Showing 174001 words to 177000 words out of 186303 words

Chapter 59 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18756

test "


Da sauri ya juyo daga barin HAJIA dake son karbe hantar ya zubawa Mama ido, itama KHausar sai ta samu kanta da zubama Mama ido jin abinda Maman ta ce, ita kuma Mama sai ta mike tana alamun tafiya zata yi


HAJIA ta mike ta karbi plate din tana fadin" Yau ga bakin ciki, sai na ci, ke minene shi prcy taste din?"


Mama ta yi turus , ta juyo ta zubawa HAJIA ido, gannin itama amsa take so sai ta dan sosa goshinta ta ce" Dama, Mamansu KHausar ce ta yi kirana dazu tace juwar nan ta KHausar a duba ta yiwu wata kama ce"


"Ki rantse da huwa rahamanu, Kina nufin Juwar da y'ar nan ke yi ko sati bata cika a gidan nan a matsayin matar MAGIDANCI juwar ciki ce? La'ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam, wayo Ni Dije Allah na gode maka , ke ama tsaya yo wani irin ciki kuma? A irgena ai ta yi wata bakwai a gidan nan ga ciki shafe kamar nawa ? Ke dan mike dan mutun ai ya fi karfin kwonciya a mara ko? Dan mike in gani , kar dai yar nan irin matan nan ne da ciki ke shigewa nono da duwawu, tashi in gani sun karu ne ko mene? Yau na ga ikon Allah Ni Dije, yanzu ciki ne da ke?" HAJIA ke fada tana salalami, Mama ta yi saurin ficewa ya zamto sai TAUFEEK din da KHausar da HAJIA, sunna bin hajiar da kallo tamkar bakuwar halitta


TAUFEEK ya lumshe idannuwansa da kyar, a hankali ya ce" HAJIA barta dan Allah kar ki dagata da karfi mana kin ce a cinya in fa kika daki kan dan ko yar a cinyar nata?"


HAJIA ta saki KHausar ta dan matsa daf da shi ta ce" Kuma fa hakane, to ama kai likita ita likita karatun jabo ne kuka karanta da zaka dirkawa yar mutane ciki ana ce min juwa take? Wannan ai wulakanci ne, Magidanci ka yiwa Allah ka tashi mu je a tabbatar min da cikin nan ko na iya rintsawa, wayo Allah mai alheri ashe ashe abin a kusa yake, kai ana iya shege kace na maka auren dole?"


A raunane ya sake duban HAJIA a fizge ya ce" Tashi ki je bangarenki kin ji kakata?"


HAJIA ta sakar masa harara ta dauke kai ta ce" Aikin birit in ji tusa ai ko tsohon mutun yau ba zai rabani da KHausara ba, kin ga cinye hantar kin ji? Baiwar Allah ashe yan kwadayin da na fara tsorata na ALKHAIRI ne?, In me ta sameni ina ci yar nan sai ta ci shi har na fara tsorata ashe ashe ashe asusun Magidanci ke habaka? Ka tashi mu je!" Ta idasa fada da dan karfi tana wartar kaskon wutar nan ta ce" Bari in kai raushin in zo, dauko mata sutura mu je!"


HAJIA na fita ya samu ya kamo hannayenta yana sake tsatsareta da ido
A hankali ya ce," Dan Allah fada min haka ne? Are you pregnant?, KHausar tunda muka zama abu daya da kwana uku kika fara juwar nan, tl me please Akoy babyna a nan?"


Cike da kunya KHausar ta sada kanta tana janye hannunta , gaba daya ta shiga a halin rudu


Taufeek ya sake janyota jikinsa sosai yana dage rigarta a tausashe ya ce" Kar ki sako kunyar nan yanzu, na fi so na gane eh ne ko a'a? Ina son ganewa"


Ajiyar zuciya ta sauke, ta rasa ita amsar da zata bashi, abinda ta sani shine kwarai lokuta da dama idan mahaifiyarta ta tsananta juwa kwanaki ฦ™alilan tsakani zata tashi da nakuda ne, ama shin itama irinta ne ko yayane?, Ita dai bata sani ba, kuma shima ta tabbata ya shiga rudani ne na tunanin maganar nan, ko dan shi din likitan kwakwaluwa ne ba na mata ba? Ama koda likitan kwakwaluwa ne yanada wasu sani a fanin matan, shine zai fada mata ai ba ita ba,


