Showing 192001 words to 195000 words out of 231718 words
Chapter 65 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt
hakan ya sa ta shagwaɓe fuska ta ce. "Yaya Musa ne ba shi da lafiya, shi ne Inna ta ce wai yau ni zan ɗebo ruwa."
"Ina ne gurin ɗibar ruwan?"
"Bayan nan ne." Ta yi maganar tare da nuna masa hanyar.
Bai ce komai ba ya karɓi botikan suka jera suna tafiya. Gurin ɗiban ruwan rijiyoyi ne da yawa, mutane mata da maza kowa ya zira gugansa yana ɗiba. Ƴar Baba na zira guga Adnan ya karɓa ya fara janyo ruwan yana zuba mata a cikin botikan, bayan sun cika ya ɗauka ya kai mata har ƙofa gida, ita kuma ta ɗauka ta shiga da shi ciki. Haka suka dinga yi har ƴar Baba ta cika komai na gidan.
"To ko ke fa, ba ga shi har kin gama ba, sannu Allah ya saka da Alkhairi, amma yau kin yi sauri, hala babu layi ne a gurin?" Inna ta faɗi haka lokacin da Ƴar Baba ta dire bokitin ƙarshe.
"Ke dai ba na deɓo miki ruwan ki ba?"
"To ai na ga da in kika tafi ɗiban ruwan sai ki wuni akan bokiti ɗaya, kina ta neman magana a can."
Tura baki ta yi ba ta ce komai ba ta fita gurin Adnan dake jiran ta a waje. ganin yadda duk ya jiƙa wandon jikinsa ya sa ta kwashewa da dariya har da ƙyaƙyatawa. Ɓata fuska ya yi ya ce. "What's funny?" Girgiza kai ta yi tana cigaba da dariyar. Ɗage kafaɗa ya yi ya ce. "Gurin Inna na zo mu yi magana a kan ki, sannan in sanar mata iyayena za su zo neman aurenk.."
"Taɓ, wallahi ni bana son ka ba zan aure ka ba." Ta katse shi da faɗin haka cikin serious dake tabbatar da abin da ta faɗa har cikin zuciyarta haka ne.
Littafin kuɗi ne, ku biya kafin ku karanta. 09047871750
[11/14, 9:13 PM] Abk: "Are you sure baki so na ba zaki aure ni ba?" Adnan ya faɗa cikin tsoro da fargaba maganar data nemi ta sar masa da mikin dake damun zuciyarsa na rashin Abra.
"Ni fa ba zan taɓa aurenka ba, gaskiya kayi mini baƙi da yawa kuma bana son ka shi ne kawai....,"
"Stop it.." ya faɗa a tsawa ce yana riƙe saitin zuciyarsa dake masa zafi lokaci guda, kalaman bakin Afra na neman sauya masa lissafi. Kasa magana ya yi sai idanunsu daya rufe zuciyarsa na harbawa.
"Na kawo maka ruwa kasha ne, naga kamar ka ƙware?" Ɗago jajayen idanunshi ya yi tare da zuba mata akan fuskarta wanda a kullum take masa gizo, ƙarfin hali yake kawai na Kasancewar su tare da yawan lokota sai ya ji kamar ya jawota ya rungometa ya faɗa mata how much he loving her!
Ya sauke numfashi a galabaici yana kallon yadda tai shiru tana binsa da idanu. Ba tare da ya ce komai ba ya juya ya bar ƙofar gidan nasu.
Ita ma bata kira shi ba, amma har zuciyarta ta ji babu daɗi a shirunsa da tafiyar ta shi, zuwa yanzu ta fara sabawa da shi.
"Wannan karan kuma mene ya faru kika shigo jiki a saɓule kamar kazar da ƙwai ya fashewa?" Inna ta tambayi Afra wacce ta shigo tana bin bango ta luuula duniyar tunani da alama bata ma san abin da Innar ke faɗa ba.
"Yau naga abin da ya ishe ni, anya yarinyar nan lafiyarki ɗaya kowa? Ina ta ɓaɓatu kin yi mini shiru?. Haka kurum kada naje ina tufka wani na warware mini ita na shiga uku"
Nan ma dai Afra ba ta ce komai ba sai bin bango da tayi ta zauna tana wawware idanunta. "Kee! Kee!! Ƴar Baba?"
"Na'am Inna"
Afra ta faɗa a gigice bayan Inna ta girgiza kafaɗarta.
