Showing 210001 words to 213000 words out of 231718 words

Chapter 71 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt

28 Feb 2025

14676

wacce zan bawa Salman Please Alhaji Aliyu"

"Shi Salman ɗin ya ce baya son Afra? Kai Salman kana son ta ko ya ya?" Ya faɗa yana kallon Salman wanda zuciyar shi ta fara harbawa da jin maganar ta Abbinsa.
Kasa cewa komai ya yi sbd Kunya kansa a ƙasa.
"Kaga ni ma kamar uba nake wajanka kada kaji komai yanzu zan amsar maka auren Afra da izinin Ubangiji"
Salman ya ɗago kai suka haɗa idanu da Afra tayi saurin rufe fuskarta a jikin Ummi. Ya ce "E, Abba ina son ta and I want marry her"

"Masha Allah Ubangiji ya sanya albarka" ya juya kan Dr Bulama wanda ya kasa cewa komai ya ce "Dr muna neman alfarmar wajanka, idan babu damuwa muna buƙatar ka yarje mana akan nemawa Salman auren Afra" kafin Dr Bulama ya yi magana Ummi ta ce.
"Sannu Alhaji, yanzu ɗiyata bata da wani Uba wanda ya shige ni, ni ce uwarta ni ce uban ta, Abdullah zai zama waliyi a gare ta"

"Kada ki yi making decision cikin fushi uba, Uba ne komai lalacewar shi"

"Don Allah kayi mini wannan alfarmar zuciyata a kusa take"
Abba ya ce "To shikenan Allah ya yi mana maganin komai sai haƙuri"
Ummi tai murmushin baƙin ciki ta ce "Afra daman taku ce ni kawai ƴar kallo ce an baku ita halak malak"
Da sauri Adnan ya miƙe tsaye tare da Aishatul-humaira da sauri Mami ta ce.
"Adnan son Ina zaka da Mamana?" Kasa yi mata magana ya yi, ya nufi ƙofar fita tari na sarƙe shi ya fara yi babu ƙaƙƙautawa jini na zuba, Little ta fara kuka tana ƙanƙame mahaifin nata da sauri Abbi ya miƙe shi da Hajiya Mama.
Mami ta karɓi Little tana faɗin "Subuhanallah sannu Son" Abba ya kasa motsa wa tausayin tilon ɗanshi ya mamaye zuciyarshi amma duk abin da ya same shi, shi ne ya kawa kansa.

"Ya Salam sannu Adnan, Salman get the car immediately, zamu koma hospital" hankalin Hajiya Mama ya tashi suka nufi asibiti da Adnan Little na ihu tana buga ƙafa zata bi ubanta sbd ta fara gane shi.

Abba ya dafe kansa da hannu bibbiyu fargaba da tsoro ya cika masa zuciya. "Daman bashi da lafiya ne? Allahu ya sauwaƙe" Mami ta cewa Ummi "Amin ga grandchild ɗin naki nata rigima" Ummi tai murmushi ko inda Dr Bulama yake bata kallo yana son cewa zai duba Adnan amma babu mai yarda da shi. Jiki a saɓole ya miƙe tare da yin waje ko zai samu peace of mind

Yana fita wayar shi tai ƙara ganin number Saudat ya sanya ya yi tsaki jin kiran ya yi yawa ya ɗauka cikin faɗa ya ce "Wai ya akai ne?" Ta cikin wayar tayi dry sosai ta ce .
"Oh calm down Dr Yusuf Garba Bulama" ya buɗe baki da kyau ya ce "Ni kike kiran sunana haka?" Ta ce "Daga lokacin dana san ka san su waye yaranka, ni ma na shiga nutsuwata kafin dani dakai duk mu rasa mu fara yawo a titi ya sanya na nemawa kai na mafita, while before i say anything zan fara da wanda zai girgiza maka lissafi, ni ce na sanya a kwashe Mini yaran da Matarka Rumaisa ta haifa, aka maye gurbin su da matattun yaran dana bada kwangila aka sato suma a ranar aka haife su, na shirya wannan plan ɗin da P.a ɗin Hajiya Rumaisa tare da alkawarin zan bashi miliyoyin kuɗi, dana tabbatar ya ɗakko yaran kuma bana da kuɗin nasa aka buge motar ɗaya ɗakko yaran babbar mota tabi da kansu, nayi mamakin yadda yaran suka kuɓuta domin an tabbatar da P.a da motar ƙonewa sukai, abu na farko daya bani tabbacin jininka na raye saƙon da aka bani na baka, ina buɗewa naga photon wata budurwa mai kama dakai, tare da wasiƙar cewa jininka ce"

