Showing 27001 words to 30000 words out of 231718 words

Chapter 10 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt

Advertisement

28 Feb 2025

14926

sunanka kawai take iya kira, sannan kuma a cigaba da haƙuri za ta warke insha Allah"

Khamal yai ajiyar zuciya, Bayan samun cikakken bayanai, hankalinsa ya ɗan kwanta, kuma yayi imani zaluncin Na'ima ne yake ƙara tsorata ta, ya jefata cikin firgici, amma duk da haka abun na damunsa na yadda Abra ba ta magana.
Ɗaukan Abra ya yi zuwa waje, a hanya ya tsaya tare da siya mata kayan wasa kala-kala wanda zai ɗauke mata kewa.
Kai tsaye gidansa ya nufa, yana zuwa ya samu Ammi a Parlo da Granny sai few people ƴan uwan Na'ima.
Yadda Ammi ke kallonsa yasa ya ɗan shafa kai a hankali yace
"First love" Da sauri Granny tai farat tace "Kaga ƙadaddararriyar matar da Ubangiji ya haɗaka da ita? Mace babu rufin asiri ko kaɗan?" Murmushi kawai Captain yayi domin ganin jariri da mutane a zazzaune, ya tabattar masa da haihuwa Na'ima tai.
Ganin jaririn ya sanya ya mance da ɓacin ran da yake ciki... A hankali ya sauke Abra zuwa gefensa ya ɗauki Baby boy ɗin yana rungume shi.

"Abinda kayi ka kyuta yanzu? Kasan illar abinda hakan ke nufi?" Ammi tai maganar tana kallonsa.
Idanunsa akan Baby boy yace "I'm sorry first love ba zan sake ba"

"Uhm bana son Fitina, bana son zuwan yarinyar nan ya kawo sauyi tsakanin ka da matarka"
A hankali yace "In sha Allah, hakan ba zata sake faruwa ba"

baki Granny ta taɓe tana faɗin "yanzu wanne suna ka sakawa Yaron?"

A hankali yace "SALMAM KHAMAL KHAMIS" Ammi tace "Allah ya raya mai gidana Salman"

A ranar Khamal ya lallaɓa Na'ima ya yi, tare da bata haƙuri, gaba ɗaya ya manta da abunda tai masa, saboda murnar haihuwar Salman, yai ta mata faɗa akan abunda ta aikatawa Abra, da bayanin likita tare da misalta idan akan Salman haka ke faruwa ya za ta ji?.
Ta ce In sha Allah ba za ta sake ba, maganar iya baki ce domin bata kai zuciya ba, tana nan tana tunanin ta ina za ta sake ɓullowa lamarin.



Duk da tarin munafunci da zagon ƙasa, haɗi da almundahana da makaman da gwamnati take bayarwa saboda a bawa jami'an tsaro, amma su General Ibrahim  suke ha'inci akan su, anyi nasarar kuɓutar da 'yan makarantar, bayan tafka uban gumurzu, suka kashe sojoji sosai a wannan karon ma.
Wannan karon babu Captain Khamal, a wanda suka je opretion ɗin, amma shima anyi Nasara.
Wannan Nasarar da aka yi, ta raunata alaƙar da ke tsakanin Gwaska da General Ibrahim, har yake tunanin ko General Ibrahim ke ƙoƙarin juya musu baya.
Se da ƙyar sannan suka sasanta suka cigaba da yi wa harkar tsaron ƙasa ɓarna.





Shekarar Salman Biyu a duniya, lokacin Abra nada shekaru biyar, a lokacin aka ƙarawa Captain matsayi zuwa Major.

A lokacin kuma bincike ya tabbatar Abra bata da ƙarfin ji, ba sosai take jin magana ba kuma idan zatai magana da ɗan ƙarfi take.... (Conductive hearing loss)
Likitan ya shaidawa Captain wanda yanzu ya dawo Major, ya tabattar masa da idan aka sa mata hearing aid za ta da din ga ji.
Dan da fari Khamal ya zaci abun daga ƙwaƙwalwarta ne, se da ga baya suka gane, idan akai magana a hankali ba ta ji, se an ɗaga murya ko ta kalli bakin mutum, sannan take gane me yace.
Aka samawa Abra hearing aid, wanda Abbin ya bada kuɗi masu yawan gaske, aka siyo shi daga Germany dan yi mata amfani da shi.