A sanyaye bayan ta kama hannun nasa itama ta ce" TAUFEEK ban sani ba, ban sani ba, Ni dai na san ina juwa, ina cin abinci fiye da da, wani lokacin kuma nakan ji gajiya sosai ama da zarar na yi barci Shikenan sai ka ga komai ya wuce"


Zai kuma yin magana wayarsa ta ringa ringing sosai a dole ya dauko ya daga bayan ya ga mamansa ne


Da wata Muryar da maman bata cika amfani da ita ba ta ce" TAUFEEK dama Yumnah nakuda take yi tunda yama ban sani ba?"


A hankali ya samu kansa da lumshe ido, a Nutse ya ce" Nakuda?, Ban je part dinta ba , tana wajenku ne?"


Mama ta furzar da hucin bacin rai , ta cire hijab dinta ta ce" Ni na isa na san abinda take ciki ko na kai matsayin sani? TAUFEEK ace ina cikin gidan nan da raina da lafiyata ka auro macen da zata raina Ni? Tun ban yarda na furta ba har ta kaini makura? Ni makiyiyarta ce ko bata san girman mahaifiyarta ba da zata raina Ni?, Ace ina cikin gidan nan jikinta ya motsa na abin dake cikinta wanda nake cikin zumudin zuwansa duniya nake siye siye dominsa nake addu'a ba dare ba rana kan Allah ya nuna min, sai yanzu HAJIA nawarah ta shigo ta fada min cewa wai tunda yama sunna tare da mahaifiyar Yumnah a bangarenta tana kan gwuiwa YANZUN dai jikin ya motsa sosai ta yiwu haihuwar ce in sanar maka zasu tafi asibiti? Na nuna a kan me ba'a sanar min ba tace wai Yumnar ce bata so KHausar ta san tana nakuda sai dai ta ganta da abinda ta haifa? Wannan wace irin masifafiyar nataciyar gaba ce yarinyar nan ke fama da ita a ranta tana tare da yan zuga?, To bari ka ji, ina fatan matarka ta sauka lafiya, ama ka sani na kai makura , tunda har Ni Khadija ban isa da ita ba ba laifi Allah ya raya , ama Nima babu ruwana da dukkan abinda ya shafeta , ciki harda abinda zata haifa!"


Daga haka Mama ta katse kiranta ta jefar da wayar ta yi zaune a bakin gadonta tana dafe kanta wasu hawaye Masu zafi suka balo mata


Shin yaushe ne zata samu sasaucin zama da abokanan zamanta? Ko dai har ta koma ga Ubangijinta ba ranar samun sauki? Tun bata saba wahalaliyar raayuwar nan ba har ta gane in fa ba kanta ta rike ba komai na iya faruwa ciki harda sakwantar mata da cilon danta, sai ta basu lafiya take rayuwarta a gefe itama
Ama abu kulun cikin tugu da shari kala kala ake yi mata?
Tun tana da jan sawunta har yanzu da jinni ya dauke mata take kokowa da su da lamarinsu, shin yaushe zasu bata lafiya? Ace matar TAUFEEK, TAUFEEK nata , sai dai ta hangota da su? Me take tunani ne ita Yumnar?, Ba damuwa ko TAUFEEK suka kwace zata yi addu'a ta bishi da addu'a bale wata Yumnar banza da wofi, Allah ya taimaketa ga KHausar, wace ta mayar da ita tamkar uwar da ta haifeta, tunda ya auri KHausar take rayuwa da yanci itama a cikin gidan, take da abokiyar fira, mai yi mata girki ta kawo mata, mai zuwa ta yi mata fira, mai share mata kaso tamanin a damuwarta, kuma ga kyautar Allah ya bata itama, in sha Allah zata kaita asibiti da kanta gobe da safe a duba mata ita, su dawo ta raini cikin nan dan ba zata yarda ta koma aiki ba sai ta haihu da izinin ubangiji