Tai dariya sosai kafin ta ce "Wannan ke nan, abu na biyu tunda yaranka sun dawo nasan kawo yanzu Matarka Rumaisa ta samu labarin aurena da kai da kuma ƴata Meenal, so dole zata ɗauki matakin cin amanar da kayi mata, kafin haihuwar guzuma ɗa kwance uwa kwance na kwashi rabona dana Meenal, duk wasu file na filayenka suna wajena wanda ka saka hannu da sunan Meenal kai da duk wani abu daka san ka mallaka, dan haka kayi ta kanka ina jiran takardar saki saduwar alheri"

Kusan mutuwar tsaye Dr Bulama ya yi "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un" ya shiga faɗa tare da faɗin "Na shiga uku" yana tsaye aka fara masa messages an rufe dukkan wani acct bank ɗinsa, daga na gida zuwa na company har na asibitin wanda kuma aikin Abdullah ne ko Ummi bata sani ba ya fita zuwa baya ya shiga kiran ma'aikata.

Dr ya fito da sauri daga room Abba ya kasa haƙuri ya ce "Dr ya jikan son me ya sa me shi ina ɗana" ya buga ƙafaɗar Abba ya ce "just pray for him Ita yake buƙata" Hajiya Mama ta saki kuka ta ce "Kaga abin da kake shirin jawa Adnan? Me ya sa ba zaka taya shi neman abin da yake so ba? Gashi nan zai rasa rayuwar shi yabi matar tasa" Abba dai ya kasa magana Abbi ya ce.
"Insha Allah za a ba shi auren Afra indai a kanta ne" cikin sauri Abba ya ce.
"Kasan Allah idan har ina raye Adnan ba zai taɓa Auren Afra ba" yana faɗin haka ya nufi office ɗin Dr ya same shi zaune bayan sun gaida Dr ya ce.
"Adnan ya samu ciwon zuciya wani gefe har ya fara kumbura ayi ƙoƙarin nema masa abin da zuciyarshi ke buƙata kafin mu samu ya farfaɗo daga dugun suman da ya yi"
Abba ya ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un yanzu sai yaushe zai farka?" Dr ya ce "for now ba zan iya cewa komai ba, sbd jikinsa ya yi tsanani da yawa anyi wasa da zuciyarshi" da sauri Abba ya fita waya kare a kunnenshi.

Daƙiƙo na juyawa zuwa sekonni, sekonni na juyawa mintuna, mintuna na juyawa zuwa awanni, a hankali suke sauyawa zuwa yini daga yini zuwa kwana. Adnan ya ɗauki wasu kwanaki kusan arba'in a gadon asibiti ba tare daya farfaɗo ba. Har lokacin Ummi na ƙasar gidan Abbi, Bulama kullum sai ya zo Ummi bata kula shi bata nuna masa ta san Abdullah ya rufe komai nasa ba, shi ma Bulama ya kasa cewa komai. Saudat ya yi neman duniya ya rasa inda zai sameta daga ƙarshe ma wayarta baya shiga.

A hankali ya shiga buɗe idanunshi wanda sukai masa sosai da sauri ya mayar da idanun ya rufe sbd hasken da ya yi masa yawa. Slowly slowly ya ƙara trying na buɗe idanun, har ganinsa ya sauka akan drip dake maƙale a jikinsa.
Hannu ɗaya ya sanya ya dafe kansa dake masa ciwo a hankali ya zame hannun zuwa saitin zuciyarshi dake bugawa da ƙarfi yana jin ciwo sosai ta cikinta.
"Allahamdulillah son ka farka?" Hajiya Mama ta faɗa tana yin waje kiran Dr da kuma Abba da Abbi da suke waje suna tattaunawa akan a fitar da Adnan ɗin ƙasar waje.
Salman ya gyara tsaiwa ba tare da ya kalli Adnan ɗin ba, duk da cewa yana jin tausayi shi. Fararen idanunta ta ɗaga kaɗan tana kallon inda yake kwance da sauri ta ɗauke sbd wani abu mai kama da tausayi da taji..
Dr dasu Abbi suka shigo bayan Dr ya gama duba jikin ya ce.
"Allahamdulillah yanzu saura a ɗora shi akan magani" Abba ya yi murmushi yana faɗin "thank you Dr"

