Showing 111001 words to 114000 words out of 186303 words

Chapter 38 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18788

aka dannan karaurawa aka kuma yi salama ta tabata masu son shigowar manya ne, dan bata taษ“a gannin kaffafuwan yaren gidan a bangarensu ba


Budewa ta yi, sai kuma da sauri ta bada hanya tana amsa salamar


Su Hajia ne suka fara shiga, sannan Mama sai kuma Baban shima ya shigo da suturarsa mai kamala hannunsa da carbi da hularsa a kansa domin shi ma'abocin fita da hula ne ko a cikin gidansa


Mama ce ta fara karasawa daf da Hajia ta duka har kasa tana gaisheta, kishiyoyinta suka mara nata baya , sai uwa Uba Aba ya karaso shima da kuzarinsa ya duka har kasa yana cire hular kansa ya ce" Barka da safia HAJIA, fatan an tashi lafia?"


Hajia ta yamutsa fuska tana kallon TAUFEEK dake kokarin tashi daga kujerar da ta saka shi a gaba ya duka shima kansa a kasa yana gaisar da iyayen nasa , ama babu wanda ya amsa tunda amsar ta Hajia suke jira kafin su iya amsawa, sai ya zamto Yumnah itama a dole ta duka din gannin harda baban a duke gaban wannan mai fuska a haden


Hajia ta sake hade fuska ta ce" Kwana ku kuka ganshi Ni ban ganshi ba, dan kuwa kwana na yi ina fama da jikana, ba lafia numfashinsa da kyar yake fita , hannuna a saman daidai zuciyar magidanci haka kirjinsa ke bugawa , Yaren nan sam bakwa jin tsoron Allah, ban san me yaron nan ya tsare maku ba fa kuka tsane shi, a zo a kama min a kai min shi asibiti kuka kiya kuka je kuka kwonta, wai harda ke da kai, in su Wadinnan basu san zafinsa ba ai bai dace ace harda ku ba, daga yau na san zaman da zan yi da kowa a gidan nan, kuma babu wanda zai yi ciwo mu damu Ni da Magidanci, gaisuwa ku rike abinku bana so, wulakancin banza da wofi!"


Taufeek ya zuba mata ido kasa kasa ya sakar mata harare, ita kuma ta tsuke baki ta ce" Ka harari wannan, kai yanzu du abinda suka maka dan rashin zuciya sai ka ji ciwo in na masu fada ko?"


Aba ya yi murmushi kansa a kasa ya ce" a yi hakuri Hajia mun yi laifi, a yi hakuri ba zamu sake ba in sha Allah, ai jiyan kin ga baki ne basu tafi ba sai dare, masha ALLAH daurin auren kamar da wasa ya tara jama'a kuma aka zauna sosai sai da muka ci abinci aka yi zumunci sannan aka watse"


Hajia ta yi dan shiru sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Ni walahi du sai da abin ya min lami, ita KHausarar fa har kamar zata summa wai bata so, bata son magidanci fa, kuma na taho nan dan in ganshi na tardashi ba lafiya abin sai ya rikitani, auren nan du sai ya shige min, to yaya ka barota ita KHausarar ?"


TAUFEEK da kansa ke kasa , a kasan dai yake, sai dai a bayanin kakarsa ya dan so shiga hali na rudu kadan, Magidanci dai du duniyar nan daga bakin Hajia shi ake nufi, to meye hadin maganar bata sonsa Khausar kuma?


Aba cikin murmushin ya ce" Ai haka dai aka bata hakuri, sosai ta nuna bata so din, ama an rarasheta tunda an riga an daura ai hakuri za'a yi, kuma tsakaninta da Elhaji karamin ai sun fi kusa , zasu daidaita kansu ne bi izinillah "


Yanzun kam dago kai ya yi ya zubawa mahaifinsa ido, hakama du wani wanda ke wajen ama banda Mama wace ke murmushi itama ta diramar mijin nata da sarakuwarta


Hajia ta yi murmushi gannin yannayin TAUFEEK, ta mike tana fadin" Ku karaso mu zauna a yi maganar abinda ya faru jiya, ke yaminah je sako hijab mana in Ni kin rainani kina yawo da rigar nan da hula a gabana Wadinnan din ai sirikanki ne harda uban mijinki ai da kunya ko?"


