Showing 168001 words to 171000 words out of 186303 words
zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣
🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥
*HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528
kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji
Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu
Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528
Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji
Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan
Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa
Sabulun wanka
Kalolin sabulun tsarki
Turaren tsugunno
Turaren al'ajab
Hatsabibin turare
Da sauransu 07034251528
Kalolin gumba
Gumbar Dabino
Gumbar gero
Gumbar madara
Gumbar matsi
Gumbar ukku bala'i
Gumbar tada zaune tsaye
Gumbar sabon budurci
Gumbar sa buzu kuwa
Gumbar aya da kwakwa
Gumbar ridi
Gumbar mazari
Sarauniyar gumba 3in1
Da sauran kalolin da bansamu fadi ba,
Kalolin gari
Garin mallaka
Garin hutar da malaminki
dakan jaraba
Dakan Amare
Dakan Ni'ima
Dakan kishiya in bakiyi bani waje
Garin sa buzu kuwa
Garin buje.sharkaf
Garin Dan la'asar
Yayan hadiya mai suna dan la'asar
Original Dan goshi
Original Dan goshi (sabon salo)
Original man damo
Original man ayu
Kitsen damo
Sirrin tafin kafa
Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata
Kwallin idonka idona
Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki
Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc
Kalolin tsumi
Tsumin mallaka
Tsumin jaraba
Tsumin madarar ni'ima
Tsumin tabaje
Tsumin Amare
Tsumin sabon budurci
Tsumin nono rakumi
Matan gaske
Ruwan jaraba,
Da sauran kalolin da ban fada ba
Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar
Matsin Dan mannau
Matsin mallaka
Dan la'asar
Sabon budurci
Mak'alemata
Mashahurin matsi
Ukku bala'i
Matsin uban budurwa
Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi
Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta,
Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake
*Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu ,
KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida
07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah
Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528
Maman zarah mabera SOKOTO
A nutse ya zauna yana duban docter Mufeeda wace ta daburce ya mata nuni da kujerarta ya harda yatsunsa ya bata dama har ta zauna tana ta kokarin gannin ta hanna kanta rikicewa ama a bayane rikicewarta take, dan asibitin nan sunna da doka masu ƙarfin gaske da ake dukkan kokari dan kiyayewa
"Akoy matsala ne da ya hanna masu aikin wanke datin patient yin aikinsu?" Ya fada ba da hargowa ko wani tashin hankali ba
Docter Mufeeda sai da ta ja numfashi na tashin hankali a hankali ta girgiza kai ta ce" A'a babu sir"
"Me yasa zaki saka Khausar wankewa? Me yasa a irin lokacin nan da kowa keda damar zuwa ya ci abinci idan har ba urgence GAREKU ba ita take nan tana aiki?"
"Docter, aikinta ne bata gama ba shine yasa bata je din ba, kuma da ta gama sai nace ta wanke cen din dan an tabo mu ya yi aman gashi sun je cin abinci" ta fada tana dawurwuri da neman mafita
Tsareta da ya yi da duban nan nasa ba tare da ya sake ce mata komai ba ya sakata shiga halin rikicewa
Kanta ta dafe da hannayenta biyu ta ce" Dan Allah docter ka yi hakuri, ba zan sake ba in sha Allah kowa zai yi aikinsa yadda ya dace ka yi hakuri"
"Idan kina da wata case da ma'aikatan da suke karkashin ki a matsayinki na baba, ki bi yadda ya dace dan a ringa mutuntaki , idan ta maki wani laifi ne ki shigar da kara , ko me tsakanina da ita zata dauki hukuncin da asibiti ta ɗorawa doka, ba zamu bari ma'aikata su raina ku ba, but ba zaku wulakanta su ba, kuma ki sani kamar yadda kike da damar kai karar ta maki tana da damar kawo karar kin mata, idan har tana da gaskiya Docter Mufeeda Muhammad doka zata hau kanki ne kuma ko ina kika je sai ta hau kanki dan kin san ban kafa asibitina ba sai da na tsaya da kaffafuwana, i'm i clear?"
Wani irin yawu ta hadiya mai santsi da sauri ta gyada kanta tana ci gaba da bashi hakuri shi kuma ya mike ya yi tafiyarsa zuciyarsa na kuna da tunanin dolema Khausar ta saka kara dan ya samu damar wanke wannan matar, domin a haka ba zai hauta kai tsaye ba, shine zai taka dokarsa da kansa, ama inda yake godewa Allah ba wai manyan docter kadai keda ikon kai karar ba, harta wa'inda ke karkashin su sunna da damar nan!
