Showing 45001 words to 48000 words out of 186303 words

Chapter 16 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18775

ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃














Dan juyowa ya yi da alamun a dan kagauce yake ya ce" Hajia ki bani mana ya haka ina ango sai kin sa na je a lati an zane ni?"


Dariya maganar ta bata, dan haka ta karaso tana fadin" Ka ga wani sako a wayarka, na san wanda ya turo yana cen yana jiran amsa bai san TAUFEEK NAWA ya turowa sakon ba , ba wani ko inspector ko me ba, inspector fa, kai mu dama mu kurayi numbar a mana hanyar ganninsa ka san wane ake nufi?"


Wayar ya cafe dan ya ga number take son fitarwa dan ta yi kira , da yan yatsunsa ya mata alamun ta koma mana, sannan ya tayar da motarsa ya yi tafiyarsa


Komawa ta yi tana zumbura baki , hakan ya saka rukaya saka dariya ta ce" Har an bata ko?, Ni kam ina mamakinku, yanzu za'a ga shawara daya yanzu kowa zai kama gabansa"


Da haushi ta ce" Ke baya jin magana ne, daga cewa a dauki wata numba a wayarsa a yi kira ya wani warce waya, Allah na tuba da ace banida waya sai na ji haushi, sai me wata wayarsa uwa ta munafukai ba komai a cikinta , kin ga banma fada masa turaransa ya dawo ya amsa gobe ba ya bata min rai"


Mama ta girgiza kai tana mamakin itama shirmen Khausar ta ce" To ai goben kwa hadu dole kim manta yace gobe ne zaki fara fita aikin? Kai har gadin abanku nake ya zo da wuri yau ya ga abin arziki, Allah mun gode maka da tarin ni'imomin da ka yi mana, ya rab yadda kake fito mana da hanyoyi ba da tsumi ko dabararmu ba ka nunan auren ya'yan nan lafiya, ubangiji ka sakawa bawan nan naka da ahalinsa da alkhairi, in ba hanya ba ta yaya kai tsaye zamu haka ? Babar asibiti fa, ai kam mu sai yi khausara da allura"




Dariya yan matan suka saka dan yadda Mama ta nuna Khausar din zaune an cire hijab za'a sake alwalar sallar isha
Rukaya ta ce" Mama, Allah ya sa mabudin dukkan wani alkhairinmu kennan"


Mama ta ce" Amen ya hayu ya kayum Rukaya, bi'izinilallah alkhairin kennan"


Da wannan suka cika daren ranar, domin da Aba ya dawo tare da auta aka sanar masa alwallah ya daura ya haye darduma ya shiga yiwa ubangiji kirari da fatan Allah ya nuna masa sauranma sun samu alkhairai a rayuwa ya nuna masa aurensu




Yauma TAUFEEK ya cika dare sosai, domin ya shantake a wajen abansa ne sun sha hira daga nan kuma ya je wajen Hajia ta gama masa turare turarenta wanda a dole sai da ya je ya yi wanka ya cenza kayansa domin a tunaninsa bangaren Yumnah da baki ba zai je haka yana kauri uwa dan bori ba


Yau dinma da hannunsa rike da tsaraba ya karasa bangaren nata
Sai dai abin mamaki tunda ya tura ya shiga da salama ya fahimci yau din kamar ita daya ce ba bakinsu


Du irin yadda ranta ke bace da gannin rabonsa da ita tunda safe da zasu wuce gaishe da iyayenta da abokansa sai yanzun, ama ganninsa ya saka ranta yin fari, harma ta mike tana murmushi ta nufo shi dan amsar ledar hannunsa


Da dan mamaki ya bi shigar jikinta da kallo, riga da wando ne a jikin nata masu tsarin santsi da dan lafewa a jiki kadan, domin idan ka saka su zasu bi tsarin jikinka ne su lafe


Dauke kansa ya yi a lokacin da ya tuna cewar ai normal ne yanzu mijinta yake dan an tarbeshi a haka daidai din kennan


Yana zama saman kujerar falon yana dan waigawa dan maganar da ya dauka yana fadin" Ina bakin ne? Ko sun kwonta da wuri haka?"


