Showing 75001 words to 78000 words out of 186303 words

Chapter 26 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18759

nufin nan ne bakin suke su su takwas cif kennan


Lokaci daya Gabanta da nasa suka buga, Bugawa mai tsananin gaske


A hankali ya lumshe idannuwansa ya kai hannunsa na hagu ya dan sosa gefen hancinsa sannan ya sake daure fuskarsa tamau tamkar bai taba sannin wani wai shi daria ba a lokacin da ta kai hannunta na dama ta murza idannuwanta ta sake murzawa ta bude su tarrr a saman fuskarsa da matsanancin mamaki ta budi bakinta tana dan kokarin mikewa duda rawar da jikinta ya karra kwasa tana kallonsa ta ce""''


























😌😌😌😁 Mun shiga uku😀😀😀😀


*wollah in fada maku na ci waya, sai dai a yi hakuri har mu samu daidaito da ita ko na cenza wata, thank you*








πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”πŸ˜”
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”β€β€πŸ©Ήβ€β€πŸ©ΉπŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”β€β€πŸ©Ήβ€β€πŸ©ΉπŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* πŸ’“2️⃣7️⃣



LITATAFAN MARUBUCIYAR


Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicΓ©
Lait de nuit
Parfums dΓ©sodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*WaΙ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwaraiπŸ’ƒπŸ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuΙ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan MataπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ








Tana kallonsa a saman lebenta ta iya furta" TAUFEEK?"


sai dai mikewar da ta so yi bata samu yi ba wanda ke gefenta ya kama mayafinta ya maidata zaune saman kujerar kamar wani wanda ya santa ko suka yi sabo da shi, shi kuwa tunda ya zauna addu'a ce yake yi a kasan zuciyarsa kan Allah ya sa a dauke su summa su samu wannan dace na kasance ma'aikatan wannan asibiti mai daraja


A hankali ya dauke dubansa ya sake tsayawa cirr a gabansu baki daya kafin ya bude bakinsa
Cikin gogagen turanci, turanci irin na gogagun wa'inda suka koye shi har suka so su fi mai kora shafawa, watau su fi turawan iyawa domin nasu turancin na haihuwa ne sukan iya yinsa yadda suka yi niya koda basu ba komai hakinsa ba


Da salama ya fara yi, wata salama irin ta nagartatun yan gayun nan, sannan ya fuskance su ya shiga bayanin abinda ya tara su a wajen


Ba alamun wasa ko zolaya a tsakaninsa da su ya ce" Kamar yadfa kuka sani a wajen aiki bana wasa bana son a min wasa dan abu kalilin na iya aika mutun kiyama idan har ka yi wasan, hakan ya sa nake aiki ba sani ba sabo, in ka iya mu yi, idan baka iya ba ka koma ka koya!, Ina fatan du kun san haduwar nan na daya daga cikin abinda yake wajibi a garemu du karshen wata? "


Kusan a tare suka amsa da yes sir
Hakan ya saka shi dan yin murmushi sannan ya juya ya koma wajen abokan aikinsa ba tare da ya sake furta A ba


A lokacin ne Chef ya karaso gabansu ya dora daga inda ya tsaya ta hanyar gabatar masu da wanene shi, watau shi wanda ya tsaya ya yi magana a gabansu a yanzu da kuma sauran ma'aikatan da suka shigo tare


A hankali suka shiga gabatar da rabe rabe dan kowani Likita da wa'inda zai yi evaluer , shi kuwa yana tsaye gaban teburin nan tsayuwa irin ta watsa kafa kadan, hannunsa na hagu cikin aljihun rigarsa ta likita wace ya kai sau uku Chef na sake kallon yannayin nan da alamun mamaki a fuskarsa, domin haka din nan da sir ya yi shine da kansa ya hanna cewar ina likita ina tsaye tsayen saka hannu a aljihu idan Kanada abin yi gwara ka yi da ka zo kana tunani a kan aiki, sai kuma ya ga ya dan dantse lebe sannan ya saki, hakan ya tabatar masa ko menene yau sir akoy abinda ya tabo shi ko yake shirin tabo shin


Mintina Ζ™alilan macen ta sanar masa sun daidaita komai, dan haka ya karasa shima wajen zamansa ya zauna sannan ya sake zuba ido sosai da sosai a kan harkar aikin


A hankali ta juyo dubanta daga kansa ta kalli Wannan bakon da suke tare a lokacin da ya rage muryarsa ainun ya ce " sister ko dai baki da lafiya ne? Na ga tun dazun kin yi wani iri kuma sir kike kallo, ki dan maido hankalinki nan idan an gama da su za'ai mana kuma mu fa shine zai yi mana ance baya bari wani ya daukar masa ma'aikata sai ya gamsu da iyawarka yake daukan ka"


