Showing 114001 words to 117000 words out of 186303 words

Chapter 39 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18785

hakuri ki zo ki zauna"


Rai bace ta juyo tana daga hannunta kusa da ita ta ce" Ke Akilah walahi idan kika yarda kika kawon raini a wajen nan zan dauke fuskarki da mari, in ke baki san zafin Yumnah ba Ni na san ciwon abata idan ba zaki iya ganni ba kauce ki koma gida!"


Wani tsadadan murmushi Hajia Fatahiya ta saki tana sake talabe jaririyarta, hakama Hajia Nuwairah ta dauke kanta tamkar basa wajen


Hajia ta shiga rafka salati tana kallon mahaifiyar Yumnah, lokacin ne kuwa Nurse Halima ta wwucewarta dan ta kula abin na nema ya zama family isu
Hajia ta ce" Ikon Allah, wai kamar wace kike yade yaden magana a wajen nan , Ni wama ya sanar maki da maganar nan ne? Mu bamu isa mu kula da ita bane sai an taso ki? Aure ne fa aka daurawa magidanci Bama shi ya je ya nemi auren ba shine zaki zo kamar kubunuwa kina magangannu kamar wace ke daf da kyatsa ashariya? Allah dai ya sa ba magidanci kike son fadawa magana ba , dan da wahala na iya kawar da kaina kowani shashasha ya wulakanta min jika, da kika ganni nan babu irin fadan da ban gani ba, ke karama ce, in zaki nemi kawo min raini a duniyar magidanci in dauke fuskarki da mari ba wani abu bane a wajena! Ke yau ga salamamiya, an yiwa yar taki kishiya kuma ubanda ya kirayeki ko waye ya kuka da kansa, ai ji ji zaki yi dan ba abin a boye bane, yaro kuwa da kudinsa da lafiyarsa akoy wanda ya isa ya tsayar da shi a daya kwalin kwal ? Ai hudu cifff zai jera maki gani ya kauda idannuwansa!"


Hankali tashe Akilah ta karasa tana kokarin riko hannun Hajia ta ce" Hajia, dan Allah ki yi hakuri, duka abin nan an samu rashin fahimta ne, irin yadda aka sanar da momynmu maganar auren da rashin lafiyarta ne ya tayar mana da hankali, ama ba maganar wulakanta TAUFEEK,, itama momy ba zata yi haka ba , an riga an zama daya ai du wata fitina ana fatan Allah ya tsare ta, aure kuwa ai nufi ne na Allah dan ya yi aure ai ba shine damuwar ba in dai mutuniyar kirki ce fatanmu Allah ya hada kansu ya bada zaman lafiya............"


Magana Akilah ke yi da dukkan gaskiyarta, burinta ta katse fitinar da take gannin na kokarin Kunno masu a tsakaninsu, bayan ita fitina farkonta aka sani ba'a san karshenta ba, kuma ko ba komai a duniyar hausawa ake kuma musulmai, idan har aka yi duba da irin yannayinsa bata san lafiyarsa ba ama a tsarin dukiya da yannayin nasabarsa tara mace hudun da kakarsa ke ambata ba laifi bane, dama an umarta a yi idan za'a iya kula da su a fita hakinsu ne, a nan bata ga abin rikicin nan ba, abinda ba'a yiwa kanwarta adalci ba daya ne tak, shine aka yi ba'a sanar mata ba, dole ne a ji ba dadi, ama idan rai ya bace hankali ya tashi sai a yi shiru a yi ta ambaton sunnan Allah sai ka ga komai ya zo da sauki


Tana rike da hannun Hajiar wace ta zuba mata ido tana kallonta alamun jikin Hajiar kamar ya fara yin sanyi jin kalaman Akilar suka ji an fizgo Akilar, basu yi wata wata ba suka ji dauke fuskar Akilar da zazafan marin da ya saka MAMAN TAUFEEK dago kanta daga wajen da take kallo tana jan carbinta irin na jikin yatsar nan fari kal mai yar kyalkyali a jikinsa ta sauke dubanta a kan su gaba dayansu, daidai lokacin ne kuma TAUFEEK ya karaso, ya dan samu tsaikon isowar ne sakamakon rigar aikinsa da nurse Halima ta je cen sama office dinsa ta dauko masa da takalmin aiki da Safar hannu da abin auna awon zuciya


A nutse yake karasowa, idannuwansa a kansu baki dayansu, tun daga kan iyayensa har na matarsa