General Ibrahim ya cigaba da cin karansa babu babbaka, tare da samun goyon baya, da ga manya manyan muƙarraban gwamnati, suka dinga kawo tarnaƙi ga matsalar tsaro, sannan ya cigaba da takun saƙa  da Khamal, mussaman da aka ƙarawa Khamal ɗin matsayi zuwa Major, tunaninsa kawai shi ne, yadda ze kawo ƙarshen Khamal, yayin da Khamal shi ma ya ɗora alamar tambaya akan General Ibrahim ɗin.

Bayan shekara Goma! (MAFARIN ƘADDARAR ABRA).

KAR KU BARI AYI BA KU, AKWAI TARIN SARƘAƘIYA DA BAN MAMAKI A GABA.

BRIGHT PENS
ZEE KUMURYA
NIMCYLUV
AYSHECOOL





LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.
[9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷*

Brigh pens✍️
Nimcyluv
Ayushercool
Zee Kumurya


             *P.....8*

Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks


https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949

https://arewabooks.com/u/nimcyluv


Elegant online writers

LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.


Abra ta sha wahala sosai zamanta a tare da Na'ima, samun sauƙinta kawai shine idan Major Khamal yana gari, ko kuma idan sun je gidan Ammi, ko idan ta na tare da Faris, wato Salman.

GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY.

MD ne wato Doctor GY a office ɗinsa, tare da wani mutum, GY ya gyara zaman glass ɗinsa ya kalli mutumin yace "wannan harƙallar ana samu sosai, zamu tura musu wannan mutumin da za suyi masa aiki, zasu turo mana da namu share ɗin".

Mutumin ya gyara zama yace "amma doctor baka ganin zasu iya ganewa, dan mu ci kuɗinsu za'a tura su india?"

"Ba zasu gane ba, ai ba yau muka fara wannan harkar da doctor Aman ba, shine shugaban Asibitin Darman Shakti, wannan ne karo na huɗu ina tura masa mutane, muna wannan harka"

Mutumin yace "Amma in balli ya tashi akwai damuwa fa"

GY yace "kar ka damu, ba wani balli da ze tashi, normal ne"

Mutumin yai ajiyar zuciya yace "Shikenan doctor, Allah yai mana jagora".


"Wallahi ranka ya daɗe, gaba ɗaya ji na ke aikin nan ya fita daga kai na, bana ƙaunar aikin nan yanzu gaba ɗaya".

"Subhanallah, amma meyasa ka ke jin aikin ya fita da ga ranka ba ka so?"

Cike da damuwa yace "Yanzu fisabilillahi abun da ake ya dace? Muna sadaukar da rayukanmu saboda ƙasarmu, amma manyanmu sun mai da ranmu ba a bakin komai ba, ƙirƙiri ga Nasara mu na kallo, amma se a dinga dakatar da mu?".

Major Khamal ya gyara zamansa, ya kalli matashin saurayin da ke ta mita yace "kai min bayani sosai yadda zan gane"

Matashin yace "Ranka ya daɗe, yaƙin da mu ka je ɗin nan, just recently, an gama shirya Komai mu ka shiga dajin nan, sedai ƙiri ƙiri aka hanamu harbi, su kuma kamar sun san dabarun da za mu yi amfani da su gurin yaƙin, su ka far mana da harbi, muna ji muna gani haka su ka far mana da harbi, se ɓuya mu kai Kamar wasu sakarkaru ba sojoji ba.
Shekaranjiya mun biyo ta wani ƙauye, an turamu wani aiki, ga mu ga 'yan ta'adda muna kallonsu, su na ta wucewa akan babura, sun rako wani Babban ƙusa a cikin su, wanda da ina gabda Allah ya sa mun kama wanda suka ɗakko ɗin, da mun karya alkadarinsu, dan a lokacin mun fi su yawa da kayan aiki a hannu, mu kai waya mu kace a bamu umarnin harbi, gamu gasu, amma se cewa a kai ba ruwanmu da su, kawai mu wuce.
Dan Allah ya rayuwa za ta yuwu da haka? Muna sanye da uniform amma ya zama aikin banza, sedai mu saka mu ɗau tsofaffin bindigogi muna hura hanci, idan munje yaƙi a fito a kashe mu, ba mu da kataɓus".

Ɗan shiruu Major Khamal ya yi Sannan yace "waye kwamandannku, lokacin da kuka je yaƙin?"

