Showing 78001 words to 81000 words out of 186303 words
da ALLAH ya bata, sai dai ga dukkan alamu kamar ta dan shafa mayafin ne dan ko alamar fita daga hannunsa bai yi ba
A tsorace ta dan ja baya sakamakon kallon da yake mata wanda ya kayar mata da gaba
Da sauri ta waiwaya wajen wani vigil da ya karaso jin hayaniya sama sama dan gannin ko waye
Da sauri Vigil din ya yi gagawar yin baya bayan ya fadi" Sorry sir" ya koma bakin aikinsa
A birkice ta juyo tana sake kallonsa......., Sorry sir???????, Kennan yana ganninsa shima? Yana, yana?????, "Wayo allahna......" Khausar ta fada tana kokarin dora hannunta saman kanta
Sai kuma ta fasa a hankali, ta matukar rage karfin muryarta, hannunta na rawa rawa ta miko da nufin taba fuskarsa
Gannin bai hannata ba ya sakata kai hannun nata a hankali for the first time da ta taba fuskarsa haka a hankali ta dan shafa gefen fuskarsa mai dauke da saje madaidaici har zuwa wajen jajayen lebensa sannan ta sake zuba idannuwanta cikin nasa a hankali ta sauke dagen da ta yi dan shafa fuskar tasa ta nemi janye hannayenta zuciyarta na yayankewa tana neman sake fitar da ita daga hayacinta a raunane ta so janyewar dan ta yi tafiyarta, sai dai ya ki bata wannan damar ya saka lalausan hannunsa da sauri ya rike nata hannun ta wajen tsintsiyar hannunta a hankali ya maida hannun wajen da ta dauke, daf da lebensa yana kallonta ido cikin ido a sanyaye ainun ya ce" Please besty am, clm dwn, Khausar nine fa, TAUFEEK dinki ne......."
Kai ta langwabe, hawaye suka shiga tsere a saman kuncinta, zuciyarta na dokawa da karfi , lebenta na rawa rawa tana kallon fuskarsa da ta dauki ja da idannuwansa da su dinma suka dauki jan, lebenta na barbarbar ta ce""'''
Oh ya rab, du yadda na so sama maku da yawa ya gagara sorry plzπ sai na gyara wayana wollahππππππππππππππ
Yanzu fa za'a shiga wani babin
Babin rikicewar zuciya da kwakwaluwa
Babin bugawar zuciya da tashin hankali
A dole tauheeki jikan hajia ya yi hawaye
A dole besty ta yi baram baran da kowama dan ita ba shashasha baceππ
A dole muma mu rikice domin ba zamu taba yarda da rikicin nan ba
Abinda na sani shine ko me lukutar Aba zata yi a kan gaskiyarta take!
Mu kafta auren Mujaheed da khausara yar baiwaπ₯Ή
Nnnn. πΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈ Na tafi
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
*DA CIWO A ZUCIYATA*
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 2οΈβ£8οΈβ£
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicΓ©
Lait de nuit
Parfums dΓ©sodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*WaΙannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwaraiππ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuΙi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mataπππππ
Lebenta na barbarbar ta ce" TAUFEEK? , Dan Allah ka sanar min kai mutun ne ko aljani?"
Magana take yi ranta na kuma dugunzuma yana Ιaci, hankalinta na neman tashi, hakan ya sa take fitar da numfashinta da dan gaggawa da kuma dan karfi, wanda ya hadasa a dole numfashintan nan shine yake shaka
A hankali yana rike da hannun nata yake so sai ya saka ta daina hakin nan ta hanyar tsatsareta da dubansa mai wuyar fasara
Muryarsa a sanyaye ya ce" Kin gaji, ga yinwa kina ji baki ci komai ba, mu tafi gida ki ci abinci sai mu zauna mu yi magana, yaya zaki min duban aljani? Ni mutun ne kamarki, kuma wannan fuskar da kika gani itace Ni, plz ki kwontar da hankalinki mu tafi"
Eh lalle ta yarda, ta fado duniyar wulakanci da rainin wayo
Sai dai bata tunanin haka daga gareshi ba
Da karfi ta janye hannunta zuciyarta na kunna tana kallonsa ta ce" Kana nufin, duka kaf zaman da na yi da kai shekaru uku da doriya ba kai din bane wani version na rayuwarka ta karya ne?
............"
Ta karashe fada tana juyawa tana bin makeken asibitin da kallo ta juyo ta ce" Kana nufin wannan daula taka ce malakinka a matsayin shugaban wajen kuma baban likitan zuciya professeur sai kuma me???......"
