Showing 54001 words to 57000 words out of 186303 words
karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
A sanyaye sosai ta ce" Dan Allah ka yi hakuri Elhaji, a nan ban ga abin bacin rai ba sam, wayana tana gida yau tunda na tafi wajen aiki ban zauna ba sai yanzu da Aba ya saka ya daukoni, TAUFEEK fa dan uwana ne ba wani abu da zai taba shiga tsakanina da shi, dan Allah kar hakan ya saka ka fara wasu tunani a kan zumuncina da shi, domin shi din ya min halaci kuma yana cikin yi min "
Maimakun sanyayawarta, tausasawarta, da kalamanta naa fahimta su dan ganar da shi inda ta nufa sau ya ga ta karra rufa TAUFEEK, to in bama wulakanci ba shi zata duba tace wai TAUFEEK dan uwantane? Na ina?
Tare numfashinta ya yi ya ce" Ba sai kin nunan kin gaji kina son shiga gida ba, dama kulun a gubdure kike in ina gefenki, ki sani dan ya fini kudi ba yana nufin zai iya yin kyauta fiye da tawa ba, ko a gari ni an sanni in ina neman aure har gida bake ba budurwar, kema kun katsenine tun farko domin da kun barni da yanzu ba haka kike yawo ba sai a motar kanki, kuma da na cireku a gidan nan na maida ku wanda ya fi shi, nima ina iya yi maki halaci sosai Khausar dan ina sonki, bara na tafi na barki ki huta idan na dawo ma yi maganar, ki yi tunani sosai a kan maganata ta Elhaji, ni kam bana son tarayarku!"
Da ido ta raka shi har ya bacewa ganninta
Zuciyarta ta ji ta sake cinkushewa sosai har kamar zata kifa daga tsayen da take
Da kyar ta lalubi gidan ta shige da salama kasa kasa,
Idannuwanta suka sauka a fuskar Aba dake sake fadada fuskarsa da murmushi yana fadin" Oyoyo ga bokan turaina, ga autana, ga shalelena, ga masu yaki da allurana nan"
A hankali ta ja numfashi tana kallon fara'ar dake kan fuskar mahaifinta, a sanyaye ta shagwabe fuskarta ta sake kifta ido, sai ga abinda ba zata iya rikewa a gabansa, da mama, da TAUFEEK ba, watau hawaye,
Mama dake lekenta ta koma tana dariya dan ta san in ta fito abin kamari zai yi har ta mangareta, domin Aisha ta fada masu a dane take , a sama take sosai har tace wai ba zata koma ba, shi yasa Abansu ya kori kowa ya shinfida tabarma da ruwa da abincinta dan ya san in ta dan fara jajen dole a bukaci ruwa dan a dan jika makoshi a kuma ci abinci dan a sake samun karfi kadan, fatansa dai ta sauka da wuri dan ya fita ya siyo nata panadol ta dan hadiya, ko jikin ya dan saku
Tabarmar ta karaso tana cire takalmin kafa ciki ta yar a nan ta haye tabarmar tana kallon abanta
Sai kawai ta sheke da kuka harda tafa hannaye ta ce" Mahamadou Rasululahi sallalahu alaihi Wasallam Abana haka ake mutuwa? Ba accident ba, ba gobara ba abana gawa biyar biyar abana, wayo allahna abana kashi a fili, abana ashe aikin asibiti da kace ba zan iya ba inada saurin kuka na maka gardama haka ne?, Ai kam na yarda yanzun ba zan iya ba, gwarama a sakani wajen koyon dinki na koyo na ringa yiwa yan anguwa inda samun na sakawa a bakin salati"
Aba dake ta amsa salatin da ta yi da kula sosai ya ce" Asha, asha asha, to in ba autar Aba ba rasuwa ai kulun yinta ake yi, kuma kin san mafi yawancinta daga babar asibitinku ake fitar da ita, kin san gari ya girma ba yau ba al'uma ta cika, kuma harda kauyuka, idan lokaci ya yi dole a amsa kiran mai sama , Allah dai ya sa mu cika da kyau da imani, ni abinda nake sha'awa a aikin asibiti har nake tsayuwar dare ina kai kukana wajen Allah ya nunan irin ranar nan tarin ladan da kuke samu, yau a kawo maka marar lafiya ka masa sannuma lada ne bale ku da zaku cencana ku bi ku wanke jinni ku gyara waje, Allah ya sa sanadiyar shigarki aljanna ne wannan hanya Khausar dina"
Tsuru ta masa tana kallon yannayinsa
Kasa kasa ta ce" Abana, wai da cewa na yi fa an fasa aikin , tunda na je ban ci komai ba fa ina ta aiki ina ta aiki kamar in summa, wai da cewa na yi mu yi shawararmu da kai sai ka cewa Mama ka soke aikin asibiti ba zan koma ba ko Abana?"
