace ba zan bi shi ba, wai kar na je bangarensa ai dole na je yaron nan ko dan na ringa masu nasiha, wai Khausarar ce yace matarsa? Nan fa yace min na masa auren dole Ni na manta ban fada mata ba dazun na taho mu je in sanar mata yanzu"
Wani irin cin birki TAUFEEK ya yi ya dawo yana nuna mata falonta ya ce" Koma, koma kin ji? Je ki cikin dakin in je in dawo , koma hajiata kar a shiga tsakanina da ke yan uba su ci galaba a kanmu, Ni fadan nan da muke yi ma gwara ki mana turare ta yiwu ba kalau ba"
Hajia ta yi ram da hannunsa ta ce" Kaima ka fara tunanin ba kalau ba ko? Ku je zan zo da safe in mana turare dan gaskiya bana tunanin ko lafiya ku je, Husaini na gambo Allah ya sa a sauka a jirgi lafiya ka saka hular sanyi saboda mura ka kuma tabatar ka yi addu'a ka ji? A kuma ringa yin jijin nan dan yana maganin iska sosai"
Alhusain a dole ya ringa dariya harda zama yana tsokanar Taufeek
TAUFEEK ya yi murmushi ya yi gaba yana fadin" Maragaici in ka gama ka sameni "
Alhusain ya daga murya yana fadin" ko Hajia bata fada ba Ni zan fada mata auren dole aka maku!"
Murmushi ya yi ya karasa bangarensa, shi kuma Alhusain maimakun ya mike ya bi shi su shiga ƙafarsa ƙafarsa sai ya yi zamansa saman kujera fara wajen shukoki kasancewar akoy hasken fitila ya dannawa matarsa kira wace idan suka fara fira ya tabata ba zasu gama da wuri ba bale ta san zai taso in an jima ta kama tambayarsa me yake so me zata masa da sauransu dan ba zai shiga ƙafarsa kafar aminin nasa ba bai san me zasu tarda ba, ko ba komai gidan mutun mai aure ba'a shiga kai tsaye haka ba
A lokacin da TAUFEEK ya tura falon ya shigo sai da ya dan zubawa falon ido ya lalubo wajen kunna fitila ya kunna
Falon ya karewa kallo sai kuma ya dan gyada kai, lalle an taba matar gidan, watau yau fitilarma Hajia Yumna bata kunna ba bale a yi tunanin tardo kanshi ko wata tarba irin nata ( masha ALLAH, ya zamto ko yayane mace idan mijinki ya zo ya samu wani yannayin da bai saba gani ba ya gane, ama ba a hade masa tunani ba kulun gidansa a hargitse kamar juji baya gane fari bale baki, du iya shegen Yumnah mijinta ya gane yau matarsa a sama take dan takan saka kanshi ta kuma girka koda na cikinta kadai ne)
Haurawa ya yi ya fada dakinsa ya shige bayi direct bayan ya ajiye karamar wayarsa, gaba daya yau bai dauki babar ba, dan kuwa koda yace masu na zai fita aiki ko kasuwa ba ya san sunna iya nemansa, Alhusain kuwa ya san ba zai shigo ba sai ya tabo shi dan haka suke yiwa junna , dabi'arsu ne, hasalima du tsakaninsu bai fi a irga ba suka shiga falon junna, sukan hadewarsu su sha firarsu ne a waje idan sun zo inda iyalansu suke basa sakin kari a yi ta zuba shirme ba kamun kan nan na wasu abokan mijin
A nutse ya yi wanka sosai da sabulun wankansa na ruwa mai sanyin kanshi sannan ya fito da tawul yana jin dakin nasa wani iri dan yau bai samu turaren wuta ba,
Wani yadi ya fitar mai tsari marar hayaniya ya saka a saman kannanun kayansa tamkar wanda zai fita anguwa sannan ya samu turare ya fesa sosai yadda ya saba kafin ya fito a nutse ya fara shiga dakin Yumnah da salama
Bakin gadonta ya sameta rike da kofin kwalba cike da madara da nido sai dan karamin cokali tana sha
Tunda ta amsa salamarsa ta kalle shi sau daya bata kuma kallonsa ba ta maida kanta cikin abinda take sha gabanta na dokawa hankalinta na neman tashi
Dan murmushi ya saki ya karasa bakin gadon ya zauna ya sake dubanta a tausashe ya ce" Ina yini Yumnahna"
Yumnah ta lumshe idannuwanta hawaye ya bale mata, a hankali ta fashe da kuka
Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya janyota jikinsa ya rungumeta yana taping din bayanta kadan kadan, a hankali ya furta" Its ok Yumnah, ya isa haka kin ji?"