"Son ya jikin?" Cewar Abbi. Adnan ya buɗe idanu sosai kallon shi ya sauka kan Afra dake kusa da Salman, ya runtse idanun zuciyarshi na ƙara bugawa ya kalli Abbansa, da Hajiya Mama sai kuma Abbi. Ƙamshin da yaji a gefen shi na dama ya sanya ya juya dan ganin waye, ya zabura jiki na rawa ya miƙe zaune yana ƙara kallon wacce ke dab da shi, ya ƙara juyawa ya kalli ɗayar wacce ke kusa da Salman.
Ya mustsika idanu tare da diruwa daka bed ɗin yana tsinke ruwan hannunsa. "Abba idanuna ya samu matsala me ya sa Afra ke rabewa gida biyu ne?" Abba yai murmushi ya ce "A Lallai mukan ras namu idanun suke, mata biyu ko wacce daban" Adnan da jikinsa ke rawa sosai ya ƙara kallon wacce ke can kusa da gadon shi ko ɗago kai ba tayi ba, ya sake kallon wacce ke kusa da Salman, ya juya ya kalli Abba.

"Your wife Abra khamal Khamis" cewar Abbi Innalillahi da wani irin sauri Adnan ya nufi wajan wacce ke kusa da Salman yana zuwa Salman ya girgiza kai yana sakin murmushi ya ce. "No! Wannan is no longer your's. Is not your Abra is mine"
Adnan ya juya ganin haka ya sanya wacce ke zaune kusa da gadon ta miƙe tana tsare shi da idanu sosai alamar "Don't ever trying to come" da wani irin sauri Adnan ya nufeta gadan-gadan tamkar mahaukaci.....

Contact to subscribe
09047871750
[11/27, 12:18 PM] Abk: A gigice Adnan ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya sa ba kuma haukacewa zan yi ba, dan Allah ku tasheni idan bacci nake, ko dai nima mutuwa na yi ne, muka haɗu a lahira?".

Abba ya ce "Ba mutuwa kai ba, da ranka abin da kayi ka ke girba, tunda an salameka sai ka tashi mu tafi" A rikice Adnan ya nufi Abra zai damƙota, amma ta zura da gudu ta ɓuya a bayan Abba, tana kallon Adnan.
Afra ma tashi tayi ta koma kusa da 'yar uwatta, tare da riƙe hannun Abra , cike da so da ƙauna.
Adnan ya kuma nufo su, Amma Abba ya tare shi, ya ce "Ai baka isa ba, yanzu kazo mu koma gidan Major, zamu gabatar da ita ga mahaifinta da kuma mahaifiyarta, sannan ka zauna ka gaya musu abin da ka aikatawa 'yar su".

"Abba dan Allah kayi mini rai" Adnan yai maganar yana haɗa hannayensa biyu.
Abba ba sani ba sabo, ya haɗe rai ya dinga yiwa Adnan tsawa, suna fitowa daga ɗakin, Salman ya kuma rungume Abra, ji yake tamkar mafarki ne, ga Abransa a kusa da shi, abu kamar mafarki haka yake ganin faruwar abubuwan, Abransa is alive.
Wani baƙin ciki ya kishi ne ya mamaye zuciyar Adnan, zai yinƙura yai wajen su Salman Abba ya ce "Wallahi kai mini wani hauka, sai na ci mutuncin ka a wurin nan, wuce mu tafi" Duk in da Abra ta waiwaya 'yan uwane masoya ke ta farincikin sake ganinta.



Suna zuwa gida, suka tarar da Mami, ta na ta rusawa Ammi kuka, tana cewa  akan me Major ya ɓoye mata Abra tana raye, ya jefa zuciyarta cikin ƙunci.

Ai Abra ba tayi sallama ba, ta tafi da gudu, ta danne Mami tana wani irin kuka kamar wadda ranta zai fita.