Cikin damuwa sojan yace "Captain Alex ne"

Ai yana cewa Captain Alex, a hankali Major Khamal yace "General Ibrahim"

A fili yace "Komai ze wuce insha Allah, idan irinku zaratan matasan sojoji na rasa karsashi suna ajiye aikin ya goben ƙasarmu ze kasance?"

"Yallaɓai to mu ya ta mu goben za ta kasance, da mu da iyalan mu da iyayenmu, idan an tura mu daji an hanamu kare kanmu balle ƙasarmu, in mun mutu wa ze kula mana da su?"

Major Yace "Allah yana tare da ma su zuciyar taimako, wadda ta ke aiki dan Allah".

Yai ajiyar zuciya yace "to shikenan Yallaɓai, Allah ya wuce mana gaba".

Major yace "Ameen, amma kar a karaya Please" jinjina kai yayi, ya gyara zaman bindigarsa ya fice.


TWO YEARS LATER....
Tsaye yake a ƙofar kitchen, ya zuba mata idanunsa, tana sanye cikin riga da skirt na English wears, ta na gaban sink ta na wanke wanke, gefe kuma ta ajiye littafi tana yi tana karantawa.

Murmushi ya yii tare da gyaran murya, duk da ya san ba jinsa za tai ba, saboda a hankali ya yi, cikin sanɗa ya je bayanta ya tsaya, ba zato ba tsammani ta waigo ta ganshi a bayanta, "Abbiii" ta faɗa a tsorace.

Dariya Salman ya shiga yi mata ya ɗan ɗaga murya yace "Matsoraciya kawai"

Ɗan tura baki tai tare da kai masa dukan wasa tace "shine zaka bani tsoro?"

Yace "Sorry Uktyna, Abran Abbi, kina aiki kina karatu?"

Tace "Eh mana, kasan from now, anytime our timetable can be fixed, amma kai kana yawon ball ko?"

Ɗan sosa kai Salman yai yace "don't mind me, dan Allah ki dafa min indomie mana".

Ɗan buɗe baki tai da mamaki tace "Ohh God, Faris kafin ka fita fa almost kai ka cinye Abincin rana fa"

"Eh, to ai ball nai gaba ɗaya ji nake kamar ban ci komai ba"

Abra tace "to yanzu dai kana gani aiki nake, bari in gama se in dafa maka"

Salman yace "let me help you with the dishes, bari in wanke se ki dafa mana"

Abra tace "ni a ƙoshe nake, kai ne dai sarkin ci gashi nan kafi kowa girma a gidan nan"

Salman yace "ke ma da za ki dinga cin abinci sosai kamar ni ɗin nan, da kin yi girma sosai, amma yanzu kalli ba wanda zece kece yayata, amma na ji daɗi gara a dinga cewa nine yayanki"

Dariya Abra tai tace "Koma dai menene nice Babba"

"Ba wani nan, in aka duba girma na fi ki girma, baki fi in goyaki in ta gudu da ke a cikin GRA ba"

Haka ya cigaba da tsokanar ta, ya karɓi wanke wanken, ita kuma ta ɗora tukunyar dafa masa indomie.

"Kai Salman meye haka? Me kake yi a kitchen?" Salman ya waiga ya kalli in da Mami ke tsaye a ƙofar kitchen ɗin, ita ma Abra waiwayawa tai tana kallon Mamin.

"Nace me kake a kitchen?"

Salman yace "Mami wanke wanke na ke ta ya Sister"

"Uban me ya haɗaka da wanke wanke, mace ne kai? Me ma kake yi a kitchen ɗin ba ka da aikin yi ne?"

Cikin sanyin halinta da son bawa ɗan uwanta kariya Abra tace "Eyya, Mami yi haƙuri ni nace ya tayani"

"Dalla rufemin baki da ke nake?" Abra ta ja bakinta tai shiru, Sam Salman baya jin daɗin yadda Mami ke treating ɗin su da banbanci, yana mamakin yadda Mami ke banzatar da Abra kamar ba ita ta haifesu ba, ko da yake ya ga Abbi ya fi son Abra, shi kuma Mami tafi son sa, amma duk da haka ai shi Abba baya hantararsa kamar yadda Mami kewa Abra.

Salman yace "Mami, ba Yaya ce ta sani wanke wanke ba, aiki take nace ta dafa min noodles, shiyasa na karɓa nake tayata".