Shima ya rage muryar sosai ya ce" kina nufin dan kawai kin dan wanke jinni kin ga gawa shikenan har kin karaya? Bayan kece mai kokarin a gidanma kaf? To da kike cewa fata kike ki fara aiki ki siya min babur in kika fasa da me zaki siya min kennan? Da kike cewa keke zaki koma shekara nawa zaki dauka kafin ki koya kuma ki dawo ku layu da su maman ummi wa za'a ba dinkin wa za'a hannawa? Ta yiwuma ke sai dai ki ringa dinkan jalabiya kawai a gidan, ni dai ina so ki yi aikinki abinda wahalar ta dan lokaci ce, na wata uku ne fa kawai, kamar gobe ne, kuma abincin da komai ni zan ringa kai maki fa, daga kasuwa zan je na kai maki sai in dawo, ni zan ringa rakakima fa"
Wani irin fadawa da ta yi a tunani sai ka tausaya mata ka kuma yi mamakin du girmanta shekara kusan ta ashirin da takwas ama mahaifinta ya yi mata wayo a dan kankanin lokaci, koda yake dama Khausarar aba ba dai rashin wayo ba
A sanyyaye ainun ta ce" Aba, ina jin tsoro, kuma akoy wahala sosai"
Da kula, zuciyarsa cike da tausayinta da tarin tunanin inama zai iya hannawar, da ya hanna, sai dai ya san abu ne da ba zai yiwu ba, du irin shekarun da ta dauka tana karatun nan Allah ya fitar mata da hanya ai wahala jurewa za'a yi kawai, dan haka ya ringa karfafa matya gwuiwa da kula yana nuna mata cewar ai wahala bata kisa, kuma Wajen nan da aka kaita zata matukar jin dadi zuwa gaba domin zata koyi aiki ne hannunta ya kware sosai har sai ta zama abin alfahari ga kowa da kowa
A cikin hirarsu ne yake mata maganar Yaya aka yi Mujaheed ya zo ya yi ta zama? Nan ta sanar masa basu yi zai zo ba, wayartama a gida ta bari, harma ta fada masa abinda Mujaheed din yace
A gabanta dai Aba bai nuna komai ba karshema saka ya yi ta shige wanka tana fitowa ta gaisa sosai da mamansu sannan ta shuge dakinsu, kafin kace me wannan barci ya yi awon gaba da ita
A lokacin da Aba ya shiga daki sosai ya nunawa Mama damuwarsa da damuwar yarsa, Mama ta bashi baki cewar idan aka jure yanzu abin zai wuce, dama aikin asibiti aiki ne mai girman gaske, dole za'a sha wahala idan ba'a saba ba, ama a hankali komai zai daidaita
Numfashi ya fitar zuciyarsa na masa wani kaikayi,, abin ke sukarsa har kamar zai amayar ya sanarwa mahaifiyarsu ama kuma ya rike a ransa
A maganar Khausar maganar Mujaheed ta matukar daga masa hankali
Anya akoy zaren mutunci a yarensa kuwa
Shi zai fitar da su daga gidan nan ya kaisu wani, da ta bashi dama da tana hawa motar kanta?
Me kennan?