Ta yi wata yar dariya mai ciwo da daci ta kafe shi da ido ta ce" Kana nufin zaune da nake da kai, nake kwana ina tashi da tunanin a duniya ko yan gidanku ba kowa zai iya fadin waye kai ba kamar Ni ashe shirme nake yi, Ni din nan nice ban sanka ba.....?..., TAUFEEK ama me na maka da zafi a gidan duniya da ka shigo ka zabi shiga jikina ka yi abota da Ni ka shiga rayuwana .....me na yi ne da girman laifi haka????"
"KHausar" ya fada a hankali yana dafe gaban goshinsa, ya sani ne akoy rikici a duniyarta idan ta rikice kuma shi dai kam ba'a raga masa, ama bai taba tunanin ranar da zata san waye shi zasu iya rikicewa har haka ba, abinda ya sani daya ne kwal zata sauko ta hakura kamar yadda ta saba su shirya, kai ama docter ya masa rashin mutunci, daga cewa a turata clinik sai ya turota nan? Ko bai gane yana nufin clinik dinsa ba wai Lafiya clinik ba? Gashi rana tsaka zai hadasa masa rigima da yarinyar nan!
A hankali ya saki gaban goshin nasa ya fuskanceta , a tausashe ainun ya ce" Du fa ba inda kika nufa bane, Ni inspector ne a fannin bincike na abinda ya shafi lafiya, kamar yadda kika sani akoy office dake kula da hakan, na je makarantarku ne dan na bincika a kakama wa'inda ke aikata mana aiki irin na a zo rana tsaka ba'a yi shekara ta farko a dira ta biyu na, ko a tsalake ta biyun a je ta ukun, ko a ki yi sai a karshe a samu takarda, takardar karya ko ta gasken da hanyoyin da suke bi sunna samu, duka dai da sauransu....., Ai kin gane me nake nufi, ba wai karya na maki ba, kuma kin ga dole zan boye waye Ni Ko?"
Da ya san abinda zai karra balowa da kyaletama ya yi ta tafin ya bita gida suka sasanta, domin a yanzun sai take gannin bakinsa, rai bace ta dakatar da shi tana fadin" Kana nufin, a zuwanka dan yin aikinka ka zo ne dan ka samu munafukan makarantarmu, sai ka taka ta kaina ka shiga jikina Ni balagazar makarantar wace take gaisawa da kowa ta san kowa take zumunci da kowa ta kuma san halin kowa dan ka cima burinka?, Wato Ni wawuyar nan wace ke iya fada maka komai Bama sai ka tambaya ba cikin saukin nan?, Ni wace bata san inda ta nufa ba da nake iya fayyace maka aikinka cikin saukin nan? Shine ka shiga jikina ka saka na sakankance harta iyayena suka sanka suke mutumtaka, ka saka na je gidanku na saki karina harda kwana Ni mai aboki dan uwa a gareni? Kana nufin a cikin aikin naka ne nake budar bakina in sanar maka matsalata a bayane ba a boye ba?, Sirrin da Umana bata sani ba a kaina ka sani, idan ina kuka burina na jika na sanar maka , ashe du rayuwar ture kake da Ni ban sani ba....? TAUFEEK ka ci amanar zumunci, kuma ba zan yafe maka ba!, Na godema Allah da na gani a yanzu ina mai tabbatar maka in sha Allah daga yanzun an gama, ko menene ya wuce, Taufeek zan ci gaba da zuwa in na samu an daukeni zan yi aikina cikin JAJIRCEWA, domin idan baka manta ba na sha fada maka ina karatu cikin JAJIRCEWA ne dan na san iyayena zasu gajiya wata rana, kanaina nice mamansu....., Zan yi aikina kamar kowace ma'aikaciya, ko ba komai a zamana da kai na karu ka taimakeni sosai cikin nuna min ba kai ka yi ba, Allah ya baka ladan haka, ama ka sani *CIWON DAKE ZUCIYATA* ya goge alakata da kai, ba zan yi zumunci da kai ba again, dan ban san yanzun a kan wani mataki za'a yishi da Ni ba, kar aje Ni din ta kaina ake bi ana cimma mutanena...."