Agogo ta kalla bayan ta dauko farin tawul tana dawowa da jug din jus mai sanyi a hannunta ta karaso tana sakin murmushi a ranta ta ayana' Yar banza ce ni zan zauna 8na zubawa karti ido sunna wuni sunna cikan kunne da iya shege bayan ga dalilina a gefe kunya ta hanna shi tarewa da ni?, Bama zai yiwu ba gaskiya ' a bayane kuwa cike da fitar da harufa a tausashe ta ce" Ai dama kwana daidaya ne zasu yi , kusan magariba bayan sun gama girki suka tafi"


Murmushi ya yi yana amsar jus din da ta zuba masa ya dan kurba kadan sai kuma ya bita da mamaki gannin ta duba ta kamo kafarsa zata dora saman cinyarta


A hankali ya ajiye kofin ya mika hannayensa biyu bayan ya janye kafar tasa yana kallonta da kula sosai ya ce" Hey, yumnah me zaki yi haka ne?"


Yumnah ta zubawa fuskarsa ido, cike da tarin kaunarsa ta ce" safar zan cire maka mu je ka yi wanka sai ka ci abinci Yayanmu"


Dan murmushi ya yi, kwarai hakan ya birge shi, sai dai a tunaninsa a yanzu shine zai fara riritata, ya bata daraja irin nata, ya nuna mata ita din mace ce, koda zai iya amsar irin kula daga gare ta, dan ba zai tashi zikin kato ya sakata irin wahalar nan ba tana amarya, lada ne ai yanzu suka fara ratabarsa, in sha Allah


A hankali bayan ya yi wani yannayi da bata taba ganninsa ya yi ba, yannayi irin na tarin a ji kunyar nan, domin TAUFEEK nata wanda bai cika dogon kallonta bane a yau ya bi rigar jikinta da kallo a hankali ya ce" Na yi wanka ai, sai dai zan so na maki idan Allah ya sa baki yi ba"


Ya salam, tabas maganar ta zo mata s ba zata, shi yasa ta wani irin tsare shi da ido cike da mamaki da tunanin shine ya yi furucin nan? Sai kuma wani madaukakin dadi ya nemi rufe dukkan gaban jikinta da yannayinta
A hankali ta dan lumshe idannuwanta sakamakon jin hannunsa a saman habarta ya dan murza kadan, baban burinta ta sake ce masa eh tana so ya yi mata wankan, dan irin rayuwar nan ita take hangowa kanta da mijinta dama, su zamto tamkar abu daya komai nasu iri daya
Ashe ashe zata iya jin furucin nan daga bakinsa bayan tsoro ya gama mamaye ta cewar wata ta gama yi mata karuwar alaka da miji?