Yumnah ta zubawa Hajia ido, idan har zata iya zuwa dakinta a irin wannan lokacin ai tana iya zuwa ko'ina ma


Bata tunanin ko zata iya zuwa wani daki sako hijab maganar da baba ke yi ke neman sakata juwa, dan haka ba tare da ta je din ba ta karasa kusa da TAUFEEK ta zauna a saman kafet din kamar yadda ya yi sannan ta zubawa Baba ido wanda ke saman kujera , hakama su Hajia Dukansu a saman kujerar suke


A nutse Baba ya ce" Assalamu alaikum wa rahamatulah, kamar yadda Hajia tace, haka ne, ina son sanar maku ku dukanku abinda ya faru jiya, alhamdulilah daurin auren da muka je da Magidanci aka daura shi , wannan din hukunci ne na Ubangiji, haka Allah ya so, da wannan nake dubanki Yumnah kan maganar, na san me mata ke daukan abokiyar zama, haka kuma ana iya fasarar cewa baki jima a gidanki ba hakan ta faru, ki Kadara cewa Allah ne ya hukunta haka a rayuwarki, dan kin ga Hajia gatanan da mahaifiyar mijinki rana daya na aure su, kowani bawa da irin kadararsa mijinki kansa bai san cewa san daura aurensa da KHAUSAR ba, ita dinma cikin firgicin abin take harda kukan bata so, to gaba daya dai hakuri za'a ba kowa da kuma fatan Allah ya sa KHAUSAR alkhairi ce a garemu baki daya, ban nemawa mijinki auren Khausar dan na ga gazawarki ta kowani fani ba, ban kuma yi haka dan wata mummunar manufa ba, Allah ne ya Kadara ita din matar mijinki ce , ina fatan zaku mana biyayya gaba dayanku ku zauna lafiya"


Hajia ta saki wani murmushin gannin irin zazaro idannuwan su Hajia nawarah da ita din kanta Yumnar, Mama kuwa kanta a kasa dama bata dago ba, dan bata da ta cewa a taron da bayanin


TAUFEEK kallon fuskar mahaifinsa yake yi tamkar ya ga bako a duniyarsa, Hajia ta gyara zamanta ta ce" To hakurinma da kake badawa Ni ban ga laifin da aka yi ba, aure fa aka ce, in ba'a yi ita aka aurota? Kawai dai batun kishiya ne ba dadi ama in ta yi duba da khausara ai dama kishiyarta ce ba yau ba sai ta ba kanta lafiya a zauna lafiya, magidanci kuwa Ni dama ina hango shi a mace hudu ne, dan in ka yi duba da auren nan sunna ce ta ma'aiki, jikana kuwa baya tsoron uban kowa bale ya ki jera hudu ana masa cenji cenjin tukunya yana rayuwa tamkar da Sarki wannan shine more rayuwa, itama Khausarar da take kukan bata son shi zan koma ne, na sameta , babu mai hannani wanka mata mari a kan magidanci!"


TAUFEEK a hankali ya maida idannuwansa ya lumshe , daga zaunen da yake ya gama gane Yaren mahaifinsa da kuma kakarsa, ana nufin cewa auren da aka daurawa Khausar aminiyarsa a jiya da shi ne aka daura shi?


Idannuwan nasa ya so budewa a hankali, sai dai da sauri ya bude su sakamakon faduwar Yumnah saman kansa rana jan numfashinta da dukkan karfinta hannunta a damke da rigarsa tana kallonsa a hankali idannuwanta suke rufewa har ta rufe su ruf still tana jan numfashin nan da kyar tamkar wace zata bar duniya


A rikice du suka mike, Bama kamar su Hajia Nawarah ba sunna Salalami , dama tunda Baba mai kwanoni ya fara bayanin nan suka kasance a kololuwar mamaki sunna binsa da kallo sai zubewar Yumnah ta saka su mikewa sunna neman daukaka abin fiye da misali


Hajia ta rafka salatin itama tana gannin yadda su Hajia suka talafo Yumnah ama ta ki sakin rigar TAUFEEK, haka kuma numfashinta da gaske sama sama yake yi tamkar wace zata summe
Da tarin al'ajabi Hajia ta ce" Wai summa ta yi? La ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam, summa ta yi daga mata abokiyar zama ko me ?"


A tausashe TAUFEEK ya kalli Hajiar kasa kasa ya ce" Ki daina ihun nan mana ki yi a hankali bakya gannin halin da take ciki?"


Hajia ta yi tsuru tana kallon yada yake magana da wani yannayi na lisilama, sak kamar munafuki, in ba mantawa ta yi ba dazunma da tana bashi abinci ai magana ne ya kasa kuma ya kasa ci da kansa ko? Yaushe ya samu lafiyar talafar wannan tabaryar har yake son mata iya shege?


Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce"


























Alhamdulilah, mun fa dawo, sai fatan Allah ya bamu ikon yin typing lafiya, ya kuma bamu ikon farantawa junna


*DUBUN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI ZUWA GAREKU YAN UWA DA AMINAN ARZIKI, SPCLY SAJIDA PALACE, MEMA ZAN CE? TA INA ZAN FARA? A INA ZAN SAUKE? ADDU'A ITACE TSAKANINA DA KU DA FATAN ALKHAIRI, KUN YI RAWAR GANI NA MAMAKI, KAMAR YADDA KUKA SABA KUN YI MIN ALKHAIRI FIYE DA TUNANINA, ALLAH YA SAKA DA MAFIFICIN ALKHAIRI, ALHAMDULILAH Y'ARKU NA GODIYA, ALLAH YA BIYA, WA'INDA SUKE TAMBAYANA DALILIN SHIRUNA DA YAWA KU YI HAKURI HAIHUWA NA YI SHI YASA, WA'INDA BAN AMSAWA BA KU GAFARCENI , WALAHI MSG DIN DA YAWA SOSAI FA, INA FATAN ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MUKU A DUK INDA KUKE, KUN SHIRYA JIN ME ZAI FARU A RAYUWAR KHAUSARA YAR GIDAN ABA DA AMININTA DA KUMA ABOKIYAR ZAMANTA? ME ZAI FARU TSAKANIN MAMA DA ABOKANAN ZAMANTA? MU KAFTA PEOPLE๐Ÿ˜Œ๐Ÿ˜Œ๐Ÿ˜Œ*




๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 4๏ธโƒฃ3๏ธโƒฃ


*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*


1: Duk karyar kada


2: Yar mahaukaciya


3: Neman na kaina


4: Bani da zabi


5: Bak'a ce


6: Kutkale


7: Makauniya ce


8: Mage


9: Duk nisan jifa


10: Idan ka raina inda kake


11: Dutse


12: Alkalamin kadarata


13: Bani da zabi


14: Dakika Biyar


15:Wata kokowar


16: Aure yakin mata


17: Ni zan ladabi


18: Daga tafia daukar soja


*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ








Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce" Subahanallah, yaya kun ririketa kun gaza dagata, dagata TAUFEEK mu je asibiti dagata mu je"


Mama dake tsaye tana jiran gannin su Hajia in kamata zasu yi su kamatan ama sai wani daukaka abin suke ne, Hajia baba kuwa dama hannayenta biyu a kirjinta banda harara babu abinda take makawa magidanci dan bata taษ“a tunanin zai samu karfin tare wannan matar ba shi da ba lafiyar kirki ne da shi ba?
A nutse mama ta dan matso ta ce" Hajia dan gyara in gani"


Hajiar ta dago ta dubi Mama, ta ga Maman sosai fuskarta a hade, abinda bata taษ“a gwadawa ba, kai abinda ya shafi magidancin nema Maman tana matukar nuna kara da kauda kai, da dan mamaki ta matsa din ta bata waje


Da kula sosai Maman ta ce" Sai an kaita asibiti ne? Numfashin nata nake gani sama sama Elhaji?"


Shi da kansa ya yi mamakin wannan lamari na mama duda halin da yake ciki na rabuwar tunani da kuma matarsa mai dauke da dan tayin cikinsa dake kwonce saman jikinsa idannuwanta a rufe ruf tana kokowa da numfashinta, da kula ya ce" Yumnah, Yumnah hey......"


Mama ta duka daf da su sosai , da kula ita dinma ta dafa bayan Yumnar a hankali tana dan shafa kanta ta ce" Daughter, Please calm down, kin san halin da kike ciki kar ki janyowa kanki wani ciwo a kan abinda ya riga ya faru, Please calm down...."


Hajia Baba ta sake yin KISKIRIM tana bin kowa da kallo


Baba dake tsaye ya bi Hajia Fatahiya da ido wace ta fita tana dana waya cike da basar da uban kowa, wayar Tata kuwa ba kowa take nema ba sai uwar Yumnah, domin tsabar bin salsala irin na kuturta bin dan aboki har numbar junna ne da su sunna zumunci irin nasu


Baba ya ce" Ka dauketa mu je asibiti ba wata kama ce da ita ba?"


Sai yanzu TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya , shi kokarinsa na gannin ta daina jan numfashinta ne, ama firr abu ya gagara , dan haka ya mike tsaye tsaf da ita a jikinsa tamkar ya dauki yar jaririya ya juya ya nufi hanyar fita da ita dan bin umarnin iyayensa cewar a sadata da asibiti


Hajia ta rafka salati harda talabe haba, tana biye da su ta dan riko hannun baba ta ce" Ka san wa bilahilazi yaron cen dazu sai da na masa dan jagora na fitar da shi daga dakinsa na sauko shi kasa na bashi abinci, dan sak yace da Ni baya gani jinninsa ya hau, ka ga wannan abar ta suma ya dauketa, to ko dai Mayu suka rike shi kuma yanzu suka sake shi da na yi da gaske?"