"Dalla ajiye kwanukan nan ka zo ka fita ka bar kitchen ɗin" cikin tausayin yadda yayartasa tai kasaƙe tana binsu da ido, ya ajiye kwanukan, yace "to bari in karɓi girkin"

"Salman kana so in zageka ne ko? Ba zaka zo ka bar kitchen ɗin nan ba?" haka Salman ya bar kitchen ɗin jiki a sanyaye.

Idan da sabo Abra ta saba wannan halin ko in kula da Mami take nuna mata, amma sam hakan ba ya mata daɗi, tana son kasancewa da mahaifiyar ta ita ma, ta ji ɗuminta su yi hira, amma hakan yana faruwa ne kawai idan Abbi yana gari, da zarar baya nan, shikenan za su koma yadda su ke.

Salman yana nan Falo a zaune, Abra ta fito da plate a hannunta, sai tururi taliyar take, murmushi yai yace "Yawwa ƙanwata, Allah yai miki albarka" haɗe rai tayi tace "idan ba zan mayar ba"

Salman yace "Am sorry sweetheart, tuba nake babbar yaya, uwar son girma"

Ta ƙaraso ta ajiye masa plate ɗin abincin, ta ɗakko masa ruwa da kofi ta ajiye masa, ya ɗau plate ɗin yana cewa "tun da na fara jin ƙamshin Abincin nan nake salvating, Ko restaurant zamu buɗe ne?"
Abra tace "in dai zaka dinga girkawa shikenan, and please my bro, a ɗan tsagaita da yawon ball ɗin nan, ka ga exams zamu fara fa, amma baka da aiki se dai kaci Abinci, kai video games, se yawon ball wanda be dace ba, kaga Abbi yadda yake ta ɗawainiya da mu akan harkar karatunmu, ba sa jin daɗin result ɗin da kake kawowa a 'yan kwanakin nan. And bana jin daɗi inga ana maka faɗa bana so, dan Allah ka mai da hankali akan karatun ka ka ji dearna, You are brilliant before ban san meyasa ka dena son karatu ba yanzu, performance ɗin ka ya yi baya" maimakon yai mataa magana seya ɗage mata gira ɗaya.

"Ina maka magana kana ɗagamin gira"

Yai dariya yace "dariya ki ke bani ne, wai ke a dole ga babba kina faɗa, Sannu Mami"

Filon kujera ta jefa kwaɗa masa a ka tace "ina maka magana ka mai dani abun dariya ko?"
Cigaba da yai da dariya yai yana " 'yar ficikar Abbi, don't mind me, insha Allah zan baki mamaki this time around, ki mana timetable, zamu din ga karatu tare, in dai hakan ze saki farinciki".

"Wace irin jarabace ne wai Wannan? Na koro ka da ga kitchen, shi ne ki ka kuma biyo shi nan, meye hakane Abra, waike wace irin mara hankali ce ne?"

Salman yace "Ohh my goodness, Mami idan ban hira da 'yar uwata ba da wa zanyi? Mami idan ba ku ba wa muke da, wanda zamuje mu sake da shi haka? Meye laifin Yayata ne? Haba Mami? Yanzu haka faɗa takemin akan karatu, in mutum be shaƙu da ɗan uwansa ba to gurin wa zeje?"

Hajiya Na'ima tace "Ikon Allah, Au Salman har mun kai gaɓar da zan dinga faɗa kana mayar min akan wannan yarinyar? Kaga Salman ka kiyayeni"

Abra tace 'Mami kiyi haƙuri dan Allah.....

"Dalla rufemin baki, da anyi magana yenyen ayi haƙuri, ba yau ba gobe kuna liƙe da juna, ba ku san kun girma bane, kusancinku da juna ba shi da wata fa'ida ba?"

Kai tsaye Salman ya gane in da maganganun mahaifiyarsa suka dosa saboda haka yace 'haba Mami, ya zaki dinga Wannan maganar? She's my biological sister, meyasa zaki dinga kawo wannan tunanin?"

Ji tai kamar ta fasa ƙwai a gurin kowama ya huta, Salman ya ji Abra ba yayarsa bace, dan ba zata manta lokacin da ta taɓa gaya masa ba, befi 3yrs ba, dan haka baze iya riƙewa ba, amma da ta tuna kashedin Major, wanda  se ta haɗiye ba ta faɗa ba, dan haryanzu ba ta ƙaunar Abra, ko kaɗan.