Murmushi ya saki , duda a bayane ba zai ce asalin kunya bane ya cinye harshen Yumnah ba, ama daukewar maganarta ya saka shi daukan cewa hakan ne, dan haka ya ringa jin wani sauki sauki a zuciyarsa, domin shi dai da Allah ya halice shi mutun ne mai matukar son mace mai kunya, yana so a rana irin ta yau da wa'inda zasu biyo baya ya zamto ya yaki kunyar amaryarsa , ya koya mata irin yadda ya fi so su kasance cikin koyarwar islama, a duniya ya tsani rawar kai, da shegen banzan yayi irin na wasu matan da mazan, yakan dora laifin haka a kan Mazan ne domin da ace namijin ya nunawa macen yadda zata daidaita lamuranta to da kunya ta zamto ado a motsinta, yana matukar son koda zawara ya aura a yi yayi irin na jin kunyar junna, wasu abubuwan kuwa yau da gobe suke zamtowa dole a saje, ama wasu matan har su mutu akoy yare mai daraja mai sunna kunya a tsakaninsu da mazajensu, dan kuwa du irin sabawar nan da tarin haihuwa wace ke nunin du wani sirri mai sunna sirrinta ya gama sani ciki da bai zaka ga wasu abubuwan a bayane suke na kunya har ana iya gani, shi din da kansa hakan naniya kasancewa nishadi a gareshi, domin yana iya daukan hakan abin tsokanar iyalinsa idan ya yi ta labe fuska ko ta yi shiru ta sada kai, to fa sai ka ga yana dariya a bayane ......., Yana matukar girmama darajar iyayenmu , ba wai gyaran bane ba'a yiwa maza, ba kuma kanshi bane ba'a shaka masu, uwa uba babu wa'inda suka kaisu iya kirsa da sada kai, kai sun fi yan matan iya juya akalar namijin cikin nutsuwa domin su sunna dauke da wani sirri da suka yarda da shi cewa eh a maganar gaskiyama namiji shine shugaba, a kuma maganar hanyar da zasu iya bi su sace zuciyarsama su nuna masa cewar shi din ne dai shugaban, ko magana ta hada su ta rashin fahimta sukan shanye a lokacin su bada hakuri ba dan sun kyale ba, dan kuwa sunna da nasu hanyoyin nuna maka kaime ya dace ka bada hakurin nan fa, harma ka shiga bayarwa ba tare da ka gane hakuri kake bata ba..... Abubuwa ire iren haka dai, shi shine burinsa, shine muradinsa, muhali yake so da rayuwa cike da kula da kare hakoki irin na adininsa da kuma al'adar malan bahaushe, ba rayuwa irin ta turawa ba ............
Da wannan tunanin ya mikar da ita suka karasa wajen diner ya ja mata kujera ta zauna sannan ya ja ya zauna yana dan sakar mata murmushi a lokacin da ta mike tana kokarin zuba masa abincin


A nutse ya ce" Kadan zaki saka"


Ta kuwa zuba kadan din, sannan ta zuba natama dan kadan sosai, dan ta riga ta ci tun kafin ya shigo, an fada mata cewar kar ta ringa hadama a gabansa


Da kula a lokacin da ya fara ci ta ce" Na zata zaka shigo da wuri yau?"


Bai bata amsa ba sai da ya gama cin abincinsa a nutse domin dama ba yinwa yake ji ba, ama gudun kar ya shiga hakinta ya saka ya amshi abincin


Da kula ya dubeta ya ce" Eh na dan yi wasu uzuririka ne, ama da wuri na shigo daga gidan su KHausar"


Cokalin dake hannunta sai da ya kusan fasa plate din da take dan cacaka sanadiyar caka shi da yan yatsunta suka yi da dan karfi


Hankali a dan tashe ta ce" Khausar kuma?"


A hankali ya dan bi yannayinta da kallo


Idannuwanta ta kikifta tana fadin" Me ya jadaka da gidan su KHausar yanzun kuma?, Bayan gani? Ina tunanin a yanzu ai ba Khausar tsohuwar mace ba ko yarinya sabon jinni ce ba zaka kula ba tunda kake da amaryarka a gefe sabuwa fill ko? A tunanina zuwa yanzu ko Khausar ta yi kiranka ba zaka amsata ba tunda gani ko?"


Ba da hatsaniya ko ihu ya yi furucinta ba, dan bata taba yi masa magana da ihu haka, tunda ta taba kwatantawa ya nuna mata aa, ba zasu fara haka ba, take kiyayewa,
Sai dai ko a hakan a bayane tsagwaron tsanar sunnan wace ta yi magana a kanta ya bayana ba a rufe ba


Da mamaki yake kallon fuskarta da ta dauki ja nan da nan
A hankali ya kai duban nasa kan hannayenta da take aukin murzawa kamar zata fitar da yan yatsun daga jiki, alamu na a haka din tana dane kanta ainun daga abinda ke zuciyarta


Sosai mamaki ya cika masa zuciya


Me ya hadata da Khausar mai zafi haka?


A sanninsa sunna matukar jituwa tsakaninsu, dan sha nawa zasu samu matsala ita da shi ta samu Khausar din da maganar ita kuma ta ce sai a shirya , ya yi hakuri kuwa su shirya din?,
Khausar dai Khausar dinsa ce take nufin a yanzu dan ya aureta du wata alaka zata kunce tsakaninsa da ita?
Tana nufin ko wata aka bashi kennan ya mu'amalanta ko mene? Subahanallah shin yarinyar nan bata da wayo ne ko akoy wata a kasa tsakaninta da Khausar?