Yana nufar office dinsa ne yana lalubar numbar wanda ake ajiye kara wajenta
Tana dagawa ya ce" Ki zo office dina"
Bai tsaya ya ji amsarta ba ya katse, ita da kanta sai da ta ji hankalinta na neman tashi dan haka ta mike ta dauki dukan abin bukata ta nufi office din nasa cikin gagawa
Yana shiga ya samu Khausar zaune saman kujera ta jinginar da bayanta, ga abincin da ya kawo mata a ledarsa bata bude ba, sai ruwa dake daf da kafarta da kuma madarar ruwa marar siga dake hannunta bata bude ba idannuwanta lumshe
A nutse ya karasa bayan ya cire rigar dake saman farar rigarsa ya zauna daf da ita yana kamo hannunta da madarar sannan ya bude ledar yana fadin" Ya Salam, baki ci ba? Me yake damun ki? Me ta maki ne? Me ya haɗa ki da ita?"
Khausar ta zuba masa ido, sai kuma ta saki murmushi a hankali ta yi niyar dora kanta gefen kafadarsa da niyar ce masa ba komai ba sai aka shiga neman izinin shigowa
Dama ya bada yana kokarin saka Khausar yin abinda ta yi niya ita kuma ta janye tana gyara zamanta sosai har docter ta shigo tana mai yin salama da fadin " Barka da warhaka Professeur, gani "
TAUFEEK ya sake riko hannun Khausar yana bata damar zama
Sai da ta zauna ya ce"Na je bangaren docter Mufeeda ne sakamakon gannin lokacin da ya dace matata ta zo ta ci abinci ya wuce shiru, sai na tardata tana ta yi mata fada da cewar ta je ta wanke amai, yaushe aka cenzan tsarin asibiti nake son sani da kuma dalilinta na yiwa iyalina haka!"
Daga Khausar din har docter a tare suka kalle shi,sai kuma docter Maimuna ta kalli Khausar tana fadin" Subahanallah, subahanallah, haka ya faru? A'a professeur babu wanda zai cenza dokokin asibitin nan ai sai kai kuma baka cenza mana ba gaskiya, gashi bata zo min da maganar daya daga cikin wa'inda ke aiki da ita ya mata wani laifi ba, koda laifin aka yi mata bata da hurumin daukan mataki da kanta ama bari yanzu yanzu na kirawota sai mu ji, in har wani abin ne ya faru a samu mafita ka yi hakuri, Madame dan Allah zan iya Sannin abinda ya hadaki da docter daga safe zuwa yanzu? Ko nace tunda kika fara aiki a nan?"
Khausar da ta daburce ga kalli TAUFEEK ta kalleta ta ce" Docter dan Allah ki bar maganar, babu abinda ya hadani da Docter na san na yi wani laifin ne dan ba halinta bane gaskiya, kuma koda ban yi komai ba ai ta isa ta sakani aiki tunda gaba take da Ni, Ni dai a bar maganar nan dan Allah, TAUFEEK please bana so a bar maganar nan "
Sosai docter Maimuna ta yi mamakin furucin Khausar, kai , to kuwa a ranta ta idasa yarda ba wancen madame din ta professeur bace, domin wancen din ba aikin likita take ba, kuma dai a yadda doctoci ke dan fadi sama sama haka sun nuna ita din rigimamiya ce sosai, ko ba wannan a wannan yannayin in wata ce ta samu damar TAUFEEK ba wai docter Mufeeda ba kowama sai ya fadawa yan garinsu a asibitin , sai gashi ita tana magana da girmamawa ta kuma nuna an isa da ITANE ya sa aka yi mata magana?