Abra kam tuni ta bar falon, hawaye fal idonta, ta rasa meyasa Mami ba ta sonta, kuma ba ta san ta dinga zama da ɗan uwanta, tana son Salman sosai, da shikaɗai take sakewa se Abbi, dan ita ko ƙawaye ba ta da su, saboda ba ta son hayaniya sam, hayaniyar Salman kawai take iya jurewa.
Ta koma ɗaki tai shiru tana tunanin menene laifinta a gurin Mamainsu?.

Mami ta cigaba da zazzagawa Salman faɗa, kamar za ta dake shi.

Sallamar da akayi ne ta sata yin shiru tare da amsawa.

"Ke da waye ne kike ta wannan ɓaɓatu haka?" Cewar Anty suwaiba.

"Bari Anty suwaiba, ni da wannan sakarkarun mana, kullum yaron nan yana liƙe da wannan yarinyar sekace jaraba, na rasa irin wannan abu, nayi nayi amma yaƙi ji, abu kamar jaraba".

Anty suwaiba cike da duniyanci tace "ban da abunki idan be zauna da 'yar uwarsa ba, da wa ze zauna? Tsakanin ɗa da mahaifi ai se Allah".

Salman dai ko Anty suwaiba be samu kulawa ba, ya tashi ya fita tare da jin tausayin Yayarsa.

Suwaiba ta kalleta tace "Ke Na'ima meyasa baki da wayo ne? A garin wannan zafin ran da masifar taki wataran zaki faɗa abunda ake ta ɓoyewa, idan kuwa kika kuskura kika gayawa yarinyar nan ba ke kika haifeta ba, kin san mijinki baya Magana biyu ko? Kuma muddin ya sakeki ba ke kaɗai ya saka ba, har mu ya saka, dan Allah ne gatanmu Khamal ne gatanmu, duk asirinmu a lulluɓe a ƙarƙashin inuwar arzikinsa".

Hajiya Na'ima ta zauna tace "ni Wannan lamarin ya isheni, yau shekaru nawa yarinyar nan tana gidan nan, amma babu abunda ya canza, shawarar ki ba wadda ban amfani da ita ba, amma babu alamar zata bar gidan nan, yanzu na dena jin tsoron Khamal yace ze Aureta, amma Wannan shishshigin da yaron nan yake mata ne bana so".

Anty suwaiba tace "to ke ika ruwanki? Shekara uku fa ta bashi, ta ina ze Aureta kuma Khmal dai baze taɓa cewa ze aurawa ɗansa Ita ba, in dai ba ya so gayamata ba shine mahaifinta ba"

Na'ima tace "kin san wani abu kuwa?"

"A'a sekin faɗa"

'yadda Kamal yake fifita ta akan Salman ne ya ƙona min rai, ga ɗan da ka haifa ta sunna, amma ka maida shegiya 'ya kana nuna naka bakomai bane"

"To ya zaki yi, taki ƙaddarar kenan"

Tsaki Na'ima tai dan ji take kamar ta kori Abra daga gidan daurewa kawai takeyi.

Abra na ta jin daɗi gobe Abbi ze dawo, idan ya dawo zata tambayeshi tana son zuwa hutu gidan Ammi, dan Ammi tafi sonta akan Mami, babban abunda yake sake bawa Abra mamaki be wuce yadda ake cewa dangin mahaifiya sun fi son ɗa, akan dangin mahaifi ba, amma ita a nata dagin, dangin mahaifinta da mahaifinta sunfi sonta fiye da mahaifiyarta da dangin ta.
Domin ƙauracewa ire iren wannan tunanin, se Abra ta ɗaura alwala ta fara haddarta ta Alqur'ani me girma.

Saboda sanin halin Salman, na rashin jure yunwa yake sa Abra ta tashi da wuri ta ɗora breakfast, gashi kuma Abbi ze dawo gari, dan haka bisa al'adarta ita ke shiryawa Abbin nata Abincin da za'a karɓe shi, amma a wannan karon har gari ya waye ƙarfe tara Abra ba ta fito ba.
Hakan ya bawa Salman mamaki, dan haka ya wuce ɗakinta, dan jin ba'asi.
Yana zuwa ya tarar da ita ta dunƙule a bargo, se kuka take kamar wata 'yar yaye. Cikin hanzari ya ƙarasa gaban gadonta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login