Kasa magana suka yi, daga Mami har Abra, tamkar Mami zata mayar da Abra cikinta, 
falo ya cika ga Ammi ga Abba da mahaifin Abbi, ga su Inna da Yaya Musa, gida sai koke koke ake, Ammi ta tsare Abba da son jin dalilin da ya sanya, suka aikata musu haka a kan Abra.
A hankali idon Abra ya sauka a kan Little da ke hannun Salima, Abra ta zubawa Little ido.
Ammi ta ce "Kawo mata 'yar ta ta ganta, taji ɗumin 'yar ta" girgiza kai Abra tayi ta ce "Ni ba 'ya ta ba ce"
Gaba ɗaya suka kalleta, Ammi ta ce "wane irin abu ne haka kuma?".

"Ammi na barwa Adnan 'yar sa, ina son su fita daga rayuwata gaba ɗaya da shi da ita" tai maganar tana kuka.
"Baki da hankali ne? 'yar ta ki kike cewa kin barwa babanta?".
"Eh Ammi, nima haka na rayu ba iyayena, har gara ita tana da uba"
Abbai zai tsawataraa Abra, amma Abba ya ce "Ƙyaleta Major, tayi mini daidai, amma muna dakon jiran wani albishir da zamu yi miki ne, kan mu fayyace musu yadda aka yi mu kai musu haka ba su sani ba".


Harabar gidan Major ta cika da motoci, sai hayaniya ake ji ƙasa ƙasa tun daga harabar gidan.
Falo ya cika ya batse da mutane.



A tsawon Kwanakin da Rumaisa ta yi a gidan Major, taga gata da karamci, kullum Afra tana tare da ita, ga Salman da take jin shima kamar nata ne, ga kuma Little da aka ce 'yar ta ce ta mutu ta bari, gashi suka yi wani irin sabo da Na'ima, duk da zasu yi sa'anni da Naima, amma Rumaisa tana girmamata kasancewar ita ta riƙe Abra. Bulama yana nan garin Kano, kullum cikin sintiri yake gidan Major, dan ganin Rumaisa da 'yarsa da kuma jikarsa, amma sam Rumaisa tayi mursisi ta dinga surfawa Bulama rashin mutunci, dan babu babban abinda ya ƙara mata tsanarsa irin jin shine dalilin da ya sanya ta rasa 'yar ta a karo na biyu, bayan sace su da aka yi da fari.

Rumaisa ta fito falon, jin yadda gida ya cika da mutane, sai dai babu zato babu tsammani idanunta suka sauka a kan Abra da ke kusa da Salman, ga kuma Afra a gefe guda. A gigice ta nufi wurin da Abra take tana sambatu.
" 'ya'ya na, duk nawa me sun dawo basu mutu ba 'ya'yana ne, Abdallah zo ka gani" Rumaisa tayi maganar tana nuna Abra da Afra.
Ƙurii Abra ta yiwa matar da ido, ko ba a gaya mata ba, tabbas wannan matar suna da alaƙa.
Zuwa tayi ta rungumesu gaba ɗaya, ta dinga gunjin kuka, har mayafin abayarta ya cire, dogon gashinta bar tsakiyar bayanta ya sauka, tayi larabci, tayi Hausa tayi turanci.

"Abra she's your Mum" Abbi ya faɗa yana kallon Abra.
Wani irin zillo Abra tayi, itama ta rungume matar, tana jin wani abu ya ratsata ba tare da ta gane takamaimai menene ba.

Bulama ne yayi sallama ya shigo, yana sunkuyar da kai tamkar munafuki, yana sunkuyar da kai, Yaya Musa me ya ce "Laa Inna, baki gane wannan ba?".

Inna ta ce "Ina zan manta shi, baƙin tsinanne, aka kashe mini miji a Asibitinsa, shi kume meye ya kawo shi nan, baƙin Azzalimi, muna ji muna gani yaƙi zuwa kan bawan Allah nan har ya mutu" Waro idanu Afra ta yi ta ce "Kenan kai kayi sanadiyyar mutuwar Mutumin da ya riƙe ni kamar uban da ya haife ni?"