Daga haka ta sake mika hannu ta ja mayafinta, wannan karro tun kafin ta ja mayafin ya sauka daga hannunsa , ta janye a hankali ta dora shi a gefen kafadarta sannan ta juya wajen motar nan ta dauki jakarta ta rataya ta kama hanyar tafiya tana share idannuwanta har gabanta na mata ruwa ruwa kamar wace ta sha wani abu
A tsaye yake, yana binta da kallo har ta bacewa ganninsa gaba daya
A hankali ya dan ja numfashi a kirjinsa ya sake rintse idannuwansa ya bude ya kuma bin hanyar da ta bi da kallo
A cen kasan zuciyarsa kokarinsa ya ba kansa tabacin cewa ranta ne ya baci iya bacewa shi yasa har ta yanke wannan hukuncin, ya san yadda zai bi ya bata hakuri ta sauko
Dan murmushi ya yi a hankali yana juyawa dan ba sauka ya yi ba su doctors ya takawa sai ya ganta tsaye , a sanyaye ainun ya dan sake sakin murmushi, yana so lalle sai ya kori wani gefe na zuciyarsa dake fada masa kamar ba wasa take yi ta hanyar tabbatarwa ransa cewa to ai kadan daga aikinta, in dai Khausar ce idan ranta ya baci tsaf take wanke shi abinta, bata ko duban girmansa abinta, uhum abin haushi wai mayafin da ya mata magana kansa karshema a kafada ta yafa Bama rufashi ta yi ba, ai zai ga in zata iya tafiya har gida da shi a gefen kafada
Yana shiga office dinsa ya ciro wayarsa ya zauna a hankali ya shiga kiran numbarta
Kira na farko ya shiga, ama na biyu sai kiran ke dawo masa
Ido ya dan zarro dan hakan na nufin ta saka shi a Black list kennan
A hankali ya ajiye wayar yana furta " Uhum Allah shi kyauta ya shirye ki"
Daga haka ya ci gaba da yan aikace aikacensa, duda hankalin nasa a rabe yanzu, ama haka ya ringa aikin dan dole ne ya gama abinda ke gabansa a yau
Khausar bata isa gida ba sai kusan magariba
Koda ta je ta tarda Mama bata nan ama ta Bara mata ky a makota, dan haka ta amso ta zo gida ta cenza kayanta sannan ta shiga kimtsa gidan ranta a matukar bace
Tana gamawa ta dora masu yar makaroni ta koma ta zauna ita kadai tana cije lebe da kuma tarin jin haushin da ya daskare mata a cen kasan zuciyarta
Yanzu ita? Kennan waye ya dauketa da mahinmanci ne a duniya bayan iyayenta? Bata taba tunanin zata iya riskar wannan gagarumar surprise daga mutun mafi kusanci da duniyarta ba irin TAUFEEK
Ita fa babu wani uzuri da zai gabatar mata ko za'a fada mata ta saurara ko ta gane
A zamantakewarsu ya dace ace ya fi kowa Sannin wacece ita, idan tace wacece ita tana nufin koda aikin sirri yake yi a yadda ya gama karantarta in ba dan yana anfani da ita dan cinma aikin nasa bane da ya sanar mata sirrin dake boye a tsakaninsu
Ita me ta boye masa ne?
Irin yadda take yiwa umarninsa biyayya kuwa tana tunanin su Aba kadai suke gaban furucinsa
Wata kwafa ta yi tana amsa salamar su Salma yarinyar dake bayan layinsu ta mike daga zaunen da take a zuciyarta tana ayana' hijab ko?, Zan saka ama na rantse maka ba dai irin wancen ba, kai ba zan kuma maka biyayya ba, ba Ni ba kai! Zan kiyaye adinina ama bi izinillah nima zan dauki wasu shawarwari da ake bani a matsayina na budurwa kuma musulma dan gyaran kaina ba dan batawa ba na kasance kamar kowa!, Wani sa'in harma da gudun kar kace yace nake bulumtun nan! A yanzu ka jima baka ce ba, koda yake Bama sai na kuma haduwa da kai ba bale har ka iya bani opinion dinka a kan abinda yake nawa! Domin daga yau Ni nice Ni daya ce kuma, du wani bestyma ai cuta ce, kwarai Hajia ta yi gaskiya ashe amincinmu akoy wata a kasa? Watar kuwa ba komai bace face cuta tsagwaronta!, Wasu mutanen dai sun ji kunya'
Tabarma ta shinfida masu, sunna neman zaunawa sai ga Maman ta dawo a gajiya tilis, dama daga gidan rasuwa take kuma na kusa ne sosai tarema suke da Aba,
Jin rasuwar da aka yi ya sakata kin fada masu abinda ta Ζunso take jira ta sanar masu, saima ta shiga hidimarsu ba tare da ta gane cewar salmar nan wajenta ta zo ba har sai da Maman ta kireta daka ta ce" Khausar, yaya zaki bar bakuwarki zaune ita daya ne haka?"
