Showing 21001 words to 24000 words out of 231718 words
Chapter 8 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt
surutai ake yi, amma ko yarinyar da ake jarabar a kanta ba mu gani ba." Cewar Granny tana yatsina fuska cike da rikicin tsufa.
Captain da hankalinsa gaba-d'aya yana kan Abra, ya miƙe ba tare ya yi magana ba ya nufi ɗakinsa, Na'ima ta bi shi da kallo hawaye na zuba daga cikin idonta, wani irin haushinsa cunkushe a cikin zuciyarta.
Yana shiga ya tarar Abra ta tashi daga baccin, tana ta kuka tare da kiran sunansa. Rungume ta ya yi tsam a jikinsa ya shiga rarrashin ta. Ajiyar zuciya ta saki tana kallon fuskarsa cikin maganarta da ƙarfi ta ce. "Abbi"
"Na'am My daughter, I'm sorry na tafi na bar ki ke kaɗai ko?" Ya yi maganar yana shafa kanta. Duk da ba ta ji me ya ce sosai ba sai ta tura bakinta gaba. Kissing kuncinta ya yi cikin murmurshi sannan ya ɗauke ta suka fito parlour.
Kallon Abra kawai su Ammi suke cikin mamaki. Ammi ta ce. "Ikon Allah, wannan yarinya haka kamar Balarabiya?"
Wani salati Granny ta rafka tare da miƙewa tsaye tana gyara ɗaurin zaninta ta ce. "Huhuhu, mutanen duniya babu gaskiya da tsoron Allah, ban da tsabar sharri ina Khamalu zai haifi wannan kyakkyawar yarinyar mai zubi da turawa, yana ɗan baƙi da shi? A gaskiya wannan mata babu abun da za mu ce miki sai dai kawai Allah ya shiga tsakaninmu da ke, haka kawai kina daga kwance ki narkawa jikana sharri, bayan kuma kina zaune a cikin gidansa kin gama cin abincinsa kin yi ƙat dake, kin murmuro daga ramar da kika zo da ita." Ammi ta ce. "Hajiya wannan maganar fa an wuce ta, ɓacin rai ne ya saka Na'ima ta yi haka."
Baffa da ya kasa ɗauke idonsa daga kan Abra ya miƙa mata hannu, ba ta yi musu ba ta je gurinsa, ko dan ta ga suna kama da Abbinta ne. Baffa ya ce. "Allah Sarki, sannu yarinya, Allah ya bayyana iyayenki." Ammi ta amsa da Amin. Granny ta zo zata ɗauki Abra ta ƙi yarda da ita, da ta takura sai Yarinyar ta saka kuka ta koma gurin Abbinta ta lafe a jikinsa.
Riƙe haɓa Granny ta yi ta ce. "Yau na ga yarinya da jaraba, dan ma zan taimaka in ɗauke ki ba tare da na san daga inda kike ba shine zaki mun tijara, ban da ma zuciyar musulunci irin tawa mene haɗina dake? Aba jawur a koɗe kamar ƙosai" Ta taɓe baki tare da komawa ta zauna tana cigaba da mitocinta.
Baffa ya miƙe yana duban su Captain ya ce. "Mu za mu wuce, sai a daɗa hak'uri da juna, ɗa kuma na kowa ne, idan ka riƙe na wani kai baka san wa zai riƙe maka naka ba." Na'ima ta danne zuciyarta ta ce. "Insha Allahu Baffa, mun gode Allah ya ƙara girma."
"Baffa ba za ku jira a yi Sallah ba sai ku tafin, kuma ko ruwa fa ba ku sha ba." Cewar Captain.
Baffa ya ce. "Alhamdulillah, wucewa za mu yi, na ga sauran lokacin da ya rage a kira sallah zai kai mu gida insha Allahu."
Granny ta ce. "Dama ba'a yi niyyar ba mu ruwan ba, sai yanzu za'a wani ce mu zauna mu sha." Captain ya dube ta ya ce. "Kin taɓa zuwa gidan kafin yau an hana ki ruwan ne?"
Ɗaure fuska ta yi ta ce. "Ni dai ba zan biye ka mu yi tashin hankali ba tunda ba halina ba ne kowa ya shaida, ato." Sannan ta mayar da duban ta ga Baffa ta ce. "Sai dai in ce ku gaishe da gida, dan ni anan zan zauna in kula da wannan zabiyar yarinyar mai ƙwala ƙwalan idanuwa kamar na kakata haulatu, tunda ita wannan asararriyar ta yi nauyi ba iya kula da ita za ta yi ba, tana juyi da ƙyar tana mirgina uban ciki amma se jaraba, gobe idan Allah ya kai mu Shureim sai ya kawo mun kayan sakawata."