"Lafiya ke dawa,ina kika je bayan kin kawo ruwan?"
"Gasky Inna tambayarki ba zata mutum ya yi ilimi ba, tunani nake fa amma gaba ɗaya kinsa na manta abin da nake ina jinki fa" Inna ta riƙe haɓa tana faɗin..
"Tunanin uban me kuma? Salon ki kawa kanki ciwo" ganin hawaye a fuskar Afra ya sanya jiki babu ƙwari Inna ta tana tambayar lafiya Meke faruwa da ita haka?..
"Inna tun bayan mutuwar wanda zan aura har yanzu babu wanda ya ce yana so na zai aureni, haka zan ta zama kenan kalli ƙawayena ko wacce tana yaranta abin sha'awa wasu kuma ciki garesu"
Cikin kulawa irin ta Uwa da Ƴa Inna ta kama hannun Afra tana cewa.
"A'a Ƴar Baba shi aure lokaci ne, na sha faɗa miki da lokacin ki ya yi ko bakya so sai kinyi auren nan, zaki auri miji wanda babu irinsa a garin nan ƙyakƙyawa ƙin kowa sai wanda ka taɓa,
Ba kiga kalarki ba wanke hannu ka taɓa kada ki saka wannan a ranki muna ta addu'a kema kici gaba da yi"
"Kuma bakya tunanin sbd bani da iyaye ba a zuwa neman aure na Inna?" Yanayin yadda ta yi maganar a raunace ya sa Inna yin shiru ita ma abin yana susa mata zuciya ainun bata da yadda za ta yi ne.
Ɗaki Afra ta shige zuciyarta babu daɗi abubuwa suka dawo mata sabbi a rai. Tana jin kamar bata kyautawa Adnan ba, bata ji daɗin yadda ya tafi ba babu farin ciki akan fuskarsa kamar kullum. Kuma ba lallai ya dawo ba. Kuka ta fashe da shi na rashin abin yi a haka bacci ya ɗauke ta.
Tun da ya shigo ɗakin ya kasa zaune ya kasa tsaye "Bana son ka" kalmar ta tsaya masa a rai, ashe haka ake ji idan an cewa mutum ba a son shi? Yaya matan da suka dinga son shi a baya suka ji a zuciyarsu? Afra akwai wauta amma zantunkan bakinta daga zuciyarta suke, babu alamar ƙarya ko wasa a cikinsu tana nufin abin da ta ce ne.
"What should I do? Adnan think, think" ya faɗa a hankali yana rufe idanunshi. Ba zai fushi da ita ba,amma dole ya ɗaga mata ƙafa domin fahimtar zuciyarta.
Wayarsa ya ɗauka ya kira Hajiya Mama tana ɗauka ya kwaɓe fuska tare da langwaɓar da kansa gefe guda.
"Son ya dai?" Cikin ƙasa da murya ya ce "Evening Hajiyata" ta amsa da "How are you? Ya zaman village? The you like it"
"Sure Mama, kawai ki tayani da addu'a wani abu na neman tunkaro ni kamar zai bani wahala kuma" Hajiya Mama bata fahimta ta ɗauka al'amarin aiki ne hakan ya sa ta ce.
"Addu'a kam kullum muna yinta Sp Adnan Aliyu Matawalle, Allah ya taimaka ya baka sa a Insha Allah zaka samesa cikin sauƙi"
Idanunshi ya lumshe yana jin nutsuwa na saukar masa a hankali ya mirgina gefe yana jan numfashi ya ce.
"That's why i always love you Mom..."
Murmushi tayi cike da jin daɗi domin tana ƙaunar Adnan ji take kamar ita ta haife shi duk da cewa ita bata taɓa haihuwa ba, maybe bata ɗaya daga cikin matan da suke haihuwa a nan duniya.
"Hajiya, Abba...." Ya faɗa cike da rauni domin ya fara gajiya Abba shi ne cikon jin daɗinsa dama samun nasarar baki ɗaya, sai da shi duniyarsa ke zama cikakkiya.
"Me Abba ya yi kuma Adnan?" A kasalance ya ce. "He still angry with me na rasa yaya zan yi ne bana jin daɗin"
"Adnan my Son kada ka damu da hakan, Abbanka surprise ɗinka zai yi very soon ka mai da hankali kawai wajan yin aikinka Please" Hira su kaci gaba dayi cikin nuna soyayya a haka Adnan ya manta da ɓacin ran da Afra da haddasawa zuciyarsa.
