Showing 180001 words to 183000 words out of 186303 words
MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Tallah 3
Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣
🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥
*HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528
kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji
Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu
Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528
Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji
Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan
Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa
Sabulun wanka
Kalolin sabulun tsarki
Turaren tsugunno
Turaren al'ajab
Hatsabibin turare
Da sauransu 07034251528
Kalolin gumba
Gumbar Dabino
Gumbar gero
Gumbar madara
Gumbar matsi
Gumbar ukku bala'i
Gumbar tada zaune tsaye
Gumbar sabon budurci
Gumbar sa buzu kuwa
Gumbar aya da kwakwa
Gumbar ridi
Gumbar mazari
Sarauniyar gumba 3in1
Da sauran kalolin da bansamu fadi ba,
Kalolin gari
Garin mallaka
Garin hutar da malaminki
dakan jaraba
Dakan Amare
Dakan Ni'ima
Dakan kishiya in bakiyi bani waje
Garin sa buzu kuwa
Garin buje.sharkaf
Garin Dan la'asar
Yayan hadiya mai suna dan la'asar
Original Dan goshi
Original Dan goshi (sabon salo)
Original man damo
Original man ayu
Kitsen damo
Sirrin tafin kafa
Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata
Kwallin idonka idona
Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki
Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc
Kalolin tsumi
Tsumin mallaka
Tsumin jaraba
Tsumin madarar ni'ima
Tsumin tabaje
Tsumin Amare
Tsumin sabon budurci
Tsumin nono rakumi
Matan gaske
Ruwan jaraba,
Da sauran kalolin da ban fada ba
Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar
Matsin Dan mannau
Matsin mallaka
Dan la'asar
Sabon budurci
Mak'alemata
Mashahurin matsi
Ukku bala'i
Matsin uban budurwa
Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi
Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta,
Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake
*Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu ,
KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida
07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah
Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528
Maman zarah mabera SOKOTO
Sunna karasowa suka samu tuni su Yumnar sun iso, Yumnah na zaune a kasa kafafuwanta a hade waje daya, ciwo bai barta ba na haihuwa , ama yannayin mijinta shi ya fi komai daga mata hankali, yayarta na zaune daf da ita, mahaifiyarsu na saman kujera zaunen itama, ga dare dai ya yi ama tashin hankali ya saka su idannuwansu ya kekyashe tamkar rana, ga baby ta yi shiru abinta tana barci a hannun Akilah, Hajia na zaune itama , TAUFEEK na zaunen shima ama babu mai cewa komai tun gaishe da Hajia da suka yi da TAUFEEK din wajen ya dauki shiru
Kamar yadda suke zaune a kasa itama kasan ta je ta zauna daf da aunty Akilah, so take yi ta amshi babyn nan ta rungume a jikinta, tana so kwarai a bata babyn TAUFEEK dinta ta gani , ama ta san da wahala a bata shi yasa tunda ta ciro yar ta mikawa Akilah bata kuma nuna a bata ba ama tana matukar son kallon babyn ta kuma rungumeta a jikinta, ji take yi kamar itace ta kawo masa farin cikin nan, tabas ta san yana jiran wannan ranar, sai ga ranar ta zo masa wata iri, shi yasa ta so ta saka ya yi hakuri ama ya kiya, ta tabata ko menene to fa ya kai shi makura ne
Baba ne ya fara magana ta hanyar yin nasiha a tausashe ya ringa bada hakuri bale Hajia da ta kasance a wajen a dole ya bi yadda take so , sosai ya bada hakuri yana fadin" Idan rai ya baci, hakuri shine abinda ya fi dacewa bawa ya yi, bai dace ace an yi irin haka ba, a zauna a sasanta shi ya fi komai, ko menene ana iya sasanta shi a yafewa junna a ci gaba da rayuwa kafin mai rabawa ta raba, dan haka ko me yake faruwa a yi hakuri shi ya fi alkhairi"
Bayan ya gama nasihar da bada hakurin ne ya dubi maman su Yumnah ta bata damar yin magana
Itama a tausashen da bata taba yi masu magana ba yau ta dubi Mama ta ce" Hajia, dan Allah ko me ya faru a yafi junna a yi hakuri, mu bamu yi haka dan a bata maki rai ba, kuma kin gani Yumna yarinya ce ko me zata yi sai ana mata uzuri, ki yi hakuri komai ya wuce"
Mama dake zaune ta yi murmushi ta ce" Na hakura"
Daga haka ta mike ta juya da nufin tafiya
Baba da ya gama Sannin abinsa ne ya ce" Maman magidanci dawo ki zauna"
Mama ta dakata, a dole ta juyo ta dubeshi, kafin ta dubi Hajia ta ga hararar da Hajia ke sakar mata kamar idannuwanta zasu fado , sai ta yi wani murmushin ta dawo din ta zauna daf da Hajia ta sada kanta
TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya ya dubi mahaifiyar Yumnah da Yumnah din baki daya sannan ya kalli Aba, a tausashe ya ce" Aba, ka yi hakuri dan Allah ,ama bana tunanin bayar da hakurin nan a dunkule zai gyara Ni, dan ban me da me aka yiwa mahaifiyata ba duk wannan zaman da aka yi , wanda idan na ji ne zan iya ganewa in har zan iya yafewa ko waye, domin kaf duniya babu wanda zai wulakanta min uwa na daga masa kafa!"
