Showing 165001 words to 168000 words out of 186303 words

Chapter 56 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18748

fidda uwa ake
*Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu ,
KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida
07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah
Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528
Maman zarah mabera SOKOTO






Washe gari karfe bakwai da rabi ya sauko, a lokacin tuni Khausar ta gama girkin abin kari ta yi shiri irin na wace zata fita da sassafe


A wajen dinern take tsaye tana sake gyara wajen a nutse ta juyo tana sauke dubanta saman fuskarsa


A hankali ta sake ambaton sunnan Allah a cen kasan zuciyarta , domin tunda ta sauko aikin nan karfe biyar take sake saken ko yana ina? Bata ji fitarsa masalaci ba, ama ta ji dawowarsa, haka kuma bata san wani dakin ya je ba nasa ko na matarsa , abinka da shedan sai ta ringa yan dake sake masu zafi a zuciyarta, sai dai cikin ikon Allah bata bari abin ya mata ila ba ta ringa ambaton Allah da kuma sakawa ranta cewar Yumnah iyalinsa ce bata da ikon saka wani abu a rai dan ta yi tunaninsa da ita , hakan wata hanya ce ta sakawa rai damuwa, gwara zikiri da wannan tunani, dan haka sai ta bige da zikirin


Murmushi ta sakar masa kamar yadda ya sakar mata sannan ya bude mata hannayensa


A nutse ta karasa ta shige jikinsa a hankali ta lumshe idannuwanta tana shaฦ™ar kanshin turaran da yake yi kasa kasa ta ce" Barka da safiya Magidanci"


Murmushi ya yi a hankali ya ja hancinta sannan ya dan juya wajen dinern kasa kasan shima ya ce" Iyalina....., Fatan kin tashi cikin koshin lafiya?"


Murmushi ta yi a hankali ta amsa shi sannan ta nuna masa abin karin tana fadin" Ga abincin , na kirawo Yumnah ne mu karya?"


Sakinta ya yi ya karasa bakin kujera ya ja ya zauna yana kallonta ya ce" Dan bani abu a frij mana?"


Juyawa ta yi ta karasa wajen frij din ta bude ta dan duka sannan ta juyo tana kallonsa ta ga ya mata wani kuriii ta ce" Me zan dauko?"


Idannuwansa ya dauke a hankali ya girgiza kai da hannunsa ya yafitota


Dan jim ta yi kafin ta rufe ta dawo inda yake tana sauraronsa


Hannayenta biyu ya riko yana kallonta a tausashe ya ce" Anya kuwa zan iya?"


Khausar ta zuba masa ido, a hankali ta ce" Mene ba zaka iya ba?"


TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya a nutse ya dago yana kallon fuskarta daga irin riko hannayen nata da ya yi ya ce" Da ace ba zan tauye hakinki ba, da mun je na saka hannu a gaban mai kwanoni cewar du karshen wata zaki dauki albashinki ki zauna a gida, a gidanma a bangarena....., Khausar kin yi shiga kamilaliya ama kuma idan kika juya kina min wasa da ajiya, dole sai sun motsa ne?"


Ido ta rintse cikin jin matsananciyar kunya


A hankali take son kwacewa dan ta boye fuskarta ama ya ki bata dama
A tausashe ya dora da fadin" yaya zamu yi? Ko mu yi hakan?"


Da sauri ta bude idannuwanta ta zuba masa su, eh ta sani albashinta ba komai bane a wajensa idanma du sati sati zai mata ba zai taba gajiyawa ba, sai dai yau da gobe akace, tunda ta riga ta zama iyalinsa zama ne za'a yi na sabo, komai kyanta komai son da yake ji nata a zuciyarsa yau da gobe na iya goge komai a ransa sai kauna da girmamawa idan ta yiwa kanta da kyau ta zauna lafiya da shi , ba ita daya yake da ita ba, kuma bata da tabacin daga ita zai rufe ne ko kuwa zai samu wace ta fita ne? Ko ba komai namiji ne shi wanda Allah ya halitta da bukatar hakan da kuma yan leke leke irin na ido da zuciya idan yau ta dauki wannan dama ta rike me gaba zata haifar? Gwara ya zamto an yi abin a bisa tsarin da ya dace , to fa za'a iya tsofewa ana yi...., ko ba wannan ba ai bata yi karatun likita ba dan ta zauna a gida ba tare da tana yin aikin ba, tana so, tana kwadayin ladan nan sosai