Gaba daya sai zuciyarsa ke son gannin haka a matsayin cin fuska ko sharar fage dan ya kangarar da zuciyar yarinyarsa, idan har mai kwadayi ce maganarsa na iya sakata yiwa abin wata fahimta daban, shi bama maganar rabuwarta da TAUFEEK ya tsaye masa a rai ba, dan ya san dama idan har ta yi aure ba kowanu namiji bane zai iya hakurin mu'amalar nan, kuma summa ai yana gannin hakan ba zai iya zama matsala a tsakaninsu ba, abinda yake iya yiwa hasashen na iya zama matsala a lamarin nan wani taku da ya hango wanda da wahala ya iya jurewa, watau wulakanci
Eh lalle shi talaka ne
Kuma yana zaune a anguwar talakawa, yana cin cimar talakawa
Ama hakan ba zai ba kowa damar wulakantashi ko wulakanta masa ya'ya ba
Bai je ya roka a wajen kowa ba
Bai je ya yiwa kowa maula ba dan ya san ba mutun ne zai bashi ba sai Allah
Bai wulakantar da kansa ba ko a anguwa bale a kasuwa uwa uba a gaban sirikai
Ba zai lamunci komai mai kama da cin mutunci ba
Shi yasa ko maganar auren su Aisha da aka saka ranar amsar sadaki da kaya nan da kwanaki goma sha biyu bai zurma ya yarda aka ringa ba ya'yansa abinda ya shafi kudi ko abinda ya fi karfinsa ba, ko sun amsa a rashin sanninsa ne, baya yarda baya bada kofar nan, dan ya san babu wanda ya iya rikita zuciya irin dan Adam, saima ya nuna maka duniya kaine ya yi tsaye ya watsaka
Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya kai hakarkarinsa ya kwontar, a ransa ya gana yanke hukuncin sai dai Allah ya ba Mujaheed hakuri, domin ba zai dawo kan maganarsa ba gaskiya, ba zai gaba yarjewa Khausar amsar abin hannunsa ba, ba kuma zai masa maganar ba shiruma magana ce zai gani ne a aiyukansa cewa bashi da abinda zai basu ya ciresu a talaucin da yake gannin sunna ciki!
___________________________________
Du irin yadda ya so ta sasauta yannayin tsoron da take ciki nasa abin ya faskara
Dan murmushi ya yi yana kallonta, ta yi jajajir kamar an konata da ruwan zafi, sai hadiyar zuciya take yi tana sisine kai dan kawai yace sai ta ci abinci ya dubata kafin ta kwonta, haka ta wuni a kwonce waje guda danma ya wuni wajenta ya mata dukkan taimakon da ya dace domin har karin ruwa ya jona mata ya san jikinta ba maganar ciwo a yanzu sai dai ko ta saka tsoro a ranta ne bayan shi ya san a haka din ya yi iya yinsa dan kiyaye sakata a halin tsoron, ta so ta fi karfin tunaninsa ne har ta saka shi aikata haka domin bai yi niya da wuri haka su saje ba, sai gashi abu ya faru tsakaninsu a lokacin da bai shirya din bA
A hankali ya mike daga zaunen da yake ya mika mata hannu ya ce" Taso mana, wai ko ban duba da kyai bane kar aje kin karu, mu gani?"