Hajia aka wani saki murmushi tana sake ture daurin dan kwalinta gaba ta wani ja hannun riga ya yi sama kamar zata yi dambe ta ce" Ahaf, abubuwa ai an yi su magidanci ba dan kadan ba, Ni dai abinda nake so a gane a nan a cire min wata maganar rashin kunya cewar wannan y'a yarinya ce, ke yumana dan yan gidanku baki san darajar taki uwar ba? Ni fa munafunci ne da shashanci bana so, na fada a tsaye na fada a zaune karshe nima sai na zama abokiyar gabanta, ama idan zaki tuna na fada maki ke ki kiyayi magidanci da uwarsa wa bilahilazi idan kika yarda ya gane wawa ce ke sai ya tatakaki ya kaiki gidanku a kan mamansa, ke bakima san ruwan dake wankanki ba, sarakuwa ko bata sonka neman fada kake a wajenta bale wannan da babu abinda ya dameta da lamarinku ita fatanta ku zauna lafiya? Yo Ni nan meye baba ta soro bata min ba Allah jikan rai na yafe mata iyi? Ama haka na rayu ina bin gindi kar a watsani waje , uwa ai tana gaba da komai, in ba dan iska Bama waye zai raina uwar wani? Ki dauka a kan taki uwar gatanan mana iyi? In menene kece kika fara yiwa kanki, mu muna da sha uku aka mikamu daki muka iya girmama iyayen miji bale ya'yan yanzu ya'yan salula yar latse kunna dirowa duniya kuke matse anini, kuma kun iya neman maganin mata rai a shige daka da miji, har ku ne za'a koyawa kula da uwar miji? Da abinda ke ranki dai yar nan wanda ba zai samu ba dan gaskiya ina tsoron shima ba zaki samu ba, ki sauke kanki in zaki sauke a yi rayuwa in kuma tashina tashina za'a yi in fede biri da abawa a wajen nan na irin laifukan da kika yiwa uwar magidanci kau?"
Kusan a tare su uku suka nema ba sai Hajia ta fada ba, kowane da yannayin da ya yi furucinsa ama matsayar su daya ce kar Hajia ta fere biri da abawan nan da tace zata fere, da baba mai kwanoni da Yumnah da kuma mahaifiyar Yumnar
Yumnah murya na rawa ta ce" Mama dan Allah ki yi hakuri, dukkan abinda na maki ki yafe min in sha Allah ba zan kuma ba, baba da Hajia dan Allah ku ba yayanmu hakuri ba zan kuma ba"
Baba sai ya karra jin tausayin yarinyar ya kama shi, ko dan bai san me da me ta yin bane? Ama ko menene yana ganin ana iya yafe mata, ko menene, dan haka a tausashe ya dubi maman TAUFEEK ya ce" Hajia karama, ki yafewa yarki kin ji? Kin san yayanmu sai da hakuri, ki dauka yarki ce ta maki laifi ta kuma yi nadama kin ji?"
Mama ta sauke ajiyar zuciya yanzunma a tausashe ta ce" Ni fa na jima da na yafe babansu, Allah ya shirye su ya musu albarka"
Da amen aka ringa amsawa, Maman Yumnah ta sauke ajiyar zuciya ta ce" an gode Allah ya saka da alkhairi an gode sosai, kin ga ta karu Yumnar idan da hali sai a kaita asibiti dan kar ta kwana abin ya zama wahalarwa"
Baba mai kwanoni kam sai ya mike gannin an samu sasantawa ya karasa ya dauki yar ya je ya duka daf da Hajia ya bude mata yar fuskar jaririyar yana murmushi ya ce" Hajia ga fa amaryar tawa, Ni sai nake gannin kamar ta fi magidancinma kyau masha ALLAH"
Hajia da kwallah ta tarun mata a ido a hankali ta amshi yar tana kallo , sai ta saki murmushi ta dago tana kallon Mama da Khausar dake matsowa tana so a bata, Hajia ta sake sakin murmushi ta ce" Matso ki tayani gani Khausara, kin ga yar y'ar magidanci , kin kuwa san irin adu'ar da nake yi Allah ya nuna min, kai shedan ko dan hegiya Allah dai ya rabamu da sharinsa! Mai kwanoni ka mata huduba mana ka ji? Wani sunna za'a saka mata?"