A nutse ta dubi TAUFEEK, dan son ganewa in har yana amana da furucin matarsa, sai ta ga nasa fuskar a hade take bai wani bada damar a soke maganar ba kennan, dan haka ta mike tana fadin " A'a madame ki yi hakuri ai asibitinmu ba gidan tauye kowa bane gaskiya , dole a bi maki hakinki"
Da sauri ta juya ta fice a office din,
Khausar ta zuba masa ido a raunane ta ce" Me yasa zaka min haka? Ka san hakan na iya jaza min rashin zaman lafiya da ita bayan karkashin ta nake?, dan Allah ka ce masu ba komai karma a mata maganar, aikin kasheni zai yi ne? Ko menene zan iya yi mana, haba TAUFEEK sai ka sa a tsaneni cikin abokan aikina"
Banza ya yi mata ya fitar da abincinta yana faman ta ci, domin ba zai iya ce mata komai ba sai tension dinsa ta sauka, sai dai ta yi hakuri dan babu wanda zai wulakanta masa ita ya kyale shi, ko waye kuwa sai dai inda ba zai iya ba ya fadawa Allah wato iyayensu, bayan su baya tunanin zai yarda wani ko wata ya wulakanta masa mata, in tana da laifi ok zai san yadda zai bima abin, ama fa a yadda ya san matarsa bata da wani laifi karya ne kuma a wukakantata a wajen da ta isa !
Yana faman ta cin ita kuma ta dage sai ya yi kiran docter Maimuna yace a bar maganar aka sake neman izinin shigowa
Dan jim ya yi dan ya tabbata sun masa zuwan taron dangin nan kamar yadda suka saba in ransa ya bace a kan daya sukan zo ne baki dayansu a bashi hakurin abin, gashi shi rigimar yake so a yi gaskiya dan an fa tabo shi
Da kyar ya bada damar su shigo
Ai kuwa kamar da wasa doctors suke shigowa karshe docter Mufeeda ta shigo kanta a kasa idannuwanta har sun haye dan kuka domin ita ta gama YANKEWA cewar korarta zai yi, saima da ta ga docter Maimuna hankalinta ya idasa tashi, docter ta mata tassss ta mata fadan hakan dan bata da wani dalili sannan ta sakota gaba da manyan likitocin dake iya tankwasa shi a bashi hakuri, a nan ta sanar masu kaf cewar matarsa ce, Docter Mufeeda ta wulakanta
A yadda yake zaune da cokali a hannunsa yana rike da hannunta daya bai cenza yannayi ba, bayan sun shigo dinma kallo daya ya masu ya sake duban KHausar ya ce" Ha mana bada na son gardama ba zaki ci abincin ba?"
KHausar ta tsare shi da kallo tamkar zata saka ihun kuka
A raunane cike da rikicewa ta ce" Ni zaka ma haka ko? Ni ko?" Sai ga hawaye sun bale mata ta sada kanta tana jan ajiyar zuciya
Docter Maimuna ce ta saki murmushi gannin ya maido hankalinsa kansu ya harde yatsunsa yana kallonsu
Docter Aliyu ya yi murmushin shima ya ce" A gafarcemu professor, in sha Allah laifin da muka aikata ba zamu kuma aikata makamancin sa ba, a yi hakuri
Nan kowane idan ya budi baki hakurin ne yake badawa har aka zo kan Docter Mufeeda
Tana fara magana itama sai hawayen ta sada kanta ta ce" I'm sorry sir, in sha Allah ba zan kuma ba, Madame ki yi hakuri ba zan kuma ba"
KHausar ta girgiza kai da sauri , a hankali ta ce" Docter Walahi ba nice na hadaki da shi ba, Ni saima da nace ba komai , babu abinda kika min, dan Allah ku yi hakuri "
"KHausar ya isa haka tashi ki shiga ciki" taufeek ya fada a tausashe yana kallonta
Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta mike ta nufi cikin ta rufe
Yana kallonta ne har ta rufe din sannan ya sauke ajiyar zuciya Sai kuma ya maida dubansa kansu ya basu damar zama sannan ya ce" Ya wuce, ba a kan Matata kadai nake iya yin haka ba, a kan kowa ne idan har na ga rashin adalci zan tsayawa ma'aikacina, kamar yadda kuka sani babu wanda ke raina ku, hakanan babu wanda zai wulakanta na kasa da shi dan Allah ya bashi dama, dan kina babba a wajenta nima baba nake a wajenki, ba wai maganar kina aiki karkashina ba a yau in sakamaki na yi du inda na hadu da ke ina iya cin zalinki, kin fahimta? Ina iya mayar maki da rayuwa cikin kunci in na so takuraki!"