Gabanta ya sake faduwa, curewa ta sake yi waje guda a saman gadon tana rintse ido tana jin tsoron kar fatarsu ta sake haduwa ta ji azabar da ta ji a yau
Bafa kokari ne bata yu ba, ta yi kokari fiye da tunanin bawa, abin ne ya girmami rashin hankalinta, ta yi dana sani da ta matse masa waje, ashe sanyin halinsa na macijin kumba ne sari ka noke? Ashe shi din wuta ne mai zafin gaske? Ashe hasashe ne take yi da akace da ya gama ta mike ta murje kamar ba'a yi ba? Gashi dai an yin an gama ama ta kasa mikewarma bale har ta murje kamar ba'a yi ba in ba dan an turo mata wace ta sake tayata kimtsa kanta ba da bata san yaya zata iya koda cin abinci bane
Da rarashi da komai ya bata kula daidai gwargwadon iyawarsa har ta samu barci
Murmushi ya yi yana dauke dubansa a kanta , tunani yake na lamarin rayuwa
Shi dama ya san a yanzu da take bakuwar lamarin ya fi karfin halitarta, sai dai mace rijiya ce ya san du wahala zata jure kuma du irrin abinda zata nuna a sannu zata saba
Shi likita ne baba ya san dalilin da ya sa ake so a bi mace a hankali har hankalintaa ya dauka
Murmushi ya sake yi ya karrasa saman salaya, ya shiga gabatar da ibadaraa cikin nutsuwa,
Sai kusan biyun dare ya kwonta, dan zai yi fitar wuri ne zuwa wajen aiki ga kuma kasuwa Aba ya fara maganar yana son sakar masa aiki shi kadai
_________________________________
Tunda sasafe ta shirya, Yau Aba ne tsaye kanta da zazafe tana turawa yana karra fadin ta karra ko kadan ne, abin har tausayi yake ba Mama idan tana kallonsu, soyayar Khausar da mahaifinta daban take kuma a bayane take
Tana gamawa ta sake yin bruch ta kuma shan panadol dan ciwon kan ya ragu ama bai daina ba gaba daya
A cikin hijaban da suka sha mamakin yawansu ya dauki daya ta saka a jakar da Aisha ta bata
Sosai Mama da yan uwanta ke karfafa mata gwuiwa sukai masu rakiya har bakin kofa
A kafa suka taka da Aba, sunna tafe Aba na ta yakin cire mata du wani kyankyami ko tsoro a ranta, yana nuna mata romon abin da sauransu har suka isa bakin likitar sannan ya bata dari biyar dinta cewar ta cin abinci ce
Haka dai ta rabu da Aba kamar an kawo yaro karami makaranta ranar farko tana ji tamkar ta bi shi da gudu ta su komawarsu gida
Haka ta saje ta ringa aiki tamkar ba gobe har kusan sha biyu mai gadi ya miko mata abinci cewar inji Abanta a nan ta kula ba abinci bane basa ci cin ne a tsaitsaye ba a nutse ba saboda aiki,kuma gannin jinni ko wani abin baya hanna su ci , sukan ci ne su ci gaba da aiki
A ranarma sai dare aka salameta ta nufi gida ta kuma tarda wani rikicin sabo na Mujaheed domin sai ya nuna ta ajiye wannan aiki zai sama mata clinik tunda bata da lokacinsa, karshema ya nuna shi faa gidansa bama zai iya barinta aiki ba, ita daita bashi hakuri sosai ta lalabashi suka rabu lafiya
A hankali kwanaki ke ja, har lokacin taron amsar sadakin Kannenta ya zo,ranar da ta yi iya yinta dan hanna kanta kuka, ba dan komai ba sai dan magangannu da ta ringa tsinta kala kala masu firgita zuciya da rikita tunanin bawa da saka bawa saka kansa a mugun tunani marar anfani
Kasancewar yan matan anguwa da na makaranta sun taru , ga tsofafin anguwa da datawa, kowa albarkacin bakinsa yake fada har zaman ya nemi gagararta a cikin mutane sai samun hanya ta yi ta fice a gidan ta nufi asibiti bisa umarnin Mama da itama tata zuciyar ta cinkushe gannin yannayin na khausar, bayan idan an tambaya ana fadawa mutane cewa tanada manemi magana ne bai yi ba a gaba, ama sai an bita da magangannu gasunan dai mararsa dadi
Tana zuwa ta samu doctoe Rauda ta kama mata aiki, a yanzu an fara bata dama irin ta saka allura da cirewa, wanke kurji da sauransu, haka kuma ta fara samun dama irin ta sakewa a cikinsu
Da wuri ta fito yau dan kiran da TAUFEEK ya mata cewar sunna gidan
A lokacin da ta karaso ta tardo ya zo daukan Hajia ne tare da matarsa, nan suka gaisa da Yumnah sama sama dai , ama ita sam bata gane ba dan hankalinta ba a nan yake ba a tunani yake wanda ke neman hanna mata sukuni
Sunna fitowa suka shiga mota TAUFEEK ya dawo ya dan zuba mata ido, du ta zube , kana ganninta kaa san ba jikinta bane , gashi yau harta lebenta a bushe yake kamas tsabar tunani da takura rai
A sanyaye ya ce"
*ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA*
Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu.
Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu.
Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda.
Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter.
Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba.
Muna