A tausashe ta dan yi kasa da dubanta ta ce" Ka yi hakuri, in sha Allah dukkan abinda na ga zai daga maka hankali zan kiyaye, ama Please ka daina maganar nan mana *ABINMU?* "


Ajiyar zuciya ya sauke kawai ya shiga cin abincin da ta zuba masa bayan ya tabatar mata Yumnah ษ“aci take yi, dan bata cika kari da safe ba gaskiya shima har ta kusan koya masa haka Hajia ce ta ki hakan dan in bata bashi karin ba ita ke bashi tana fadace fadace


Sai da suka gama ta haye saman ta sako hijab dinta ta dauko jakarta ta hannu baka sannan ta shafa dan sasaukan turare sai agogon dake hannunta da zobunna biyu na azurfa , takalmin kafarta kuwa plate ne baki irin jakar mai kyan gaske sai wayar da ta fara zame mata jiki saboda irin yadda yan uwanta ke saka mata riketa a rai ta hanyar tabota ta whatup da sakata a grups na karuwa na matan da suka san kansu


A lokacin da ya nufi bangaren su Mama ita kuma ta yi na Hajia, a gagauce ta amshi abinda Hajiar ta jika wai ko maganin baki ko me ta sha ita dai sannan ta yiwu Hajiar salama ita kuma ta rakota har bangaren su Maman tana faman mata addu'a


A nan suka hade da shi , a lokacin da ya gane ta zo yiwa mama salama ne zata je wajen aiki sai ya ji wani dadi a ransa, Bama da ya ga Maman ta riko hannunta ba wani kawar da kai irin na sirikan nan ta yi mata addu'a harda su gyara mata hijab dinta sai ya ji wani irin farin ciki ya idasa lulube shi


Har sun shiga Mota Hajia ta bata nasa maganin bakin ta ce" Bashi ya sha, Ni ya rainan wayo ba zai sha ba"


Khausar ta yi murmushi ta amsa ta juyo gefensa a lokacin da ya sakarwa Hajia Harara ya ce" Kauce Ni in ja motata!"


Hajia ta tabe baki ta ja baya tana sakarwa motar naushi kuma ta yarfe hannun ta ce" Aikin banza motar banza da wofi gareka wata mota irin ta munafukai na waje baya gannin na ciki sai dai na ciki ya ga na waje, da ire irinsu ake satar ya'yan mutane, a ciki kuma ake yiwa ya'yan mutane ciki!"


Ido ya zarro ya juyo ya kalli Khausar
Ita kuma bata shirya ba ta fashe da dariya har tana rike ciki ta dora hannayenta biyu saman kanta ta ce" Na shiga ukuna me yasa kake son saka Hajia fada ne a rayuwa?"


Shima dariyar ya yi yana ficewa da motar a gidan sannan ya harbata bakin titi ya ce" Hajia bata jin magana "


Ita kam rabonta da daria irin haka har ta manta, a haka suka karasa wajen aikin


A lokacin da suka fito daga motar ya zamto ne lokacin isowar manyan, kuma idan an iso din sukan dan tsaya su gaisa ne kafin kowane ya nufi bangaren da yake aikin wato manyan doctocin asibitin


Lokaci daya yannayinsa , wanda ta ganshi a lokacin da ta zo asibitin ya wanzu a tare da shi da fuskarsa baki daya


Bayan ta fito a motar sai ta samu kanta da satar kallonsa, dan kuwa gaba dayansa sai ya sake kawatuwa a idannuwanta


A nutse ta zagayo da nufin tafiya ta shige bayan ta gaisar da likitocin domin a irin lokacin du sun ga shi din ne a motar dan haka sunna haramar fara gaisar da shi a matsayinsa na baban su kuma abokin aikin su


A hankali ya kamo hannunta, sannan ya janye jakar hannun nata ya rike a tausashe ya ce" rigarki a office dina fa, mu je ki saka"


Jakar ta bi da kallo sannan ta kalli abokan aikinsa wa'inda suke manyan ta ita kuma,
Da sauri ta sada kanta ta koma gefe kadan da girmamawa ta shiga gaishe su, a cikinsu daya ne kawai ya san mata take a wajensa, shine wanda ya kula da Hajia ranar da aka kawota dan haka da kula sosai ya amsa gaisuwar yana fadin" Barka da isowa madame"