Yau ranar kirkin Mami ne tana zaune gefen gadonta lokacin kusan ƙarfe goma na dare ne, ta shirya cikin wasu haɗaɗɗun kaya na barci, hannunta ɗauke Aishatul-humaira wacce taƙi yin barci yau sai dry ta kewa Mami tana ɗaga ƙafa duk ta cire sosan da aka yi wa kanta ado da shi.
"Sweetheart yau hirar dare za mu yi kenan, kwana biyu daddynki bai neme mu"
"Idan ba Dady ai akwai grandfa right?" Abbi ya faɗa yana shigowa cikin bedroom ɗin sanye yake da ƙyakkyawar shiga ta barci sai ƙamshi yake zabgawa.
Mami bata kallesa ba hankalinta akan Aishatul-humaira iya kuzarin yarinyar abin sha'awa ne. Hannu ya sa ya ɗauki little yana mata wasa amma ta ɓata fuska alamar anyi mata ba daidai ba.
"Wato Na'ima na saka ki a bedroom tana hure miki kunne akan Granny naki ko, shi ne zaki ɓata fuska?" Kamar Aishatul-humaira ta fahimci abin da ya ce ta fashe da kuka sosai tana cilla ƙafa, Abbi ya waro ido yana miƙa wa Na'ima ita ya ce.
"Wannan soyayyar taku daga Allah take, maza ki bata haƙuri" jijjigata ta dinga yi a haka tai barci tana sauke ajjiyar zuciya. A nutse Mami ta kwantar da ita bayan tai mata addu'a ta miƙe zata bar ɗakin "Na'ima" Abbi ya kira sunanta yana bin jikinta da kallo ƙamshinta na fisgarsa zuwa gare ta.
Wajanta ya ƙarasa ya tsaya daidai bayanta tare da saƙalo waist ɗinta da hannunsa biyu cikin ƙasa da murya ya ce "Ni kike azabtarwa haka Na'ima? Ba zaki amshi wannan auren matsayin ƙaddararmu baki ɗaya ba? The you know how much i miss You? Baki san adadin son da nake miki ba ko?" Juyo da ita ya yi gabansa yana kallon yadda hawaye duk ya ɓata mata fuska ta wani shagwaɓe fuska.
"Am sorry first love uwar gidan Major Khamal Khamis, ki yafe masa mana?" Ɗaga ta yi suka haɗa idanu ta ɓalla masa harara dry ya yi mai sauti yana jawota baki ɗaya zuwa jikinsa ya matse ya ce "Ohhhu dai naji, muje na nuna miki wani abu?" Ya faɗa yana sumbatar wuyanta tare da janta zuwa other bedroom.
Washegari abin har mamaki ya bawa Salima ganin har 12 Abbi bai fito ba, kamar yadda ya saɓa ɗakinta ya tashi da wuri ya duba Na'ima da little ɗin. Tana zaune a Parlour watching TV taji dry ƙasa ƙasa da sauri ta juya zuciyarta ce ta buga ganin Na'ima cikin wani dakakken lace mai masifar kyau, sai Little a hannunta wacce ta farka tuni ita ta tashe su ma, Abbi ya saƙalo jikin Na'ima shi kansa bai san adadin son da yake mata ba. Zama sukai a saman Kujera Salima tai murmushi ta ce "Barka da fitowa honey?"
"Yawwa Barka baby" ta juya kan Na'ima wacce take latsa waya tana ƙoƙarin ɗaukansu a photo ta turawa Salman "Maman Salman an tashi Lafiya?" Mami na ɗora kai a shoulder ɗin Abbi kamar dole ta ce.
"Ya kike?" Kalmar ta daki zuciyar Salima sai kawai ta share, Naima na ƙoƙarin turawa Salmanun-faris photos taji Sallamar sa da sauri ta miƙe tsaye tana mmki, yana tsaye bakin ƙofa cikin wata dakakken shadda kyan da Salman ya yi ya ɓaci, ya zama cikakken matashi wanda samun kamarsa za a daɗe ga haiba da kwarjini. Cikin sauri ya ƙarasu yana ɗaukan Little wacce ta kafesa da idanu irin ta ganesa ɗin nan "My sweetheart my happiness daddy is here...