Baffa ya ce. "A'a tare za mu wuce da ke yanzu, Iman ta zo ta zauna a nan ɗin tunda sun kusa yin hutu a school." Bai jira cewarta ba ya yi gaba. Granny ta bi shi da wani irin kallo sannan ta miƙe ba tare da ta yi magana ba ta yi waje fuuu. Ɗan murmushi Captain ya yi ya bi bayansu.
Ammi ta miƙe tana duban Na'ima ta ce. "Ki yi hak'uri, na san zaki ga kamar ba'a kyauta miki ba, amma ba rashin kyautawa ba ne, hakan shine dai-dai. Ɗa na kowa ne, sanadiyyar riƙon yarinyar sai ki ga Ubangiji ya baki wani abun da baki taɓa zo ba a cikin rayuwarki, dan Allah ki riƙe yarinyar nan saboda da Allah, kar ki cutar da ita. Kema ba ki san me gaba zata haifar ba"
Na'ima ta share hawayen fuskarta cikin dakiya ta ce. "Insha Allahu Ammi, ɗazun ma ɓacin rai ya saka na yi hakan, ku yi hak'uri, insha Allahu komai ya wuce. Ammi ta ce. "Yawwa, Allah ya yi albarka, ya sauke ki lafiya." Ta amsa da Amin tare da miƙewa ta raka Ammi bakin ƙofa.
A haukace ta dawo cikin parlour ta shiga bedroom ɗinta ta kulle ta ɗauki wayarta ta kira lambar Yayarta, tana jin ta ɗaga ta fashe da kuka ta ce. "Na shiga uku Aunty, ina cikin damuwa, Khamal ya zo mun da wata masifa cikin gidana." A rud'e Aunty ta ce. "Subhanallahi! Mene ya faru?"
"Yarinya ya kawo mun cikin gidana wai za mu riƙe ta, a cewarsa wai a operation suka tsinto ta, ni kuma na san wallahi k'arya yake yi ƴarsa ce suka haifa da wata karuwar a waje."
"Ya aka yi kika san hakan? Ke da kullum cikin yabon Captain kike akan kamewarsa da rashin bin matan banza?"
"Aunty ba ki ga yanda suke yi da yarinyar ba ne, shak'uwarsu ta fi ƙarfin a ce a cikin abun da bai 1 month suka yi kamar ta ba, kuma baki ga shegiyar Yarinyar ba, kyau kamar ita ta yi kanta, irin kyawun nan dai na ƴaƴan shegu, dan dama a gurin aikin nan nasu akwai mata masu bibiyarsa. Na kira iyayensa kuma domin su zo a yiwa tufkar hanci amma sun goyi bayan ɗansu, ni na yi kara ban kira nawa iyayen ba dan kar ace sun zo sun goyi da bayana, ashe su ma son kai za su yi. Wallahi Aunty ba ki ji yanda zuciyata take mun zafi ba, ni dai ba zan zauna da wannan yarinyar a gidan nan ba, ki bani mafita Please."
Aunty ta ce. "Shi Captain ɗin ya kuka yi da shi?, ki nuna masa bakya san riƙon yarinyar mana."
Cikin sheshshek'a Na'ima ta ce. "Aunty cewa fa ya yi sai dai in zaɓa ko in riƙe ta ko in bar masa gidansa, ya zaɓe ta a kaina, duk irin tarin soyayyar da Khamal yake mun amma yau ni yake faɗawa haka? ba dole in ji na tsani Yarinyar ba tunda a kanta ya faɗa mun haka."
Cikin mamaki Aunty ta ce. "Shi Captain ɗin ne ya faɗa miki haka?"
"Wallahi Aunty shine." Nan ta kwashe labarin duk abun da ya faru ta faɗawa Aunty. Cikin ɓacin rai Aunty ta ce. "Lallai ma Khamal, yanzu akan wata banza can shine zai nemi ya wulak'anta ki? Ya fifita ta a kanki? To amma idan ya san wata ai bai san wata ba, ki k'yale shi ki taushi zuciyarki, ki nuna masa kin amince zaki riƙe yarinyar, taa k'ark'ashin ƙasa za mu biyo masa, a gabansa ki dinga nuna duk duniya babu wanda ya kai ki k'aunar Yarinyar, a bayan idonsa kuma ki dinga cin ubanta son ranki kina gallaza mata, yanda komai ƙanƙantarta da kanta za ta nemi ta bar gidan, koma ta gudu da ƙafafuwanta."