A hankali ya sauke dubansa a kan Akilah, wace ta dafe fuskarta kanta a kasa tuni hawaye ya fara wanke mata fuska, a haife ko Akilah ya girma bale Yumnah, sai dai a yadda take mutuntashi yakan ce mata auntynmu , itama sai tace da shi yayanmu dan girmama junna


Kai ya dauke ba tare da ya iya cewa kowa komai ba ya ratsa su, cike da kamala da yannayi irin na baban likita ya shige ciki, hakan ya sa gaba daya suka bi shi da kallo kowa na ayana abinda yake ayanawa a ransa dangane da dan uwansa a kan TAUFEEK din


Yana shiga dakin ya karasa wajen allurar da docter Muktar ya haษ—a ya amsa a nutse ya karasa gaban gadon nata ya janyo kujerar dake gaban gadon ya zauna sannan ya zuba mata ido bayan ya dauki audugar da zai yi anfani da ita dan yi mata allurar tunda ba karin ruwa ta yarda aka jona mata ba


Numfashi ta ringa ja tana kallonsa, kallo irin kamar ta ga wani maciyin amana, dubansa take yi kamar wace ta ga bakinta, tarin hawayen da ya cika gurbin idannuwanta kuwa na masa nuni da tashin hankalin dake saman harshenta, sai dai tarin firgicin da ya sameta, da irin yadda ya kasance mai tasiri a dukkan motsinta ya hannata iya budar baki bale har ta masa rikicin da take jin tana iya yi masa a kan maganar da ta gama yankewa kanta ko ita ko wace ake nufin an aurawa mijinta!


A hankali ta budi bakinta gannin ya kama hannunta ya daura yar igiyar da zata bashi damar samun jijiyar da kyau sannan ya rike audugar a nutse ya goge bayan hannun nata, ita kuma ta budi baki ta ce" Yayanmu, dan Allah ka ce min ba zaka iya amsar auren nan ba, na san ba son ranka bane, kana da damar sakin............."


"Yumnah" ya fada a hankali, cike da fitar da amon da ya fi kasarata, ya tsare idannuwanta da manyan idannuwansa, a dole ta sauke dubanta kan sajensa domin kallon ya matukar mata girma


A nutse ya maida dubansa ya soketa da allurar ya kunce daurin ya zuba mata ruwan allurar sannan ya zage ya dane da audugar ya ajiye allurar a cikin dan kwanon da nurse ke rike da , shi kuwa yana rike da hannun nata a hankali yana dan murzawa yana kallon fuskarta mai zubar da hawaye har ya dauki mintinan da zasu kai sha biyar sannan ya mike yana gyarata gaba dayanta ya rufa mata abin rufa kadan sannan ya juya bayan ya daidaita mata ac ya fice a dakin yana cire safar hannunsa


Yana fitowa ya ja ya tsaya gaban ahalinsa, a yadda ya shige ya barsu yanzun basa hayaniyar, sai dai kana ganninsu ka san kowa a dane yake, sai kuma ya fuskanci abinda ya hanna su hayaniyar vigil din dake tsaye su hudu ne kowane ya hade girar sama da ta kasa sun fada masu cewar du fa wanda ya masu hayaniya fitar da shi zasu yi


Da kula ya ce"


๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 4๏ธโƒฃ4๏ธโƒฃ


*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*


1: Duk karyar kada


2: Yar mahaukaciya


3: Neman na kaina


4: Bani da zabi


5: Bak'a ce


6: Kutkale


7: Makauniya ce


8: Mage


9: Duk nisan jifa


10: Idan ka raina inda kake


11: Dutse


12: Alkalamin kadarata


13: Bani da zabi


14: Dakika Biyar


15:Wata kokowar


16: Aure yakin mata


17: Ni zan ladabi


18: Daga tafia daukar soja


*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ








Da kula sosai ya ce" Alhamdulilah ta samu barci, ku mu je a maida kowa gida dan basa yarda da yan jinya"


Mahaifiyar Yumnah cike da gannin rainin hankalin TAUFEEK ta ce" Basa bari ko baka bari, ko kana tunanin har yanzu bamu san wanene kai da matsayinka ba? Bama wannan ba, Taufeek bani da muradin a kula da ita a wajen da ake neman ranta, ko shekara bata rufa ba an dankara mata uwar mata, wa ya san me zai sameta idan na tafi na barta, a bani y'ata kawai a tafi da ita gida mu yi jinyarta a cen!" Ta karashe tana fitar da huci, daci take ji a ranta sosai na wannan lamarin, babu irin tarewar da basu yiwa wannan abin ba ama a karshe sai da wannan anobar ta zama mata a wajensa? Lalle da take kwabar Yumnah cewar ta daina tunanin akoy wata mu'amala da ta wuce soyaya da abotakantaka tsakaninsa da wancen guzumar yanzun itama ta fara tunanin ta yiwu wata jarabar ta bulo aka yi wannan auren rufa rufar dan kar a ji!


