Showing 18001 words to 21000 words out of 186303 words

Chapter 7 - DA CIWO A ZUCIYATA COMPLT BY SAJIDA.txt

09 Nov 2024

18801

fada maka jiya cewa yau zamu je kasuwar? Biyu na raba na hannun nan na wajen Hajiya naka ne ka gwadawa abokananka ni kuwa jibi in sha Allah zan fara gwadawa sauran freinds"


Ankon ya dan kalla sai kuma ya yi diffg bai ce masu komai ba, Hajia kuwa har yi take kamar zata bude masu baki ta kalli wannan ta kalli wancen, cen dai ajinta ya tsimkota ta ce" Ni ko a kauye, zamanin da nake ta balarabe, kafin kawata ta kwacen shi karya ne ace a kawancenmu ni in ringa yiwa kawa surutu ta kyale ni, wannan ƙawance naku lalle akoy alamar tambaya, ace kina surutu ya wani kyale ki? In nice in na kumaa kulaka in zama tsintsiyar sharar kurma!"


Aisha ta mike tsagal tana tatara komatsansu tana fan murmushi ta ce" To bara na tare mana taxi Aunty ""


KAUSAR kam dariyarta take ci, ita fa walahi lamarin hajia baya wani damunta, baya taba bata mata rai, kuma tsufan HAJIA tsufa ne mai kyau, domin koda yaushe tana rike da carbinta tana ja, wannan zamanin da ya zama abin tashin hankali wani tsufan dake zuwa a gigice? Rikicinta kuwa tafe yake da rashin munafurci da bata iya ba, wasu bama tsofin bane a gaban idannuwanka zasu nuna maka so a bayan idannuwanka kuwa tamkar su soka maka wuka su daina ganninka a cikin duniyar kwata kwata


Fitowar da ya sake yi da ky a hannunsa ya ce" Tashi mu je" ya saka HAJIA sakin murmushi tana kallonsa ta ce" Ba dai rai na bata maka ba ko? Ai ka ga ciwon kai kake yau kuma kace tare zamu sha ruwan ko? KAUSAR tayani gani kamar ya kumbura fuska?"


KAUSAR ta girgiza kai tana murmushi ta ce" Hajia yama yarda ya maki fushi haba dai, bai yi fushi ba ko besty?"


Gannin ba dai zata tashin ba ya saka shi yin gaba , hakan ya sa ta mike da sauri, hajiarma ta mike tana fadin" Bara in dubo maki yar tsaraba Y'ar nan, yadda kika san me bana iya na ganki ban dan miko maki wani abin na tsaya tsaya ai na zai tafi ya barki ba"


KAUSAR na faman Hajia dan Allah ki barshi na gode Allah ya saka da alkhairi ama sai da ta fito da bak'ar leda tana murmushi ta ce" ke kuwa, sakon Babanki ne duda yau bai aikon da goron ba, ki ce ina gaishe su kin ji? Allah ya maki albarka"


Amsa ta yi bayan ta rage tsayinta sannan ta ringa godiyar itama ta fice ta fito tana ta waige dan gannin inda zata ganshi


Da sauri ta karasa wajen motar yar sumulmula fara dake parker ta bude gabam ta shiga ta rufo tana fadin" Ka ga fa da bari ka yi muka shiga taxi kai dake ciwon kai?, Wai ciwon kan menene haka?"


Hanci ya dan ja kadan yana tashin motar ya fara tafia da su a hankali ya ce" inaga rashin isashen barci ne, shi yasa yau ban fita ba na huta"


Kai ta gyada ta ce" Banama kana jan tafsir ne?"


Kai ya gyada kawai bai bata dogon amsa a wannan tambayar ba, sai kuma ya ce" A wani shago kika fitar da ankon nan?"


Dan murmushi ta yi ta ce" a shagon Elhaji Habu ne, ana mutumen nan bashi da kirki kawai sharin mutane ne, mu dai ya mana mutunci sosai"


Baki kawai ya tabe har suka karasa gidan bai kuma cewa komai ba sai tatausan karatun dake tashi a hankali a cikin motar


A kofar gidan suka tsaya Aisha ta ringa sauke kayansu murna fal zuciyarta tana kaiwa ciki sannan ta dawo ta dan rage tsayi tana yi masa godiya ina ya zabga mata harara ya ce" Malama mike ki bace min da gani ni"


Da daria ta mike din ta yi ciki


KAUSAR da kula ta kalle shi ta ce" Kamar ranka a bace ko ciwon kan ne?"