"Ta yaya Aunty? Yarinya ce fa k'arama, ba tafi shekara uku ba, ni fa kawai damuwata yarinyar nan ta bar gidan nan a yau. Dan ba zan raini 'yar haram ba in ci kashinta in ci fitsarinta ba"
"Daɗina dake gajen hak'uri, ki yi yanda na ce miki kawai, da kissa da makirci zaki kori yarinyar daga gidan ba tare an yi tunanin ke kika aikata hakan ba, amma fa dole sai kin danne zuciyarki kin ajiye wannan masiffaffen kishin naki a gefe, in kuma ki kayi dalilin kashe Auren naki ai kin huta." Haka Aunty ta dinga tausar Na'ima da koya mata irin abubuwan makircin da za ta yi, har aka yi Sallar Magriba suna wayar, sai da ta ji shigowar Captain gidan sannan ta yi mata sallama ta share hawayen fuskarta ta tashi ta fito parlour.
A tsugunne ta tarar da shi yana cirewa Abra takalmin ƙafarta wadda ke shan choculate hankali kwance. Wani abu ne ya soki zuciyarta, wato masallacin ma da yarinyar ya tafi saboda tsantsar k'aunar da yake yi mata. Danne baƙin cikin da ya taso mata ta yi ta kakalo murmushi ta ce. "Sannu da zuwa My Man." Ko d'agowa bai yi ba balle ya ba ta amsa. Ƙarasawa ta yi ta tsugunna a gabansa cikin kissa ta ce. "Magana nake maka fa." Nan ma banza ya yi da ita. A hankali ta kamo hannunsa cikin marairaicewa ta ce. "Dan Allah ka yi hak'uri My Man, na tuba na gane gaskiya, wallahi ɗazun ma sharrin shaidan ne." Ta ƙarashe zancen idanunta cike da ƙwalla.
Ba tare da ya kalle ta ba ya ce. "Ya wuce." Yana ƙoƙarin janye hannunsa daga nata ta riƙe shi gam tare da sakar masa kuka. Numfashi ya sauke ya ce. "Mene haka kuma? Ba na ce na hak'ura ba?"
"Ai na san ba ka hak'uran ba, Please My Man ka san ba zan juri fushinka ba." Sakin fuskarsa ya yi ya ce. "Komai ya wuce ki bar kukan nan haka." Sannan ya saka hannu ya shafi cikinta cikin k'aunar Unborn ɗinsa." Ajiyar zuciya ta sauke ganin da gaske ya hak'uran. Hannu Abra ta kama ta ce. "Zo nan Daughter." Ƙin zuwa ta yi ta lafe a jikin Major tare da kwab'e fuska za ta yi kuka. Duk da haka ba ta yi zuciya ba ta shafa fuskarta ta ce. "Ya sunanki?"
"Abra."
Captain ya ba ta amsa idanunsa akan Abra.
"Wow nice name, Allah ya raya mana ke"
"Amin"
"Bari na je na yi Sallah." Na'ima ta faɗa tana miƙewa, dan dauriyarta ta kusa ƙarewa akan pretending ɗin da take yi, ji take tamkar ta janyo Abra ta shaƙe ta ta mutu saboda tsanarta dake ƙara cika mata zuciya.
Bai ce komai ba sai bin ta da ya yi da wani irin kallo, darajar cikin cikinta ta ci, da kuma nasihar da Ammi ta yi masa bayan sun fita, akan ya yi hak'uri ya mayar da komai ba komai ba tun da Na'iman ta yi nadamar abun da ta aikata, shi yasa kawai ya haƙura, amma da ya yi niyyar sai ya hukunta ta akan hauka da ƙazafin da ta yi masa.
LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.
'Yan uwa da abokan arzkin wanda aka sacewa 'yan uwa hankalinsu yaƙi kwanciya, gani suke babu wani yunƙuri da gwamnati take yi, dan karɓo musu yaransu, musamman masu 'ya'ya mata a ciki.
Suka dinga kira ga gwamnati, akan Lallai a biya su wannan kuɗi, a karɓo musu yaransu.
Yayin da gefe guda, gwamanti na ta ƙoƙarin ganin yadda za'a karɓo yaran, ba tare da an illata wani ba, kuma ba tare da an biya wannan kuɗi ba, idan aka kwashi wannan zunzurutun kuɗi aka bawa 'yan ta'adda hakan ƙarara ze ƙara nuna gazawar gwamnati, wanda babu gwamnatin da zata so ace ta gaza.
Taro aka gabatar cikin dare, in da aka siyo manyan makaman yaƙi, da za'a rabawa Sojoji, cikin sirri aka kawo makaman aka saye su, a in da tsirarun da aka yadda da su a harkar tsaro ne kawai suka sani.
General Ibrahim ne tare da ƙaramin ministan tsaro, suka ɗai a wani ɗaki suna tattaunawa cikin harshen turanci.