Baba mai kwanoni ya yi murmushi ya ce" Hajia ai saukin dai ya samu ne kawai, Allah dai ya tsare gaba"


Har kusan babar motarsa suka karasa Mama ta bude bayan motar ta shiga ba tare da ta bada damar wata zata rakata ba ta masa alamar ya sako Yumnar


Hajia ta zagaya gidan gaba ta bude ta shige tana fadin" Mika mata ita mu je, bayanin dan tayin nan ya fi komai tsaya min a rai mu je , sai mun dawo "


Baba mai kwanoni ya yi murmushi bayan motar ta fice a gidan, watau sosai ya yi mamakin mahaifiyar TAUFEEK yau gannin idonsa itace ta yi gaba da lamarin yaronta, ya kuma ji dadi mai girman gaske, sai kuma TAUFEEK din dake hade girar sama da ta kasa na rashin kunya


Sunna isawa asibitinsa kamar yadda dokar wajen take idan har aka kawo daya daga cikin dangin wani ma'aikacinsa, Wada suke da kusanci sosai kama daga mahaifiya, mahaifi, mata, ya'ya to ba za'a duba marar lafiyar da mutumen ba dan gudun rikicewa da sauransu , dokar kuma na kan kowa ne ba iya ma'aikatan ba, har shi mai wajen, dan haka sunna isawa aka dorata a kujerar tura marar lafiya aka shige da ita bangaren emrgency, shi kuwa ya zauna a office din doctern dake aiki a ranar a hankali ya jinginar da bayansa bayan doctern ya fitar masa da ruwan roba ya ajiye masa sannan ya fita da sauri ya tarda abokanan aikinsa dan bata taimakon gaggawa


Cikin ikon Allah a lokaci kankanin aka samu aka daidaita bugawar zuciyarta sannan aka tsayar da zubar da jinin da ta fara , sai dai kukan da take yi sun gaza hannata shi, sun yi iya yinsu dan gannin ta daina kukan ama ta kiya, uwa uba tunda suka daidaita harkar bugawar zuciyarta ya zamto ko me aka zo za'a saka mata sai ta karanta a zaune cir a saman gadon take hakan ya sa ta ki a saka mata alurar barci, abinka da wace take da damar dakatar da su din ne, domin da wani ne gaskiya Bama zai tarki haka ba


Docter Muktar ya dubi Nurse Halima da kula ya ce" Ina ga ki tabo docter, dan kar ya mana fadan cewa a kan me zamu saurari ra'ayinta kin san baya son wasa da irin haka"


Nurse Halima ta fitar da numfashi tana cire safar hannunta ta ce" Ok docter"


Fitowa ta yi da dan gaggawa dan karasawa office din docter Ahmad din dan ta isar da sakonsa, sai dai tana fitowar ta samu wajen dakatawar ya cika sosai, dan kuwa matan Elhaji mai kwanonin sun karaso su dukansu, haka kuma mahaifiyar Yumnar da yayarta wace ta zo gannin jikin mahaifinsu da ya yi yar jinya su dinma sun karaso din, sai dai yannayin mahaifiyar Yumnar sam ba alamun sassauci a fuskarta kamar yadda yannayinta yake


Tunkarar Nurse Halima ta yi , fuskarta a hade hakama yannayinta ta ce" Nurse yaya jikin yarinyata? Ina fatan tana iya mikewa mu je gida?"


Yayar Yumnah dake tsaye kusa da Hajia ta yi gagawar kallon mahaifiyar Tata, 'ya ALLAH' shine abinda ta ayana a cen kasan zuciyarta, shin yaya zata yi da wannan fitina ne? Ama a gaskiya wannan mata da ta kirayi mamansu ta ziga rikicin nan bata yi masu adalci ba, yanzu gashi tunda mahaifiyarsu ta zo ko gaisar da iyayen TAUFEEK din bata yi ba sai fizge fizge take yi har ta saka Hajia gaishe da ita cike da mamakinta, sai kuma ga wata Maganar?


Nurse Halima da kula sosai ta ce" Sorry Hajia, matar Sir ce a ciki, jikinta da sauki sosai sai dai ba maganar tafiya da ita yanzu, ki dan yi hakuri zan je wajen sir din ne"


Da sauri mahaifiyar Yumnah ta dan tareta ta ce" ki dan dakata, ina son shiga ganninta, du wani wanda zai ce wani abu a kanta bayana yake dan nice mahaifiyarta, ina bukatar a bani y'ata na cenza mata wata asibitin!"


Da sauri yayar Yumnah ta matso ta ce" Mama, dan Allah ki yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login