A kalla ta dauki minti ashirin a zaunen nan tana share hawaye ta ringa jiyo hayaniya sama kamar za'a tsaga falon nasu


Sai da ta Saurara sannan ta ji gabanta ya fadi, ba dan komai ba sai dan tunawa da ta yi waye danta da tsinkayo muryarsa da ta yi sama da ta kowa, da Muryar kakarsa na dafe masa baya sai uwa uba Muryar mahaifinsa


A dole ta saka hijab dinta ta fito sanan ta nufi kasan tana kallon taron ba laifi harda maman Yumnah da yayarta da kuma Yumnar dake murkususu ko yaya aka yi aka nufo nan da ita kuma?


Mai kwanoni ne ya sauke ajiyar zuciya dan ya san yanzu rigimar ta lafa tunda wace ake rikicin kanta ta sauko, ya kuma san ita din mai hakuri da sanyaya fitina ce da KOWAMA bale in ta ga abin ya shafe shi, sai ya sauke ajiyar zuciya a karro na ba adadi ya ce" Maman Magidanci, ai gwara da kika sauko, shin ko me ya bata masa rai ai yana iya yin hakuri har wannan taa samu lafiya , haihuwa ai ba wasa ba maman Magidanci , sun fito zasu shiga Mota su nufi asibiti wai ya tarda su yace idan aka fita da ita a bakin aurenta sai kace ba likita ba? Kuma na yi tsawar kin ga HAJIA a gefe kin san dai ba barina zata yi in Hanna ba, dan Allah a yi hakuri a yayafawa matsalar ruwan sanyi, komai ya yi zafi maganinsa Allah, kuma hakuri shine ja gaban komai a rayuwa kin ji maman mai kwanoni?" (Wato ashe da baya kiran sunnanta dan fa ci sunan HAJIA ne?)


Mama ta kai dubanta kan KHausar wace mahaifiyarta ke sake talabarta dan ko tsayawa ta kasa yi, da gaske haihuwa ta zo mata dan kiris ya rage dan du ta fita hayacinta kukanma ya dauke azaba ta yi azaba kuma ga abinda mijinta yace
Mama ta ce" Elhaji a kaita asibiti mana, sannu Allah ya raba lafiya"
Daga haka maman ta juya da nufin komawa


Da mamaki ya ce" A'a, yaya zaki ce haka ki juya , wai yaya zaku tsaya wasa da haihuwa ne? Ke ku kamata a kaita asibiti" ya fada yana duban su KHausar dake tsatsaye, domin a lokacin da TAUFEEK ya maka wayar da suka yi da Mama a kas ya fice bai ce da ita ufan ba ta fito a guje ta bi bayansa tana ihun lafiya? Sai ta ga ya nufi bangaren Yumnah, da farko ta so komawa sai sai sunna tunkara ta ga an talabo Yumnar, a dole ta karasa tana aukin sannu, sai dai abinda ya fada ya saka su Dukansu rikicewa a lokacin da TAUFEEK, professeur TAUFEEK ya dubi tsabar idannuwan MACEN dake kan gwuiwa matarsa yace idan har aka fita da ita a bakin aurenta, sannan ya dubi mahaifiyarta yace da ita babu wanda ya isa ya wulakanta min uwata in ga darajarsa a duniya ko waye, sai kuma ya kalli HAJIA nawarah wace ta fara sarewa yace da ita a yau a gidan nan ko Ni ko ke, sai suka idasa sarewa duniya baki dayansu


HAJIA ce ta yi gagawar fadin" A kama wace? Sunna da damar tafiya da ita ama ka ji ai abinda mijinta yace , duk shegiyar da ta isa ta fita da ita a bakacin aurenta!"


Da mamaki Mai kwanoni ya sake yinkurawa zai yi wata maganar da tsawa da kuma rarashi da fadan a yi maza a kai baiwar Allah asibiti sai Yumnah ta yi wani irin ihu da nishi wanda ke nuni du inda kan d'a yake yana daf da zuwa duniya


A rikice suka rikice, gasu a falo su duka, Mama tuni ta komawarta dakinta ta datse da ky dan ta san mai kwanoni na iya cenza mata ra'ayi YANZUN nan, ita kuma ta yi rantsuwa babu ruwanta, abin ya isa haka, iskancin ya kai wajen da ba zata iya dauka ba kuma!