Yumnah ta ringa sauke ajiyar zuciya tana jin yadda kirjinta ke dokawa
Ya rab shin yaya zata yi da ranta? Ta yiwu a ga laifinta, tana yiwuwa a ki yi mata uzuri, sai dai ba zata iya ba kowa hakuri a kan abinda take ji ba, ita ta san ba laifi take aikatawa ba, kuma mijinta ya isa ta yi kishinsa
A sanyaye sosai ta furta" yayanmu....., Na kasa hakura, yaya zan yi in iya hakura?"
Sosai ya ji tausayinta ya kama shi, a tausashe ya cirota a jikinsa ya kama hannayenta yana kallonta ya ce " babu abinda zai kusanta ki da samun nutsuwar zuciya irin addu'a, sannan idan har bakya so ku zauna a waje daya kina da ikon zaba domin Musulunci ya zo mana cewa sai idan mace na so a hadata da abokiyar ZAMANTA ake haɗawa ......"
Da dan sauri ta kure lebensa da kallo, lokaci daya take ta tunanin maganarsa, hakan na nufin a fida Khausar daga wannan gidan da wannan banzar kakar rasa take ita a barta daga ita sai Hajia tana hannata rawar gaban hantsi? Ba zai yiwu ba, idanma Khausar ta yi nesa kennan ba ranar rabuwa tsakaninta da mijinta? Ba zai yiwu ba!
A hankali ta girgiza kanta ta ce" Ka barta a nan, kar a kaita ko'ina ta zauna a nan din"
TAUFEEK ya dan zubawa yannayinta ido, sai kuma ya dan lumshe idannuwansa yana rike da hannun nata ya ce" Shikenan, ama ina so ki kwontar da hankalinki ko dan abinda yake tare da ake, idan kin ji hankalinki zai tashi kuwa ki yi ta yin addu'a in sha Allah zaki ji sauki a ranki, Yumnah ban karra aure dan bana son ki ba believe me"
"Yayanmu, ka karra aure ko aka aura maka ita? Ka daina cewa ka karra, ka daina ɗorawa kanka abin nan Please" Yumnah ta fada tana sake duban fuskarsa
TAUFEEK ya zuba mata ido, yannayin na so ya fara damunsa fa, gaba daya kamar wace bata gane yarensa
A nutse ya saki hannunta ya mike ya karasa wajen tufafinta ya dauko mata hijab baba ya karaso ya mika mata
Amsa ta yi ta saka tana jiran karin bayani dan ta san ta yiwu fita zasu yi sai ta ji ya ce" *NI NE NA KARRA AURENA, BA AUREN DOLE KO NA HADI AKA YI MIN BA, MU JE HUSAIN ZAI MAKU SALAMA*"
Tamkar ya caka mata mashi ta ji a kirjinta
A raunane ta bi bayansa da kallo har ya karasa ya bude zai fita ta ji karrar bude kofar dakin da take kyautata zaton na Khausar din ne, dan haka da sauri ta taho ta riko hannunsa cikin nata harda rabun masa a Jikinsa a lokacin da suke bayyana a gaban Khausar wace ta fito hannunta rike da kaskon turaran wutar da ta sakawa dakinta bayan ya kama sosai ta ji tana ra'ayin sakawa a falon sai ta zuba wadatace ta dora hijab saman doguwar rigar yadi mai santsi dake jikinta ta fito dan kaiwa falon idannuwanta suka sauka a kansu
Wani irin abu ta ji ya caki makogwaronta, a hankali ta bi talabar da TAUFEEK ya yiwa Yumnah da kallo kafin ta dauke kanta tana tabe baki wanda tabe bakin tsaf a cikin idannuwansa ta juya bata ce masu ufan ba ta fara yin gaba a nutse ya sauka kasa turaran wutar nan na tashi ta karasa falon ta ajiye ta juya da nufin komawa sama TAUFEEK da ya hanna kansa Binta da kallo ta karfi da