Idannuwansa ya lumshe a hankali yana mai aro nasa yannayi idan ransa ya baci gudun kar ya yi abinda zai iya zuwa ya dawo, watau yin shiru wa abinda ya bata masa ran, rashin tankawa a lokacin har sai ya ji zuciyarsa ta yi sanyi


A hankali ya mike da tissu a hannunsa ya wuce ya barta a nan zaune ba tare da ya ce uffan wa maganarta ba




A rikice ta juyo ta raka bayansa da kallo har ya bacewa ganninta, sai dai abinda ya dan sanyaya zuciyarta ba waje ya fita ba, aa, ciki ya shige ta hanyar hawa sama




A nan a zaune tun tana saka tana warwara har ta ringa gannin kamar ta yi wauta ne ko menene? Kamar ta yi gagawa ne ko menene? Haka kawai zuciyarta ke son nuna mata ta yi azarbabi ita da ya dace ta bi a hankali ta raba wannan banzan tsakanin sai gashi ta yi magana wata iri bayan ta san yana son a ringa tausasa harshe?
A hankali ta dafe kanta dake sara mata ta shiga zubar da hawaye msu zafi
Shin da wani harshe zata yi kwatance a gane cewar a tsorace take
Da wani yare zata yi kwatance a gane irin zafin da take ji a cen kasan zuciyarta?
Itace ke wahala, ta fi kowa shiga wani hali a kan mijinta a kan maganar kawarsa
Wai kawarsan ce ta kasa yarda cewa kawarsa ce
Shin wani abu take bashi wanda ita bata iya bashi ne?
Du irin kwaliyarta da zumudinta sai suka dakushe, domin babu abinda ya fi daga mata hankali irin ta ga nasa ran a bace koda wani ne ya bata masa bale ita da kanta
Jin kanta zai tsage ya saka ta mike da kyar ta shiga hautawa bata iya koda dauke kayayyakin da suka yi anfani ba, dan so take yi ta je ta same shi ta bashi hakuri


Tana shiga ta tarda shi saman salaya , dan haka sai ta nemi waje ta zauna saman gado tana jira ya gama ta bashi hakuri dan bata tunanin ko zata iya dangana ta iya barci da shi haka ba




Tun tana tunanin zai gama da wuri har barci ya kwasheta


A hankali ya kai dubansa inda take dukunkune ya zuba mata ido, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya ya rufe alkur'aninsa ya kai ya ajiye shi a wajen kilacewa sannan ya haura saman gadon yana sake binta da kallo


Ya yi haka ne dan baya so yanzu yanzu ta dauko masa maganar
Ya yi haka ne dan yana so ya saba mata idan ransa a bace su kiyaye abinda ya bata masan kai tsaye, a bari zukata su huce
Dama bashi da niyar tabata a yau, domin ya fi so su saba a hankali kafin ta san shi wanene shima ya san ita wacece


Sai dai baya tunanin in har zuciyarsa zata iya lamunce masa sauraronta da murya irin wannan da kalamai ire iren wadinnan
Bai san inda abin zai kai iya kaisu ba, gwara su kiyaye
A ganninsa idan wani abu ya hadata da Khausar in ba zata iya zumunci da ita ba, to kar ta zageta, dan Khausar a kulun burinta ta faranta mata, ko anguwa suka fita in ta ga abin yan mata sai tace sai an siyawa Yumnah, itace ta koya masa kyautar soyaya ta fada masa a soyaya fa kyauta ake yi ba'a zama ba kyauta dan kyauta itace mai ciyar da soyaya.......


Murmushi ya yi ya rufa mata sabon blnkt sannan ya kwonta gefenta kadan bayan ya kashe fitilar dakin








*ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA*


Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu.
Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu.
Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda.
Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter.
Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba.
Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726


Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO*


💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔




*DA CIWO A ZUCIYATA*




💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 1️⃣8️⃣



LITATAFAN MARUBUCIYAR


Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login