"Na gaji ne" ya bata amsa , sai kuma ya kalli agogo ya kalleta zai yi magana ta sake fadin" Ko na fadawa Mama ta maka kunun ayar nan? Na ga kamar kana sonshi?"


Ido ya zarro da sauri ya girgiza kansa, wanda hakan har ya so dan bata mamaki, sai kuma ya cire mata mamakin ta hanyar fadin yau ba zai fito ba zai je makaranta ne, a zuciyarsa kuwa yana ambaton ina shi ina kunnun nan? Abu dadi a baki yana sha kamar kar ya kare ashe ashe yana shirya masa tashin hankali ne? Saboda kunnun ayar nan da ya sha jiya a gida ya gaza barci har kusan biyu na dare yana fama da ciwon ciki, ga tarin gajiyar kasuwa da ta huldodinsa na gida da waje, a haka a dadafe ya kai kiran sallar fari , an yi kira kuwa ai ba barci dole ya sake fitowa ya sha madara mai dumin gaske har yana zufa, shi dai ya rainawa kunnun aya wayo kuma ya yi tirrr da shi dan bai kyauta masa ba


Gannin yau kamar yan shiru shirun sun fi komai yawa ya sakata yi masa salama ta yi shigewarta gida tana cire hijab dinta tana shafa cikinta da yake ta sabewa saboda abin azumi a jikin nata shi kadai ke raguwa sosai sanadiyar azumi ama ba wai shafewar dindindin ba, dama da azumi haka yake mata yakan ragu sosai, har bayan azuminma yana iya daukan kusan wata biyu bai koma yadda yake ba, sai fatar jikinta dake dan karra gyaruwa daga yannayin haskenta kadan ta karra yin luwaiwai, ko dan zaman gida ne da hutu ba hanyar school?, Itafa ba fa fara bace aa, fatar mahaifiyarta ce mai haske haka, irin bakin nan mai haske mai kyau, to haka yannayin fatar jikinta take


"KAUSAR, wannan kaya haka jama'a mutanen nan su basa gajiya da dawainiya ne Fisabililahi?, Shin auren yaron nan ni me zan yi na kyautatawa ga ahalin nan?"


RUKAYA dake ta farin cikin itama domin sun zagaye kayan sunna ta dadagawa ne ta ce" Mamanmu, sai dai a je tunda safe idanma da hali a kwana a cen ko kwana biyuma , in ba wannan ba ina muka ga abin basu?"


Mama ta yi murmushi ta ce" Gaskiya ne daurin aure har amsar amarya da mu za'a yi shi, ama kuma du yawan arzikin mai arziki yana jin dadi idan ya ga an masa kara an kula, in sha Allah komai kankantar bajintarmu zaki ga mahaifiyarsa da shi kansa sun ji dadinta, duba fa ki gani, idan ta tashi ware mana abu harta ni sai an ware nawa , lalle zumuncin mace da namiji akoy jin wani iri, ama idan har da kare dokokin Allah sai nace na Kausar da TAUFEEK alkhairinsa muke gani, idan an yi aure kowane ya kama gabansa kuma shikenan sai zumuncin mu iyaye in mun rike"


KAUSAR ta yi murmushi tana kaiwa zaune hadi da neman wajen kwonciya ta ce" Mama, yinwa nake ji"


Mama ta dungure mata kai ta ce" Zaki fara ko?, Ke kam ki yi kokari ki daina yiwa ciki bauta, wannan lamari naki da cikinki abin haushi, ace mace kadan ta ji yinwa ta kama raki kennan?, Azumi dai baya son haka, tashi maza yau ke zami tuka tuwon sahur kin ga na shinkafa za'a tuka kuma kin fimu iyashi"