Murmushi mahaifiyar TAUFEEK ta yi tana girgiza kanta


Shi kuwa cikin nutsuwa ya saukewa vigil din dake tsaitsaye duba, kafin kace me sun yi gaba sun bar wajen


Hajia baba ta girgiza kai cike da tarin takaici ta ce" Kai, fito mata da y'ar ta tafi da Itan mana sai me, wato ke ana baki kina roko kema nan uwar y'a kike ko? To bari ki ji da bakina ina waje a raye babu mai dagawa magidanci hankali, aikin banza wannan har matar huce haushi ce? In ba rashin daukan shawara Bama , ai macen farko rusasa ake dauka gidan hakuri gidan huce haushi idan ya so daga baya sai a bi dadi duniya yan idan Kanada shi ake iya zama da kai in baka da shi ba'a iya zama da kai!, Aikin banza ke kuwa kina tsaye ana neman zagar maki d'a sai dai ki yi murmushi , shin zafin nakuda aka fi ki sani ko amfanuwa yarta ta fi d'anki? Idanma zafin fitar kai ne ai na magidanci zai fi azaba, ke dai Allah ya shiryeki!"


TAUFEEK ya idasa sauke dubansa a kan Hajia , ikon Allah yake kallo, Hajia da hijab kamar zai tadeta ta fadi ama banda neman rigima ba komai a cikinta,
Kai ya girgiza ya juya zai bar masu wajen mahaifiyar Yumnah da take ji inama inama idan ta bude baki ta durawa uban kowa zagi babu abinda za'a yi, ama tana tsoron wannan dakewa ta TAUFEEK da kuma sharewar da mamansa ta yi, bata san me hakan ke nufi ba, ta sake dubansa ta ce" Yaya zaka tafi bayan na fada maka ina so a fito min da ita mu tafi gida?"


TAUFEEK ya dakata da tafiyar da yake yi ya juyo, a hankali ya washe fuskarsa daga yannayin hadewa ya dan saki murmushi ya ce" Cewa na yi kowa ya koma gida, zan kawo ta idan na ga zata iya jurewa hakan"
Daga haka ya yi tafiyarsa


Mahaifiyarsa ta yi murmushi ta dauki ledar goron Hajia da ta yar tana masifa ta ce" Hajia mu je a maida mu gida"


Hajia da ta gama summa a tsaye gannin badalar da Magidanci ya aikata ta ja numfashi ta ce" Eh kaini gidan dai na ga mai Kwanoni, kin ga kuma yannayin magidanci ya bani tsoro gaba dayanmu ya hade ya kora, Ni uwar mai kwanoni harda Ni? Mu je mu je"


Da sauri Akilah ta fice itama a wajen ta bi bayan su Mama, har Mama ta shiga Mota ta dakata gannin ta karaso


Tsayinta ta rage sosai ta ce" Mama dan Allah ku yi hakuri da abinda ya faru, in sha Allah idan mun je gida komai zai daidaita"


Mama ta sakar mata murmushi cike da gannin girmanta, sosai yarinyar ta birgeta, da kula sosai ta ce" Kar ki damu auntynsu, ba wani abu kin ji? Allah ya bata lafiya, a kuma yi hakuri abin ne ya zo a haka, kin san aure da haihuwa ke da komaima na rayuwa lokaci ne, Allah ya yi haka zata kasance, kwarai ba'a kyauta mata ba, kuma Ni mace ce na san me muka dauki kishi, ama ina mai bata hakuri kuma in sha Allah Elhaji karami zai yi adalci a tsakaninsu"


Daga haka suka yi mata salama direban da TAUFEEK ya sa ya kai su gida ya ja motar


Sai da suka yi nisa Hajia ta ce" Uhum, wani lokacin sai ki yi halaya na munafukai sak , yo me kika masu da zaki basu hakuri? Aure fa an daura sai dai a ci da haka, Ni abinda nake son sani wani shege ne ya yi kiran uwar yarinyar nan ya sanar mata kai tsaye har take son zagina?"