A hankali , kamar wace take koyon juyar da kai ko motsi da kai ta juya daga fuskar bawan Allahn nan ta sake kai dubanta wajen da kwakwaluwarta ta toshe harma take son Sannin wanene wannan bawan Allahn


Ido hudu suka yi, idannuwanta a cikin nasa
A hankali ya sake zuba idannuwan nata tana kallon nasa, da wani duba kamar wace ke son sai ta ga wani abu da ta sani a cikin idannuwansa, sai dai wani yannayi na bacin rai da take karantawa a idannuwan nasa ya sakata dauke dubanta ta juyo wajen bawan Allahn nan wanda ga dukkan alamu zai yi dan surutu dan sunna kuskus da na kusa da shi ne


A hankali ta mika hannunta ta tabo farar rigar dake jikinsa dan ba zata iya masa magana ba, gashi maganar tasu kamar ta kurame ne dan ba mai daga sautinsa kowa na dan abinda ya fi tsaye masa a rai ne cen ciki ciki kamar munafukai


Muryarta a shake ta ce" To ama, wannan din wanene shi?"


Ido ya dan zarro da dan mamaki a kwonce saman fuskarsa ya ce" Baki san professeur Mai kwano ba?......."


Gabanta ya yanke ya bada wani irin karan da kunnayenta da zuciyarta ne kawai suka iya ji


A hankali ya ce" Ama bakya kai ziyara manyan asibiti ko?, Wannan yanzu baki sanshi ba a matsayinki na likita? Ai ko patient sun san shi, dan da kika ganshi nan a kasar nan shine yaron da ya fara zama professeur a fannin aikin zuciya da kannanun shekaru, dan yadda mahaifiyata ta fada min a shekara talatin da takwas tuni ya fito a rikake jajirtacen likita, ke dai Allah ya sa munada rabo , in muka samu an gama...."


Da sauri ta kifta idannuwanta, shekara talatin da takwas....., No ba TAUFEEK dinta bane, ba nata bane, TAUFEEK dinta ai shekarunsa dududu basu wuce talatin ba, kuma TAUFEEK dinta dalibi ne, bayan wannanma yau ta san TAUFEEK da har zai bace mata????....., Dan haka da har kwarin gwuiwa ta ce" Wai meye sunnansa complet"


*"Mai kwanoni ELHAJ Zakari Muhammad TAUFEEK"* ya fada cike da begen sunnan kansa yana kai dubansa bangaren da TAUFEEK din ke zaune


Da sauri ya dan zarro ido ya juya ya gyara zamansa yana kimtsa kansa Ι—an sai ya ga kamar su Sir ke kallo


Tunda ya fadi sunnan nan, na mutumen da ta sani a matsayin TAUFEEK ZAKARI wanda sai daga baya bayan shekaru biyu da sanninsa ta san d'a ne a wajen Mai Kwanoni har ta san gidansu ta san ahalinsa sai kanta ya fara hade mata abubuwa sala sala ta yadda ta shiga tunani mai tsauri da nisan gaske har ta daina jin motsi da fahimtar abinda ake yi ta afka a tunanin me kennan? Me hakan yake nufi kennan? Menene wannan din kennan? TAUFEEK dinta? TAUFEEK din da iyayenta suka sani matsayin baban amini kuma abokinta?, Taufeek din da sai dai ta daki kirji ta fadi wanene shi wa duniya? TAUFEEK din dake kare mutuncinta su hau sama su fado su shirya? Taufeek din da yake tamkar wani babi na rayuwarta wanda take jin ba zata iya shaΖ™ar numfashi ba tare da zumunci da shi ba?, Shi din nan da a cikin sirrin rayuwarta wanda Mamanta bata sani ba shi ya sani? Shine tsaye cen a matsayin bako sabon bako a duniyarta da rayuwarta baki daya?
Sai Khausar ta tsinci tunaninta na hade mata , domin tashi daya sai ta shiga tunanin to anya a tarenta da shi akoy abu daya da ta sani gaskiya? Kar aje ahalinsama da ta sani ba nasa bane, kar aje Mama ba mamansa nace, kar aje Hajia ba kakarsa bace, kar aje, kar aje kar aje.................... Harta shi din kansa lokaci daya tsoro ya shige cikin zuciyarta cewa kar aje aljani ne ya shiga jikinsu ita da iyayenta yake mu'amalar zumunci da su....., Kai hatta rashin samun mijinta sai da ya gifta a kwakwaluwarta cewar kar aje to aljanun a jikinta ne suke??......babu dai abinda bata saka a ranta ba, wa'inda burinta ta samu kanta gaban mahaifiya, mahaifiyarta kadai ce zata iya warware mata wannan rudani da tashin hankali