Su Dukansu dai hakuri suke ta bayarwa har ya gama fadansa ya salame su, sannan ya sake tarda KHausar wace ta cika ta cika sosai, yana shiga suka haura sama sai masifa take tana fadin yana son hadata da abokan aikinta , shi kuwa ya ringa bata baki cikin tausasawa har sai da ta shawo kanta ta sauko ta ci abincin sannan ya dauketa suka yi gida domin ya kula ba lafiya gareta ba sai tare kai take yi kuma ta ki yarda ya dubata tace juwa ce kawai dama tana yi in bata ci abinci a kan lokaci ba
Koda suka je gidan wajen Mama ta je ta amshi jibda ta koma bangarenta ta shaka sosai, tana sakuwa ta sauko ta shiga kicin ta shiga girkinta hankali kwonce har ta gama ta koma dakinta ta kimtsa ta haye salayarta
Kwonci tashi cikin Yumnah karra girma yake yi , inda ta karra ɗorawa kanta abubuwan da take gannin zasu fisheta, domin halaya raguwa dai suka yi ama ba barin su ta yi ba, dan kuwa koda ya nuna mata maganar kaura ita dake fatan a fidata daga gidan saboda takurar HAJIA a da, a yanzu ta ce ai ba inda zata je tana nan a dole aka shiga tada gini a dayan bangaren dake da fili dan KHausar ta koma, domin ya fada mata tunda ta ki komawa wancen gidan a nan din zata yi ta zama har yadda Allah ya yi
Sanadiyar ginin nan da ake kyankyarawa matan mahaifinsa suka tada rigima ta mamaki, dan kuwa karara HAJIA Nawarah ta nuna uba fa ba na shi kadai bane, su da suke da mata ai su ne ya dace a ringa yiwa gurno mai kyau ba mutun baba kamar TAUFEEK ba wanda yake da shi kudin ama dan bakin ciki yana gindin na uba dan kar yan uwansa su samu
Allah ya taima tsakaninsu matan da uban ne suka yi rigimar HAJIA bata sani ba shima TAUFEEK bai sani ba har aka gama ginnin aka kwaso kayan KHausar aka gyara mata bangaren ya zuba dukan abinda ya dace wanda zata rayu cikin walwala kamar yadda wancen bangaren ya malaka, kuma nan dinma dakunna ne har biyar kamar cen da kicin da komai Masha Allah
Washe garin ta tare sai da Yumnah ta wuni gidansu, sai dai bata samu yadda take so ba domin ta tarda mahaifinta a gari yama na yi ya tarkatata ta koma gidanta da nasiha da tsaraba irin ta iyaye ga cikinta ya fito sosai dan a yanzu ya yi girman da ta kusa shiga watanta na haihuwa
Bangaren KHausar tana rayuwa a cikin wannan familly ne tamkar tana rayuwa a familynta domin a watanni bakwai da ta yi a cikinsu zata iya cewa Alhamdulilah,dan kuwa tana ba duk wani wanda ya girmeta girmansa kuma tana kiyaye duk wata fitinar da za'a ce itace sila, tun daga kan HAJIA baba kuwa har auta ba zata ce ga wanda ya mata ido da ido ba, domin su auta idan mamansu ta fita fit suke su je bangarenta in tana nan su yi kallo su dan taba fira, dan irin yadda take jansu a jiki sun fi sakewa da ita fiye da Yumnah, domin Yumnah Akoy tsare gida, kuma tunda ƴaƴansu ya kara auren nan har iyayen nasu take baya baya da su , tana zuwa ama ba kamar da din nan ba da take zaunawa su yi ta sake sake tsakaninsu, domin yanzu har Mama tana zuwa ta gaisar sai dai babu wani abu tsakaninta da Maman bayan gaisuwar wace ta maidata kamar dole ne ba abinda ya dace ta yi bane dan isar abin a duniyarta, haka kuma tsakaninta da KHausar ido ne in sun hadu KHausar din na mata Salama takan amsa a takaice Shikenan dan kuwa bata tunanin zata iya yin wani dogon zumunci da matar mijinta!
Tsakaninta da mijinta ne kawai tafia ke tafe ta fahimta da kokarinta na itama ta samu fuska yadda ya dace, Allah ya taimaketa shi din mai son kare hakokinta ne sai take samun kwonciyar hankali harda rigingimunta yakan Saurara ya kuma bata lokacinsa, sai abin ke kayatar da ita , ama a lokacin da ta so nuna ita zata je sabon ginin