Khausar da mamaki ta ce" Mama bakuwata kuma? Na zata ko aikota aka yi wajenki?"
Maman ma da mamaki ta ce" Wajena kuma? To wa zai aikota Wajena?, Da aikotan ne aka yi ai da ta sanar min ko?, Na ga tare na tardo ku kuma Ni bata nuna Wajena ta zo ba ki je ki dan saurareta mana ?"
Khausar ta fito zuciyarta cike da mamaki, abinda ya sa mamakin ke damunta Salmar nan dai na farko ba sa'arta bace, dan a kadan tana iya bata shekara shida ko fiye, sannan irin rikakun yan ji da kan nan ne na anguwa wa'inda ko gaisuwarka basu cika amsawa ba don mahaifinsu na mai kudin anguwa, a gaskiya a gidansu ana fadin sun cika girman kai, kuma daga mahaifiyarsu suka dauko domin kaf layin nan da bayanshi babu wanda mahaifiyarsu ke hulΙar arziki da shi, ita ta fi karfin ajinsu, mahaifinsu dai da sauki dan shi ko me ake yi a anguwa in dai ya ji ana yi da shi yana zuwa fatiha na sunna ta aure ko zana'iza
Zama ta yi yanzun du a takure ba kamar dazu da take sake ba, dan dazu a tunaninta wajen mahaifiyarta Salma ta zo
Salma kam ko a yanzu da Khausar ta dawo ta zauna tsaf ta kare mata kallo,.kallo irin na son Sannin shin da gaske Ζ΄aΖ΄anta matar nan ta masa ne har da ya nace haka da son samun kusanci irin na zuciya da zuciya da ita ko da akace likita ce ita din yake so ta zamto a cikin ahalinsu?
Dan murmushi ta yi tana mikewa ta saba jakarta a kafadarta ta yan gayu tana kallon KHausar ta ce" Sister, zan juya, ki dan ban numbarki dama fira na kawo maki"
Sosai Khausar ta so cewa Fira kuma? Ta me fa? Sai dai ta kasa fada saima hijab da ta saka a shigarta dakin dan bata cika son kallo irin wannan ba a rayuwa yana damunta ainun
Wayarta ta dauko ba wata damuwa ta ba Salma numbar tata harma ta dan taka mata bakin kofar gida sannan ta dawo da sauri tana ta hade rai dan a dan fitar nan ta san ta sake cirarwa kanta magana, ana iya cewa bata mu'amala da mutane talaka sai masu kudi, shi yasa batama tsaya har Salma ta shiga motarta ba ta dawo da sauri
A wannan daren abincin kirki kasa ci ta yi, danma juwa ta fara nusar da ita menene yinwa, da tana iya kasa cin abincin kwata kwara dan cin amanar da akai mata, wani sashe na zuciyarta kuwa kuka yake yi sosai na decision dinta, sai dai ta ja ta tsaya zata ga waye keda iko cikin ita fa shi!
____________________________________
Karfe bakwai na safe
*TAUFEEK*
Zaune yake saman table yana karyawa kira shigo wayarsa, kira ne mai mahimmanci dan haka ya dan mike ya shiga amsawa, Yumnah kuwa ta bishi da wani irin sansanyan kallo tana jin wani irin nutsatsen kusancin zuci da idannuwa idan tana ta kallonsa
Idannuwanta ta lumshe, tana matukar jin tarin kauna da girman mijinta a zuciyarta
Dawowarsa ya sakata sake zuba masa wani shayin sannan ta koma ta zauna tana kallon yadda yake dan sha yana duban screen din wayarsa dake ajiye a saman table din
Dubanta ta kai itama, sai ta ga kamar call ne yake aikawa
Har zata cire kanta sai ta sake dubawa dan haka kawai ta ji idannuwanta sun sake likuwa a saman screen din wayar
Da sauri ta dauke idannuwanta ta zuba a saman fuskarsa
Yannayin fuskarsa sam ba walwala a tare da ita, tana fadin tun jiya kamar hankalinsa a dan rabe , kuma yanzu sai ta ga yana kiran matar da ta yi tunanin ko ta tabata ne? Watau an yi baram baram ne? Dan kuwa an jima bata ga kiranta a wayar mijinta ba
Ajiyar zuciya ta sauke mai zafi a lokacin da ya gama sha ya nuna ba zai iya karyawa da wuri ba zai dan fita, sannan ya mike yana daukan rigar dake ajiye mai ruwan ashe color ta vst ya