Mama ta ce" Aa Hajia ba zata yarda ta zageki ba, kawai rai ne ya bace, ama komai zai wuce , ita Allah ya bata lafiya, wanda ya hadasa haka kuma Allah ya bashi ribar da ta dace da shi"


Sunna tattaunawar nan har suka isa gida


A asibiti kuwa hajia nawarah basu tashi bada hakuri mai kama da zigi ba sai da aka watse aka barsu da Maman Yumnah
Hajia Fatahiya ta saba yarta a kafada tana fadin" Zamu tafi Hajia, kin san mijin Yumnar bai cika lalaba abu ba, du girmanmu da matsayinmu na matan mahaifinsa in ya dawo ya same mu a nan yana iya zazaginmu , kin san abu da baban gida , Allah dai ya sanyaya ama ai abin ba tausayi sam, yarinya karama a hada da wannan ina zata saka ranta, yaya zata iya kishi da wannan mace, ai kawai in nice Elhajin zan nemi gani a duba lamarin nan , gaskiya a zaba y'ata ko wancen kaska rabi mai jinni jikar"


Hajia nawarah ta cafke da fadin" Uhum, Ni dama na san a irin kwadayin yarinyar nan da iyayenta komaima zai faru, Allah dai ya sa a barwa Yumnah cikinta kar aje a kaita wajen bokaye a rabata da cikinma dan kuwa na tabata kai sake Elhaji ba zai aurawa Magidanci wannan guzumar ba, menene abin mora a mota mai hayaki? Wahala ce kawai, Allah dai ya kyauta mun tafi kar ya dawo ya wulakantamu , kin san bashi da sauki ko kadan!"


Sosai abin ya sake rikita mata lisafi, suka fice suka barta zaune ta zubawa waje daya ido har Akilah ta dawo ta zauna gefenta kanta a kasa ta kasa cewa komai ama tana sauraron wayar mahaifiyar Tata domin ta yi kiran babansu ta sanar masa abinda yake faruwa ya kuma ce zai kirayeta yanzu yanzu su koma gida zai dawo shima yanzun ya sameta


Huci ta sauke tana share hawayen fuskarta ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kar dai idonmu ya rufe mun biyewa Yumnah da son da take yiwa yaron nan mun aura mata marar mutuncin dan kasuwa? Ki duba ki ga kaf dinmu ya kora ba jin nauyina yace zai kawo min y'ata kennan yana iya sakinta ba damuwarsa bace ko?, Kin kuwa ji me iyayensa ke fadi? Wai bari su yi su koma kar ya dawo ya same su ya wulakantasu, wai ya saba, to ya wulakanta su su, Ni wacece da ba zai min ba? Uwa uba y'ata? Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une kar dai mun shigo rigimar da ta fi karfinmu, d'an baba da so ne ubansa ya masa aure ko shekara y'ata bata rufa ba a gidansa ba shawara ba komai kuma kakarsa ta zageni tasss? Ba zai yiwu ba, Allah ba zan iya yarda ba, sai an saki yarinyar nan ba za'a hadata kishi da Yumnah ba, ko ni uwarta ba'a min kishiya ba bale ita!"


Ita dai Akilah kanta a kasa, har ta gama kira ya shigo wayarta mahaifinsu bai tsaya sauraronta ba ya bata umarnin kasancewa a gida yanzu yanzu yana jiranta


Da kyar ta yarda suka tafi tare gidan suka bar Yumnar a asibitin, a gaban idonsu Nurse ta shiga da kayan kula da ita da komai , itace mai jinyarta kuma likitocin sai lekowa suke ana fadin matar docter ce ba lafiya, ita ya san za'a kula da Yumnar fiye da du inda zasu kaita, fatanta mahaifinta ya ci karfin wannan fitinar dan babu inda zata kai su sai dana sani


Sosai ya samu hutun shima a asibitin a ranar, barcin da bai samu ba jiya ya samu ya dan rama sannan ya sauka ya koma dakin Yumnah ya dubata sosai da karin ruwan da aka jona mata da abinda aka rubuta za'a ringa mata har ta warware sannan ya yiwa nurse din dake tare da ita salama ya nufi gida


Ko da ya isa gidan part dinsa ya wuce ya shige wanka, Yana gamawa ya je wajen mahaifiyarsa ya zauna suka dan taba fira sannan ya je wajen mahaifinsa, daga nan ya yi tafiyarsa bangarensa ya kwonta dan zai je aiki ne goben da wuri dole


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login