Tsayin kwanaki uku ciff Adnan ya ɗauka bai sake haɗa hanya da ƴar Baba ba, hankalinsa akan aikin daya kawosa baya son haɗa abu biyu domin ya fahimci yarinyar na neman bashi ciwon kai. Cikin ikon Allah ya samu nasara cikin daren wata rana aka zo aka tafi da Ɗan kunama da sauran muƙarrabansa. Adnan kuma ya ce akwai abin da ya ke jira. Amma duk wanda ya gansa ya san baya cikin nutsuwar ya faɗa tsoro da zullumin yadda zai ƙara tunkarar Afra a lokaci na barkatai suka ƙara wanzuwa a ransa, neman aurenta ya bambanta dana Abra domin cikin lokaci kaɗan ta amince masa.
Ƴar Baba na kwance abin duniya ya isheta ko abinci kaɗan take ci, tunanin rashin ganin Adnan kwana biyu ya addabi zuciyarta. Inna dake zaune ta juya tare da kallon Afra ta ce "Yau idan baki faɗa mini abin da ke damunki ba, babu abin da zai hanani yi miki doka wallahi"
"Haba haba don Allah Inna dame zanji ne wai? Kawai baki san meke damuna ba kici zaki dakeni, ko na faɗa miki cewa zaki aljanu suka shafan nidai kawai ki barni da abin da ke damuna"
Miƙewa tsaye Inna tayi tan ɗakko abin doka ta ce "Bari dai ki gani, kina zaton ba zan iya bugunki ba ƴar butu uwa kawai ja'ira" da gudu Afra ta bar gidan bayan ta ɗauki mayafinta.
"Kinibabbiyya ki tsaya mana kiga yadda zan yi dake yarinya ta mayar dani kamar kakarta" Inna ta faɗi haka tana ajjiye abin dokan data ɗakko.
Adnan na tsaye a ƙofar gidan cikin wasu ƙananun kaya masu kyau ya saka sunglasses a idanunshi ya harɗe hannayensa a ƙirji. Kamar daga sama ya ga ta fito tana haki ganin tana ƙoƙarin yin gaba ya sanya hannunsa tare da kamo nata.
Jin an riƙe hannunta tayi saurin waigowa idanunta ya sauka akan sa bata taɓa tunanin zata gansa ba, ganina ya sanya ta masa ƙuri da idanu wanda suka cika da hawaye. Baya ta juya masa tana sakin kuka tako a hankali cikin nutsuwa zuwa inda take suka fuskanci juna, tallafo fuskarta yai yana kallon yadda take kuka sosai kamar wacce ya daka me hakan ke nufi? Kewarsa tayi ko mene? Ita da ta ce bata son shi.
"Mene? Why are you cry" ya tambaya a hankali turo baki tayi tana ƙara fashewa da kuka. Adnan ya dafe kai ya ce "Goodnight Zaki tarwatsa mini zuciya angel bake kika ce bakya so na ba?" Cikin shassheƙar kuka ta ce.
"Kuma don na faɗi haka sai ka daina zuwa ko?"
"To tunda baki so na me zan miki?" Ta tura baki ta ce "Ni ba ruwana da kai,mun ɓata" ta ɗan dire ƙafarta tana ƙara sautin kukanta.
Juyawa ya yi ganin ba kowa a wajan ya ɗan lumshe idanunshi yana jawota gefensa trying to hug her ya ce "Ohhh am sorry my rigimammiya yanzu gani" ya share mata hawayen tas yana riƙe da ita sosai kuma ba tai ƙoƙarin guduwa ba. Ya riƙe haɓarta ya ce "Ina son ganin Inna Angel zaki kiramin ita?" Kai ta ɗaga masa yaja hancinta tare da kai baki kamar zai sumbaci wajan ta zilli da sauri tana masa dry. Girgiza kai kawai ya yi yana tsaye ta dawo ta ce Inna ta ce ya shiga, da fara'a Inna ta amshesa bayan sun gaisa ya zayyana mata abin da ke faruwa, da zuwansa garin da ganin Afra da ya yi ya ɗauka matarsa ya yi mata bayanin komai.
Ta jinjina kai ta ce "Ikon Allah, ashe rabon ganin wani dangin ƴar Baba ne ya sa kuka haɗu, Ubangiji ka amsa mana wannan addu'ar"
"Amin" Adnan ya amsa idanunshi akan Afra wacce tayi kwance a cinyar Inna sumarta gwanin sha'awa duk ta bayyana domin ita har tafi Abra tsayin suma.