Sauran kuwa du sai abin ya sake basu mamaki, bale matan cikinsu


Docter Umaima ta ce" Docter kawo jakar na rike"


TAUFEEK dake gaisawa da mazan a nutse ya dan girgiza kai ya ce" Ta madame ce Zan rike docter, thank you"


Daga nan ya karasa da ido ya mata alamun ta yi gaba dan haka ta juya ga yi gaban tana lumshe idannuwanta dan hanna kirjinta dokawar nan ta fara shigewa lft din shima ya shiga ya danna ya rufe su sannan ya yi sama da su


"Professeur aure ya karra ne?" Docter ta tambaya cike da mamaki


Docter ya ce" Eh matarsa ce, haka dai ya fada min ranar da aka kawo Hajia"


"Wauh ashe mugun dan soyaya ne? , Ka ga a irin yadda baya sakarwa matan wajen nan fuska ban yi zaton zai iya zuba soyaya harda rikewa mace jaka ba" docter Aliyu ya fada yana murmushi, har ga Allah ya manta cewa Docter Mufeeda na fama da kai kawo irin na soyaya a zuciyarta na ogan nasu, sai da ya ji ta ja tsaki ta yi gaba da jakarta ta nufi bangaren da take aiki wato itace shugabar su KHausar din ta barsu a nan ne ya zarro ido a ransa ya ce" Toh fa"


Sai da ya Bala mata boturan rigar kaf sannan ya barta ta tafi wajen aikinta bayan ya yi mata kashedin karfe goma sha biyu maza ta hayo ta ci abinci ko me take yi zai tanadar mata abincinta ya bata ky din office din koda baya nan ta bude ta ci ta koma


A lokacin da ta sauko ta je stf dinsu tuni an shiga aiki, sai dai tana zuwa yau din ta hadu da aiyuka harda na mamaki, domin tarin yan pansamar da aka yiwa aiki ne ke jiranta ba sakin fuska ba komai docter Mufeeda ta umarceta kan ta hau aiki bayan ta mata fadan dora lokacin da ta yi gaban kowa ta dizgata da fadin ba fa zata dauki irin wannan abin ba, ta kula aiki ya kawota ba biye biye ba


Sosai Khausar ta tsorata da yannayin docter, dan bata taษ“a ganninta tana masifa haka ba, hasalima bata san menene laifinta ba ama gudun karawa kanta wani laifin sai ta shige dan dakin ta shiga aikin ba ji ba gani a tsaye ne ba a zaune ba


A kala ta kai awa uku tana aikin nan dan asibitin ba karamar asibiti bace, yan fashin kuwa ba iya na haihuwa bane


Tana gamawa ko ruwa bata bari ta sha ba ga abokan aikinta ga komai sunna zaune sunna dan hutawa da yar fira docter tace" ki je dakunna ki duba duk wanda karin ruwansa ya kare ki cire in an karra masa wani ki kara in ba za'a kara ba ki masa bayani"


Da dan mamaki Khausar ta ce" Docter duka dakunnan ?"


Docter Mufeeda ta ce" Eh, akoy damuwa ne?"


A hankali ta girgiza kanta ta je tana harhada kayan aikin tana jin juwa na dibanta sosai, sai dai ita ta san ba wai dan ta yi wannan dan aikin bane domin wanda ya samu horon hospital urgence karya ne aikin tsaye ya saka shi juwa


Tana gama hadawar sister Humaira ta mike tana turo abin turawan nan ta ce" Dora mu je sister"


"Ita kadai zata yi!" Docter Mufeeda ta fada tana gimtse fuska ta ci gaba da aikinta


Gaba dayansu hakan ya matukar basu mamaki, kowa sai ya saka a ransa ko laifi Khausar din ta yi? Ciki harda mazan domin daya sai da yace" Docter ko sister Khausar ta yi laifi ne? A gafarceta abu da bako?"