Kiri kiri TAUFEEK ya yi tsaye kikam a lokacinda KHausar ke sake sakin nishimai tare da bayanin fitowar kan Da daga jikinta


Da sauri mai kwanoni ya fice, kusan suka fita tare shi da KHausar wace ta yi bangarenta da gudu ta warto Safar hannu da kayan aikinta ta juyo da gudu gudu tana saka Safar hannun ta koma dakin hankalinta tashe , kana ganninta ka san taimako ne zata bada dan ceton rai


Wato an yi gudun Gara an fada gidan zago, sai ga KHausar din da aka so sai an haihu ta ji duke gaban Yumnah ฦ™afafuwan Yumnah Ware a irin mummunar warewa, jikinta bude a budewar da ko mijinta da wahala in ya taba gani a zamantakewarsu, jiki ya aune halitta ta zazago ta bude kai ya bado tana ihun azaba da ni'imar ubangiji har kai ya fito KHausar ta kama cikin kwarewa na cikakkiyar likita mai ruwa da tsaki a fannin amsar haihuwa ta juya jikin baby cikin dabara ta fitar da hannu daya sannan ta sake juyawa ta fitar da dayan kafin ta janyo babyn da ta tsalara kuka kamar a baakinta aka fara gwajin kukan, ta mike ta mikawa Aunty Akilah dake hawaye, hawayen girma irin na hukuncin ubangiji wanda ya fi kowa tsara komai, wannan shine kana naka Allah na nashi,daga wannan idan mahaifiyarsu da kanwarta suka ci gaba da wani abin to lalle zata dage da sanarwa ubangiji kan ya shirye su baki daya, a raunane ta sake kallon mijin kanwar nata wanda ya juya ya fice a lokacin da aka shiga musayar yawun ta karu, sai an yi mata ษ—inki, gashi ya Hanna fitar, wannan shine ga koshi ga kwanan yinwa , ga amsar haihuwa daga wajen kishiya ga kuma ษ—inki da kishiyar zata mata.........
















*ASALAMU ALAIKUM WA RAHAMATULAH YAN UWA, SAKWANI NA SAMUNA SOSAI TA MAGANA KAN TALLAH DA NA SAKA , ANA CEWA TA YI YAWA, HAKANE KAM TALLAH NA SAKATA SOSAI MASHA ALLAH, A HAKAMA NA RUFE AMSA NE , KU YI HAKURI TALLAR NAN DA KUDI NE NAKE YINTA๐Ÿ˜‚๐Ÿฅน , ama idan da wace zata maida masu kudadensu sai na bayar da account numba a maida masu sai na daina sakawa in sha Allah, daya ta biya Ni a kudinmu na Nijar jaka arba'in, dayar kuwa ta saka dubu goma dan mutunci, na gode๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜*
๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 6๏ธโƒฃ4๏ธโƒฃ


*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*


1: Duk karyar kada


2: Yar mahaukaciya


3: Neman na kaina


4: Bani da zabi


5: Bak'a ce


6: Kutkale


7: Makauniya ce


8: Mage


9: Duk nisan jifa


10: Idan ka raina inda kake


11: Dutse


12: Alkalamin kadarata


13: Bani da zabi


14: Dakika Biyar


15:Wata kokowar


16: Aure yakin mata


17: Ni zan ladabi


18: Daga tafia daukar soja


*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ


Tallah 3
Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa๐Ÿ˜”, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gadoโ˜น๏ธ๐Ÿซฃ
๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’ฅ
*HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528




kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji


Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu


Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528


Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji


Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan


Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa


Sabulun wanka
Kalolin sabulun tsarki
Turaren tsugunno
Turaren al'ajab
Hatsabibin turare
Da sauransu 07034251528




Kalolin gumba


Gumbar Dabino
Gumbar gero
Gumbar madara
Gumbar matsi
Gumbar ukku bala'i
Gumbar tada zaune tsaye
Gumbar sabon budurci
Gumbar sa buzu kuwa
Gumbar aya da kwakwa
Gumbar ridi
Gumbar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login