"Ai ba zama bari a ki rawo kawonta sai an yi magana ta fahimta ko?"
"Hakan yafi ina son komawa,amma sai an tsayar da manufa" "Ƴar Baba maza jeki kira kawonki yanzu" miƙewa tayi ganin Adnan ɗin ne kuma yasa ba tai musu ba. Suna zaune ta dawo tare da kawon nata. Sun gaisa da Adnan cikin sakin fuska, da farin ciki bayan ya gama jin komai ya ce. "Allahamdulilla Allah abin godiya, yanzu dole mu fara ji idan ita ƴar baba na son shi kuma zata aure shi ko?" Inna ta ce "Haka ne" ya juya kan Afra ya ce "Ƴar Baba kina son Adnan ɗin?" Ta kalli Adnan wanda yake Kallonta yaji abin da zata ce duk a tsorace yake. Kamar daga sama yaji ta ce "Kawo gaskiya bana son shi, kawai iyaye na nake son a kawo mini ko akai ni wajansu amma ba zan aure shi ba" Innalillahi wata zufa ce ta shiga yankowa Adnan ya kasa cewa komai sai kansa da ya sunkuyar zuwa ƙasa.
"Yarona Adnan kada kaji komai, ina son ka kira wasu naka muyi magana ta fahimta batun ƴar Baba ka barta akwai ƙuruciya kaji ko?" A sanyaye Adnan ya yi musu godiya kana yabar gidan.
Ikon Allah ne kawai ya kai Adnan gida yana zuwa wani zazzaɓi ya rufe shi jikinsa sai rawa yake, barci ya gagari idanunshi rashin Afra tamkar rasa ransa ne. Da gari ya hawaye ya kira Abbi ya faɗa masa komai tunda ya san Abba ba zai ɗauki abin serious ba. Ya kira Uncle Khabir tare da Uncle Mustapha ya faɗa musu komai.
Abu kamar wasa har Abbi ya yi dirar mikiya a ƙauyen shi da Salmanun-faris Adnan bai iya cin komai ba, ya fito cikin ƙyakkyawar shiga ta amy colour ɗin shadda wacce ta yi masa kyau. Lokacin suna ƙofar gidan Hakimi Salman na cikin mota yana vedio call da Mami little nayin dry.
Ganin Adnan ya sa Abbi ya yi Sallama dasu Hakimi idanunshi akan Adnan ya ce "What happing to you son? You looks so Lean and weak" murmushi kawai Adnan ya yi ya ce "Am okay Abbi ya mutan gidan?"
"Lafiyarsu lou har little,tare muke da Salman ya dawo garin" shiru Adnan ya yi rabonsa da Salman har ya manta tun a ɗakin da Abra ta rasu, daman haɗuwar ƙarshe da sukai ba mai daɗi sukai ba, yasan zuciyar Salman ɗin cike da jin zafin shi.
"Muje mota mu ƙarasa ko?" "Abbi a ƙasa za a shiga" Abbi ya ce "Ohh to bari na kira Salman" Salam na cikin mota Abbi ya bubbuga yana kiran sunansa. "Yes Abbi" buɗe motar da zai yi idanunshi ya sauka akan Adnan wanda yake tsaye ya zura hannunsa a cikin Aljihu.
Fitowa ya yi shaddar jikinsa na ƙara wacce take iri ɗaya data Abbi, shi bai san me ya kawo su ƙauyen ba, bai taɓa tunanin zai haɗu da wannan mugun mutumin ba da bai zo ba.
Babu wanda yaiwa ɗan uwansa magana Abbi na lura dasu bai ce komai ba, duk da har yanzu babu wani babban dalilin daya sanya suke hakan a garesa zai ma iya ɗauka ko rashin sabo da juna ne. A haka Adnan da Abbi na gaba Salman na baya shima hannunsa a Aljihu yana ƙarewa ƙauyen kallo har suka isa ƙofar gidan su Afra daman kawon nata yana nan. Iso akai musu suka zauna saman tabarma Salman bai shigo ba ya tsaya ɗaukan wayar Ammi dake tsokanar shi.
"Yaronku ya zo mana da zance wanda a garemu zance mai muhimmanci ne, duba da halin da yarinya ke ciki muna saka ran ta dalilinsa zamu samu iyayenta, shi ya sa na nemi ganin wani nasa mu tattauna akai da