Ama sai docter ta masa banza ita kuwa Khausar a haka ta fice ta shiga aikin nan cike da kula da mutunta marar lafiya


Wannan zagaye sosai ya saka ta gaji, ko dan ta kwana biyu bata yi bane? Ko menene? Koma dai menene gaskiya ji take yi kamar ta kifa ga wata juwa dake janta sosai, a haka ta karasa office din nasu ta ajiye chariot din sannan ta daura alwallah ta shiga sallah dan a lokacin tuni an yi azahar


Tana gamawa ta fito da nufin zuwa ta ba docter hakuri ko wani laifi ta yi? Ba dan ta ringa sakata aiki ita kadai bane, ko daya, yannayin fuskar na docter ne ya sakata a damuwa, dan bata saba ganninta tana masu haka ba sam, eh lalle mace ce mai kamewa ama ba har haka ba, karrara fuskarta na nuna kamar tana jin haushinta ne


Tana fitowa wani ikon Allah ko damar ta je cin abincin ita yau Docter ba zata bata ba da wani daure fuskar ta ce" Ki je daki mai numbar ashirin da daya ki goge amai patient din ya yi"


Da dan mamaki ta zuba mata ido, gugar amai kuma? Gugar amai fa?, Yaushe asibitin ta fara hade hade ne kuma bayan akoy wa'inda wannan din ne aikinsu ita likita me ya hadata da zuwa gugar amai,
Da kula sosai da kuma girmamawa Khausar ta ce" Docter gugar amai? Babu masu yi ne?"


Docter ta dago da mamaki tana dubanta ta ce" Sai babu masu yi zaki yi? Ko ban isa sakaki ki yin bane?"


Da sauri Khausar ta dan girgiza kai tana sada kanta ta ce" Ki yi hakuri ba haka nake nufi ba, bari in je in yi, dan Allah idan na yi wani laifin ne ki gafarceni docter"


Docter zata yi magana aka sake dan kwankwasawa dan haka ta dago a dan fusace ta ce" Com in, wai wanene dan Allah!"


A nutse ya murza kofar ya shigo yana sauke dubansa a kan docter Mufeeda wace ta zuba masa idon itama zuciyarta na dokawa da abubuwa masu yawa a cikinta


Da kula ya ce" Barka da warhaka docter"


Da kyar ta iya yakar bakinta har ta iya fitar da furucin bakin nata sada dubanta a tausashe tana kokarin boye damuwarta da kuma girmamawa a gare shi ta mike tana fadin" Professeur Barka da rana, ka yi hakuri dan Allah ina cikin aiki ne sosai shi yasa na amsa a haka"


Bai ce mata komai ba sai Khausar da ya kalla, a nutse ya sake kallon Docter Mufeeda sannan ya kuma kallon KHausar


Ledar dake hannunsa ta take a way ya mikawa Khausar din a tausashe ya ce"Ba nace karfe 12 ta maki a office dina ba Wifey????"


Da sauri Docter Mufeeda ta dago ta zuba masa ido, Khausar kuwa da ta amshi abincin ta rike a hannunta ta kasa koda kallonsa ne dan idannuwanta sun ciko da kwallah ta dan sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" Aiki ne nake yi TAUFEEK, yanzu zan zo"


Wani sake zarro idon Docter Mufeeda ta yi jin gatsau wannan ta kirayi Professeur da sunnansa?


A nutse ta kai ledar ciki ta fito ta karasa wajen abin sharar nan ta dauki bokici guda da kayan aiki ta juya da nufin tafiyarta


A dan daburce Docter Mufeeda ta ce" AM, sister Khausar dawo ki ci abincin mana"


Khausar ta ja ta tsaya , ta juyo tana kallonta sai kuma ta kai kayan ta ajiye ta koma ta dauko ledar ta fito


Da kyar ya iya budar bakinsa da ya wani irin dafkewa da bacin rai ya ce" Ki je office dina"


Khausar ta gyada kai ta wuce, ita ba abinda ya fi damunta irin juwar nan ta nufi sama


Da mamaki ya zubawa docter Mufeeda ido yana kallonta ya ce "
๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”




*DA CIWO A ZUCIYATA*




๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 6๏ธโƒฃ2๏ธโƒฃ


*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*


1: Duk karyar kada


2: Yar mahaukaciya


3: Neman na kaina


4: Bani da zabi


5: Bak'a ce


6: Kutkale


7: Makauniya ce


8: Mage


9: Duk nisan jifa


10: Idan ka raina inda kake


11: Dutse


12: Alkalamin kadarata


13: Bani da zabi


14: Dakika Biyar


15:Wata kokowar


16: Aure yakin mata


17: Ni zan ladabi


18: Daga tafia daukar soja


*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ


Tallah 3
Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login