Ta matukar shagala a tunaninta ta ji an sauke hannu kan hannunta


Da sauri ta kalli wanda ya tabata, wannan suarayin dai ne, watau ta tabo shi dazu shine shima ya tabata yanzu tabawa irin wannan domin hannunta ya taba kai tsaye sannan da ido ya mata alamun ta mike mana


Mikewa ta yi, kaffafuwanta na son gaza daukarta ta zuba dubanta a kansu su biyu


Shi sir din, sai likitar mace wace ke sanye da farin glasss fara kal da ita da hakoran makarta biyu sai walwali suke ta dan zubawa yannayin Khausar din ido ta ce" Lafiya kike?"


Khausar ta hadiye wani irin yawu mai wuyar fasara kafin ta iya amsawa cewar kalau take


Kacokam ta maida hankalinta kan likitar nan, wace ta fara yi masu Barka da zuwa cikin mutuntasu ba da wulakanci ba, sannan ta shiga kwatanta masu yadda nasu gwajin zai kasance, yau rana ce ta farko zasu fara amsa tambayoyi ne a kan theori zuwa gobe wa'inda suka wuce sai su samu damar zuwa gabatar da pratical dinsu


Sosai suka bata hankalinsu, cikin nutsuwa a tsayen nan tamkar tashin hankali ta ringa jefo tambaya sai ta zabi wanda ta yi niya ya bata amsa, a kadan sai ta maka tambayoyi kusan goma kana bada amsa shi kuwa yana tsaye yana bi da kallo yana kuma rubutawa a wani litafi a hannunsa har aka zo kan khausar


Cikin ikon Allah a Tambayoyinta daya ce kawai bata amsa ba, itama ba sanninta bane bata yi ba, asalima shi likitan shine ya mata tambayar cikin Muryar nan tasa ta tsare gida da harare harare irin na manyan mutane a waje din nan , sai kawai ta samu kanta da zubawa fuskarsa ido har sai da ya cire nasa duban ya ba likitar damar yi mata tambaya sannan kiri kiri ya dora bata bada amsar wannan tambayar da ya yi ba


Ita dai likitar Tambayoyinta take yi har suka gama da su sannan aka umarcesu kan su je cafetariat su karya, zuwa karfe uku su dawo su duba sakamakonsu , du wanda ya samu gobe karfe bakwai ya samu isowa dan fara aiki


Da wannan suka fice, har ta kusan fita ta sake dakatawa ta juyo, yanzunma ita yake kallo, da kallon nan nasa wanda idan tana masa fada yake zuba mata ido ya yi ta binta da shi


A hankali ta lumshe idannuwanta wasu irin hawaye suka nemi saukowa daga gurbin idnanuwan nata


Da sauri ta cire kanta ta fice ta bi ayarin sababin mutanen da za'a daukan suka sauka


Sam Khausar sai ta kasa binsu wajen cin abincin


Asalima du gaba suka sakata sunna mata tambayar yaya za'a yi ta tsare sir da ido yana magana ta ki bada amsa?, Ta kuwa san wanene shi? Bafa ya son haka, idanma birgeta ya yi ta yi gagawar cire wannan tunanin a ranta dan kuwa tsaf zata iya hadiye zuciya ta mutu tana ji tana gani, domin dubunta sun rasa aikinsu saboda nacin sunna sonsa, wasun na nan cikin wahalar nuna masa soyaya, abubuwa dai gasunnan ba dadin ji a wajenta ita, saima kunya da ta ringa cike dukkan wani gaba na jikinta, a dole ta nuna masu cewar zata zauna a filin asibitin bata jin yunwa, da wannan suka shige suka barta sunna tayata aduar Allah ya sa kar ta jawa kanta saboda ta tsaya wasa a lokacin da ba'a masa wasa




Tana nan zaune sallah kawai take mikewa ta je ta yi a masallacin mata sannan ta dawo ta zauna har suka haura suka dubo result din, cikin ikon Allah a cikinsu babu wanda ba'a dauka ba, domin tana nan zaune suka kawo mata result din ta bi da kallo sunnanta ne na karshe a kafe a result din, ta yi dan murmushin yake suka zauna tare sunna dan zantawa da musayar numbo har yama ta yi sosai du suka mike kowa ya kama gabansa


A hankali take tafia, bayan tarin tunani mai kasara zuciya da kwakwaluwa tana tare ne da tarin yinwa da gajiya, dan abincin da ta ci tunda duku duku babu shi a cikinta,