Adnan ya ce "Ba mutuwar mariƙinsa kawai ba, har da kisan 'yar sa a Asibitinsa wadda ta kasance matata Abra, sai dai gata nan a gabana, na kasa gane mafarki ne ko zahiri".
Bulama ya samu wuri ya zauna, ya sunkuyar da kai yana zubar da hawaye, ya ce "Haƙiƙa wannan ishara ce Allah ya nuna mini, mutane sun rasa rayukansu a saboda sakacina, da sa neman kuɗi a gabana fiye da lafiyar mutane mugun halina ya zame mini DARE DA DUHU, babu lallai 'ya'yana su ƙaunace ni, sakamakon kowacce na bar mata wani tabo mai tsayawa a zuciya, dan Allah ku yafe mini, dama hausawa na cewa, idan kana mugunta ba ka yiwa kanka ba, baka iya ba, na watsar da dangina, na zalunci matar da ta mini halacci, an salwantar da rayuwar 'ya'yana, wadda na riƙa da soyayya ta ci Amanata, gaba ɗaya rayuwata ta zama DARE DA DUHU, da bana tunanin garin zai wayewa wannan duhun dare nawa, ku yafe mini dan Allah".
Rumaisa ta ce "Wallahi ba zan baka yarana ba, kuma ka tattara duk wata dukiya tawa ka bani abata, wadda ka cinye kuma, zamu haɗu a kotu, sai ka biyani"

"Rumaisa duk hukuncin da kika ɗauka a kaina daidai ne, amma ni ya aka yi naga Abra, bayan an sanar da ni ta rasu?".

Abba ya ce gyara zamansa sannan ya ce "Eh wannan bayanin duk shi ne ya tara mu a nan, Adnan ya auri Abra ne bayan ya gano 'yar ka ce, dan ya ɗau fansar abin da kayi masa, na sakaci mahaifiyarsa ta rasa ranta.
Tsawon zaman da Abra tayi da Adnan...

Adnan ya katse shi ta hanyar cewa "Dan Allah Abba kayi mini rai"
A fusace Abba ya ce "Zan tsinka maka mari, ka mini shiru mutumin kawai".

Abba ya ɗora da "Ya auri Abra, duk muna sa ran ya samu yarinyar kirki, suna zaune lafiya, ashe ba baka bane ba, sai ranar da Abra ta kusa rasa ranta, ya gigice ya dinga faɗar irin zaman da yai da ita, ya dinga azabtar da ita, bayan mun dawo daga wurin likita, ya bamu shawarar idan ta warke daga C.S ɗin da aka yi mata, a kaita India, saboda suna da ƙwararrun likitoci da Asibitocin da suka ƙware, a wurin bada kulawa ga masu ciwon, kuma tun da bata kai last stage ba, zata iya warkewa.
Daga nan na fara processing yadda Abra zata tafi India, katsam Adnan da bakinsa ya dinga faɗar yadda ya rayu da Abra, bayan an mata C.S jikinta ya rikice, duk mun ɗauka ta rasu, a lokacin da shi mijint, da Salman da ita Maman Salman duk sun suma, Nurses sun basu ɗaki, likitoci suka zo suka dudduba Abra, ba su ce mana komai ba, suka dinga mata ƙoƙari, suna dannna ƙirjinta suna mata allurai, har Major yana cewa kar su wahalar da gawar Abra, suka ce masa bata mutu ba, suganta ne yayi ƙasa fiye da kima, jinint ma ya sauka. Cikin ikon Allah ta cigaba da numfashi, amma bata hayyacinta, a ranar na buƙaci Major, da kar mu kuskura wani ya san Abra bata mutu ba, saboda za'a kaita India ne babu tabbacin ta dawo da rai, dan haka kar musa musu rai, na ɓoye masa ainihin dalilina na rashin san kowa ya san Abra bata mutu ba.
Muka tafi da Abra Abuja, na barota ita da Major, kwanan su ɗaya a General Hospital Abuja, suka tafi indiya, likitan da ya dubata ya mata cs, suka haɗamu da da likitocin Asibitin da za'a kai Abra. Cikin ikon Allah ana kaita suka karɓeta, muka biya komai aka fara bata kulawa ta musamman.
Lokacin da Maman Salman ta farfaɗo mun sanar da ita, an kaita gidana an mata sutura a binneta, duk da tayi mita a kan danme za a rufe Abra ko sallama ba suyi ba. Haka Adnan muka tabattar masa da an kai gawar Abra Kano, an binneta. Major ya baro Abra a can india, amma duk sati biyu ko ni ko shi, muna zuwa mu dubata, a nan Nigeria kuma, mun saka anata saukar Alqur'ani, har umara muka biya akaje aka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login