Baba na murmushi ya kalli TAUFEEK da har yanzu ba wani sakin fuska ya yi ba ya ce" Wani sunna kuka zaba ne Elhaji karami? Ka kuwa dauketa? Kamarku daya, kennan kama take da Mamanka, matso ka yi mata addu'a sannan ka duba lafiyarta idan kuwa asibitin zasu tafi sai a kai su a basu dukan kular da ta dace, Allah ya yi albarka"
A tausashe TAUFEEK ya amsa da amen Aba, sannan ya sake sada kansa a tausashen ya ce" ka yi mata da sunnan Nana Khadija Aba, Allah ya raya ya yi mata albarka"
Aba ya amsa da amen ya Allah, hakama dukkan wani dake wajen
TAUFEEK ya dora da fadin" sai dai ina neman alfarmar a yi hakuri da maganar fitan, zan dubata da kaina, ko wanka ba zata je gida ta yi ba zata yi a nan gidan, idan akoy Wada zai zo ya zauna mata Tom, in babu Hajia zata samo duk wace ta ga ta yi ta zauna mata, sai abu na karshe, Yumnah ki ji tsoron Allah ki kuma guji fushina, ba zan lamunce ki wulakanta koda auta bane a gidan nan dan Ni ban wulakanta kowa ba a gidanku, ki sani raina mahaifiyata shine mafi munin kuskuren da zaki kuma tafkawa, domin wannan zama da aka yi yau ina mai tabbatar maki ba za'a kuma maimaitashi da Ni ba, ba zai yiwu ace kulun ina tara iyayena a kaina ba, inaga na yi girman da zan kare masu wannan tashin hankali na iyalina!, Idan har da hali zan so ki gane mu zauna lafiya, idan kin kiya Yumnah ba zan iya zuba maki ido ki wulakanta min wace ta haifa maki Ni ba, du dadin zaman da zan ji da ke lami ne idan har baki girmama min uwa ba"
Yumnah da sai yanzu ta ji sanyi na ratsa zuciyarta ta girgiza kai da sauri ta ce" In sha Allah ba zan kuma ba yayanmu" a zuciyarta kuwa tana ayana' bi izinillah ba zan kuma ba, koda mama bata so na zan yi mata biyaya bale su Hajia ne ke cewa ba zata taba so na ba, sai yau na ankara da aunty tace na san basa son mijina Ni me zan masu a duniya da zasu so Ni? Kowa ta kansa yake yi, nima kuwa zan yi ta kaina, Khausar ta zama zanen kadarar rayuwata Allah ya yi sai ta auri mijina , in sha Allah zan koyi zama da ita, ina ji ina gani na haihu maimakun na zamto ina cen lulube ana jiji da Ni gani a filin Allah ko ciwon baya damuna kamar bacin ranka? Soyaya ba karya bace Ni na san ina sonka kuma zan yi maka biyaya koda kana cutar da Ni ne bale idan har na nuna ka cutar da Ni na zalunceka!'
Masalaha aka samu sosai ,
Mahaifiyarta cike da tausayi take kallonta, lalle ta yarda da maganar da Akilah ta fada wani lokaci cewar, Mama, ki bi Yumnah da addu'a, domin son da take yiwa mijinta ya fi wanda shi yake yi mata, ki yi kokari ki ringa kwabarta kina nuna mata ta yi hakuri ta kuma iya zama da mijinta, shine kawai zai fisheta, domin ko aurenta ya mutu ita zata wahala, na riga na gane tana sonsa fiye da tunani bata iya rigima da zuciyarta a kansa, hakan ya sa take tunanin ta fi kowa sonsa, idan har zata samu ko mahaifiyarsa kar ta rabe shi, kin ga kuma son kan ya yi yawa abin zai haifar mata da damuwa, mafi a'ala shine a nuna mata TAUFEEK miji yake a gareta ba yaron gidanta ba, ba kuma abinda take kiwo ba, dole ta mutunta ahalinsa
Ajiyar zuciya ta sauke ta mike ta bi bayan mai kwanoni da yace ta zo a kaita gida, Akilah kam nan zata zauna
Baki daya suka dadaka suka nufi bangaren Yumnah banda Mama wace ta wuce nata bangaren dan ba zata iya binsu ba, ga Hajia ga Khausar ga Akilah ai ko menene sun isa, TAUFEEK ne ya wuce bangaren Khausar dan daukan kayan da zai mata anfani da su dan yi mata dinki
Sosai ta ci azabar ɗinkin nan, du kuwa da ya kashe wajen ama waje ya riga ya fara hucewa da zafin fitowar kan d'a hakan ya sa ta sha kuka da ihu na azabar ɗinkin har ya gama mata sannan ya janyota jikinsa ya rungumeta yana share mata zufar dake tsatsafowa a goshinta
A raunane ta dora kanta a kirjinsa tana shaƙar kanshin jikinsa
A tausashe sosai ya furta" Allah ya maki albarka , ya raya mana Anmi, Allah ya baki ladan daukan ciki da dawainiyarsa ya sa Anmi ta zamto mai jin kan iyaye ce"
Ajiyar zuciya take saukewa tana amsawa da amen , tana ji kwarai ta so cutar kanta, da kulawar da ta fi wannan ce zata samu , sai gashi ta yi sake da damarta, ama kuma ta