Tsabar a rude take sai da ta karasa wajen ajiyar motoci zata ratsa ta wuce ta tuna tana da dan sahu, dan haka ta rakube jikin wata mota mai numfashi ta ciro sabuwar wayarta yar karama ta shiga kiran mai adaiditar


A kira na biyu ya daga yana bata hakurin bai daga da wuri ba


Murya a matukar sanyaye ta ce" Mun tashi"


Mai adaidaitar ya shaida mata cewa gayanan zuwa


Wayar ta kashe ta dan sake jinginar da bayanta jikin motar tana sauke ajiyar zuciya hadi da sada kanta kasa


A hankali kunnayenta ke jiyo mata takun mutane, da budewar mota da tashinta da tafia, har ta ji kamar ba kowa zuwa yanzun


A hankali hancinta ke son shaΖ™ar mata kanshin turaran da itace ta bashi shi da kanta matsayin gift din aurensa tun daga lokacin idan ya kare sai ya saka ta kawo masa wani bata san dadinsa yake ji ko me ba


Bayan jin kanshin a daf da ita, sai ta fara jin alamun innuwar mutun, sai kuma idannuwanta suka sauka a bakake sidik din takalman Ζ™afarsa sau ciki masu masifar kyau da daukan ido


Da rashin kwarin gwuiwa ta dago dubanta ta sauke a saman fuskarsa, lokaci daya shi ya lumshe nasa idannuwan a hankali ya budi bakinsa ya ce" KHAUSAR......."


Da sauri ta sake bin bakin nasa da kallo..
.., eh Khausar ya fada , ita dai Khausar


A hankali TAUFEEK ya dan sake dubanta ya ce " Khausar Please, ki daina alamun nan na ranki a bace, tun dazu nake kallonki, ki daina min kallon kamar wani bakinki ko wanda ya maki karya, ki tsaya na fahimtar da ke abinda kike tunanin na boye maki kin ji?????"...... Ya fada, da sanyayar Muryar da ta san shi, Muryar da ta san TAUFEEK dinta da shi, Taufeek din mafarkin ta, ko tace aljannin tunaninta


Da sauri ta kuma cire dubanta a kansa ta juya da nufin tafia...............


Taku biyu ya yi ya riko mayafinta, hakan ya sa mayafin nata faduwa gaba daya daga jikinta daga yafen da ta masa


Ransa ne ya ji ya fara Ι“aci, ya bi mayafin da kallo a hannunsa a lokacin da ta juyo da nufin amshe mayafinta ta yi tafiyarta ba tare da ta ce da wannan aljanin ci kanka ba, dan kuwa yanzun zata tafiyarta a kafarta ne ta sanarwa mama a yi gagawar kiran Aba a fada masa ya dawo du inda yake a mata rukiya, dan ta gama yarda ta jima a duniyar aljannu har ta janyo iyayenta ciki bata sani ba!


"Wannan din wace irin banzar dabi'a ce kike son dauka bayan kin san na hanna? Meye ya sa kika yafa wannan abin kika zo har nan da shi? Bayan wannan kika zo kina kallo saurayin nan na taba maki hannu ba zaki iya hannawa ba? Menene wannan sabuwar dabi'ar da ba taki ba? Bafa na son haka kin sani sarai?" Ya fada yana huci daf da ita irin yadda suka saba idan ta bata masa


Gaba daya Khausar sai ta karra tsorata, hawayenta suka bale, sai ta ringa hasko abin ta wata fuska daban.....ta yiwuma bakin aljani ne ya aureta tunda har yana mata kashedin wani ya taba ta


Rai bace ta nuna shi tana zarro idannuwanta ta ce" Ka min shiru malan, ka min shiru ka ji? A'uzubilahi mina shaidanin rajin! Ba alaka tsakanina da kai ba zumunci ba fahimta bale wani abin ya shiga tsakanina da kai! Ka yi nesa da Ni daga yau na gane kai aljani ne ba Ni ba kai! Oh ni ga mahaukaciya ko? Ga shashasha! To ka shani daya ba dadi yau zan fadawa su Mama aljani kake macuci, ka je danginka ka bi ba dai Khausar ba, kuma hijab an ki ba'a sakawa, maganar wani ya riken hannu me kake nufi, kai jinsin aljani zaka rike min? An rike min hannun an kuma ka yi turnukin hayaki ka shakeni na mutu in gani!, Kuma bari ka ji ko a waya na kiranka sai na sauke maka wala ya'uduhu yifzuhma!, Bayan wannan in ka kuma zuwa anguwarmu a siffar dan Adam dan annabi sai mun tara jama'a mun kone ka, shirme Ni zaka haukata? Wa bilahilazi baka isa ba!" Ta karashe fadi tana wartar mayafinta da dukkan karfin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login