Baki ta zumburo ta ringa kyakyafta ido tana jin gaba daya kasala da juwa sai yanzu suke lulubeta, ama a haka dole ta mike ta kama aikinta dan kuwa kowa da aikinsa basa barin Maman ta yi komai har a sha ruwa sai iya aikin Baba wanda har yau suke mamakin irin yadda Mamansu bata sakar masu aikin mahaifin nasu, lokuta da dama idan sun yi nacin hakan sai tace to ita kuma a ina zata samu ladan ? Kowa ya yi inda yake da lada kawai su barta da aikin mijinta (wannan din wata hikima ce da hanyar da zaka iya ba yayanka tarbiyyar sanni da kuma sake rike girman miji a bayyane da kuma badini, domin a rayuwa yaya babu abinda ya kai iyayensu girma da daraja, sukan dauki dukkan abinda iyayensu suka dauka da daraja suma da daraja ne, idan har uba na so ya'yansa su raina shi ko su ringa yi masa biyayar dole to ya ringa wulakanta mahaifiyarsu a gabansu , a cikin iyayen kuwa wace ta fi gagawar saka zuciyar ƴaƴanta biyaya da daukan launin abinda take so itace uwa, uwa idan ta so za'a gyaru, in ta ki za'a lalace kuma a kan turbar da ta dora ne, Muna karbe du wani motsi na iyayenmu muna hanna su yi dan ba zamu iya muna zaune su motsa su yi wani abin ba bayan gamu a zaune, hanyar da suke bi ta nuna mana na mahaifinmu bamu da hurumi a ciki na matukar shiga zuciyarmu har muma muna gina tamu rayuwar a haka, idan har a gidan aure irin haka ta samu kuwa inaga da izinin mai sama jin dadin zaman auren zai samu domin akoy gannin kima da biyayar wanda ya ajiyeka...., Allah ya dafa mana)








A lokacin da Baba ya zo aka sha ruwa aka wuce masalaci sai kusan goma suka dawo suka zauna fan cin abinci, a kuma lokacin ne Aisha da zumudinta ta kawowa Baba kayan
💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔




*DA CIWO A ZUCIYATA*




💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔


_MALLAKIN_


*SAJIDA NIJAR*


*FREE BOOK NE* 8️⃣



LITATAFAN MARUBUCIYAR


Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar


Now


*Da CIWO A ZUCIYATA*






*Tallah, tallah, tallah*


*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*


_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_


Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes


*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata


Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃












Sosai Baba ya rasa bakin magana, sai dadagawa yake yi ,
Shi dai namiji ne bai san tsadar kayan mata a ido ba, in ba zuwa siya ya yi ba yakan hanki masu irin nauyi a idon nan haka a cen bangaren manyan kaya, bangaren abinda ya haura dari du kwaya daya, a yanzu haka wannan na hannunsa ya tabata kudi ne na mamaki, hakan ya sa ya dubi iyalinsa ya ce" Mamansu, kayan nan basu yi yawa ba kuwa?, Kayan nan da gani zasu yi tsada"


Murmushi ta yi tana dan sake ziga masa kunnun dake hannunta ta ce" Ai kama Abansu kayan nan zasu yi tsada sosaima, kuma ka ga na wajen mutuniyarka? Har cewa ta yi yau ko dan goron baka aika mata ba, dama jira nake yi idan ka zo ka gani abinda kace sai a yi in sha Allah " (not, kar ki ringa nunawa namiji a cikin gidansa a irin girma da daraja da Allah ya masa cewa bai isa da wasu manyan decision na cikin gidansa ba kece kika isa..., Tsakaninmu mu mun sam cewa muna da baban iko da rayuwarsu fiye da tunanin bawa, domin muna da damar tankwasa su a lokacin da su da kansu basu gane ba....., Yarda da hikima irin tamu ta siya mana haka ba nuna isa da takama ba, to wai wace isarma Allah na tuba ke da akace ki zo ki yi biyaya dan neman aljannarki? Ba gazawa bane dan kin bashi damarsa a matsayinsa na mai nemo gero da hatsi yana daukan decision din abinda ya shafe ku a cikin gidansa.......hakan ba yana nufin ki kasa juya abinki cikin hikima ba, cikin hikimar kina iya samun abinda kike so shima yake so ba tare da daya ya ga an tauye daya ba......, Allah ya karra hada kawunnanmu da Mai hause🥹😍)


Murmushi Aba ya yi yana girgiza kai ya ce" Hajia hajiar shagali, ai zan je da kaina na kai mata goronta , ama kuma ba za'a mayar da kayan nan ba, a tsakaninmu da mutanen nan inaga idan muka yi haka bamu kyauta ba, sai dai kin ga kudin shadar da na ba Elhaji? Zan koma na ce zasu je su zabo maku takalma da kudin, idan ya so kudaden takalman da wasu tanadin sai na karra mu fara shirin gudunmuwa, har sai na shiga tunanin nawa zan tanada ta gudunmuwa ?"


Mama ta miko masa kunnun da dan dumi ama kuma ba sosai ba tana murmushi ta ce" Abinda Allah ya hore maka, yadda ba zaka takura ba ba kuma zaka yi kauro ba, kai da kake da bikin a gabanka kaima?"


Ai kam ta saka shi dariyar, domin katon asusu ne ya bude yake jefa tanadi kulun ta Allah, da safe da kuma yama , tanadin da suke sakawa a tare domin itama in cenjin kayan miya aka yi sai ta kai ta zuba, a zaunen da take yan saide saidenta su lalle da salatif da dai dan abinda ba za'a rasa ba ta kayade riba na hawa tana zubawa, danma ya ki sana'ar a fita ne ai da samun ya fi haka.....haka dai suka cika darensu kafin suke kwonci dan murnar yau ta hanna masu kwonci da wuri


Kwana biyu tsakani Khausar ta shiga rabon anko ita da yan uwanta


Kusan abinda ke ba Kausar mamaki har ya bata dariya shine du wace ta kaima sai ta jefo mata tambaya fuska cike da mamakin wai dan Allah dama irin yadda zumuncinta yake da TAUFEEK ba saurayinta bane?, Har sai da ta gaji da bada amsar a tsare sai kawai ta katse amsar ta badata a hade dan maganar ta wuce, takan yi dariyar wannan kwabin da wani tunanin wasu mutanen, kai du wanda yake irin wannan tunanim ta yi waje ta ajiye shi a matsayin mutun mafi rashin fahimtar rayuwa gaskiya
In ba rashin fahimta ba ina mahadi? Ina hadi? , Eh lalle TAUFEEK ba wai ta girmeshi bane, haka kuma a yannayin jikinsa TAUFEEK ya fita tsayi kuma jikinsa kakauran jiki ne ba lange lange ba, ama sam bata gannin wata mahada ko kamanin dale iya sakawa mutane wannan banzan tunanin, ba wai da tana y'ar talakawa ba yana ɗan masu kudi ba, ko daya, ita bata taba raina asalinta da samun mahainfinta ba, kuma ta san masu kudin na auren talakawan su kilace cikin hukuncin mai sama, abinda ta gama sani ne ko giya take sha TAUFEEK ba abokin soyayarta bane, ba kuma abokin kalamai ire iren wadinnan bane, kai mtssss haka kawai ana nema a hade mata tunani? Tana zamanta ana hade mata lisafi? A gaskiya abin sai ya fara bata haushi da tarin dumbin uban mamaki..... karshe ta kawo na mujiya ta zubawa du mai mata kallon, in har a ganta da ankonsa ba zai cire tambayar nan ba a ran mutun to dan Allah ya rike tambayarsa a ransa abinsa




Yawan zuwa shagon Elhaji amsar atampopin masu hada mata kudadensu wata halaka ta kulu a tsakaninta da baban yaron Elhajin watau Mujaheed


Alaka ce irin ta shanshakai ta siyaya da farko farko, a hankali ta ringa karantar wasu sababin hulda a tare da shi da suka so bata tsoro, domin sai take tunanin cewa ta zo ne zata yi lokaci kalilan a shagonsu zai kula alakar dan ya tozartata ko dan ya mayar da ita costoma a wajensu ta yadda ko zuwa gaba bata da wajen cire anko sai shagonsu


A hankali kiran dake shiga tsakaninsu ya dan fara yawa, ya zamto ya fara sakata boyewa idan har zata amsa kira a cikin gidansu domin kamar jira ake yi yar rakani masai dinta ta kwashi tsuwa du sai a ratabo mata ido ba ga Maman ba , ba ga ya'yan maman ba, uwa uba ana daf da shan ruwan kwana na goma sha takwas da azumi a ranar Aba ya dawo da wuri wayar nan ta dauki tsuwar da ta saka yayan hanjinta yamutsewa dama ga abin yinwa na sakata juwa domin a irin lokacin nan du wani kayan buda baki a gabanta suke jira kawai take yi a yi gyaram murya a masalaci ko na tsokana ne ta daga ta maka sai kawai kiran nan ya shigo ya zamana Aba dake zaune saman darduma yana jan carbi sunna dan taba hira da Mama dake zaune daga kusan dakinta Auta a saman kan cinyarta ya yi matashi yau azumi yake kamar an summar da shi , su Aisha kuwa sunna gama wanke wanke dan su kam da sauki sosai sunna da juriyar azumi sosai da sosai kowa ya juyo inda wayar ke ajiye tana kuka irin na kashe kunnan nan tamkar mai son saka kurma ya ji tana ringin daf da yasashen hannun Kausar dake yashe ya sake du ya fice a hayacinsa


Da sauri ta dauke kanta, har zuciyarta bugawa take yi, wani takaici na neman kunnota gannin sunnan dake kai watau ATAMPA sai ta ji kamar tana dagawa ta kirta masa Alllah ya isa da masa tsakani da ita, to in ba yana neman sakata a halin ha'u'i ba a gaban Aba? Sai dai kashhh, a dole hawaye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login