Ƙaramin minista ya kalli General Ibrahim yace "ai mu wannan abu gaba ta kaimu, ka saka amintattun yaranka su fita da wasu daga cikin kayan da na gaya maka, aka kaisu wannan mararrabar, masu shi za su zi su karɓa, kuma akwai ƙishin ƙishin tun da gwamnatin tarayya ba zata karɓo su ba, Gwamnan jihar ze rage wani abu ya basu ya karɓosu, wanda muna da kaso me tsoka a ciki".
General Ibrahim yace "an gama ranka ya daɗe, duk yadda kace haka za'ai, sannan akwai wasu sojoji, da aka kora suke ta ragaita a gari, cikin sirri zan janyo su cikin harkar nan, zasu bada gudunmawa sosai da sosai".
Minista yace "ni dai fatana kar a samu matsala, dan idan aka samu matsala na san yadda zan zame kaina in barka".
General yace "ba za'a samu wata matsala ba, za'a fitar da makaman a siyar musu da wasu"
"Good" suka cigaba da tattaunawa akan yadda za su yiwa harkar tsaro zagon ƙasa dan gina kawaunan su.
Yau kuwa gidan Captain Khamal, bayan Sallar isha'i suna zaune a kan carpet suna yin dinner da Pride rice with chicken ɗin da Na'ima ta yi musu, Abra dai ta ƙi ci dan har yanzu ta kasa sabawa da irin abinciccikan nan, sai fruits Captain ya bayar aka siyo mata masu yawa take shan abun ta, hakan ba ƙaramin ƙara ƙonawa Na'ima rai ya yi ba. Suna cin abincin amma hankalin Captain gaba-d'aya yana kan Abra, da ta yi motsi zai ce. "What happen Daughter? Ko, What do you want?" Ko Abincin ya ƙi maida hankali ya ci, ya lalace akan Abra. Imagining take da babu wannan shegiyar yarinyar, da tuni yanzu tana jikin Mijinta tana zuba masa shagwab'a yana tattalinta, yana ririta ta kamar ƙwai. Gashi ƙarin abun takaicin yarinyar ta ƙi yarda da ita ko kaɗan, duk irin wayon da ta yi mata amma yarinyar ta ƙi zuwa gurinta.
Bayan sun gama cin abincin da kansa ya yiwa Abra wanka ya kwantar da ita ya tofe ta da addu'a, sai da ya ga ta yi bacci sannan ya baro ɗakin da take.
Sai a wannan lokacin Na'ima ta samu ya ba ta full time ɗinsa a kanta, ya nuna mata soyayya kamar yadda ya saba, tamkar babu wani abu na ɓacin rai da ya faru a tsakaninsu.
Washegari da safe Captain yana bacci Abra ta yi kashi a ƙasa a cikin toilet ɗinsa, duk da zaman da ta yi a gidan Madam Halima, amma har yanzu ba ta saba da hawa kan toilet seat ba idan za ta yi kashi. Na'ima tana ɗakinta a lokacin suna waya da mahaifiyarta tana ba ta labarin abin da ya faru, ba ta san me Abra ta aikata ba.
LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.
[9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU*
_Brigh pens✍️_
Nimcyluv
Ayushercool
Zee Kumurya
P7
Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks
https://arewabooks.com/book?id=6220842688e1ec3a0410329f
https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949
https://arewabooks.com/u/nimcyluv
Elegant online writers
LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.
Cikin wani irin ɓacin rai, Na'ima ke bin Abra da kallo! Wacce ke tsugune a toilet ɗin Captain, tayi kashi a ƙasa gaba ɗaya ta ɓata toilet ɗin da jikinta.
Bata taɓa jin, akwai wani data taɓa tsana a duniya kamar ABRA KHAMAL ba, ta tsani Yarinyar tsana mai yawan gaske. Gani take shigowarta rayuwarsu gaba ɗaya matsala ce.
Wannan dalilin ke sa wa Na'ima ta ƙara jin ranta ya ɓaci akan Abra. Kishin Abra ya kama Na'ima, irin kishin nan na tsakanin Kishiya da kishiya (crazy jealousy) mussaman yadda ta ga Khamal ɗin ya na bawa Abra kulawa.
Rai ɓace, Na'ima ta ja hannun Abra zuwa Part ɗin ta, Abra na tirjewa tana ƙoƙarin ƙwala kiran sunan “Abbi” Na'ima ta hankaɗa ta zuwa cikin toilet ɗin dake nata part ɗin. Wannan shi ne dama ta Farko, Da Za tai amfani da ita wajan cin Uban Abra, ta san idan tace a part ɗin Captain Khamal Khamis zatai Punishing ɗin ta, Tabbas zata ɓata rawar ta da tsalle, wanda zai sanya Captain Khamal Khamis ya din ga yi mata kallon Munafuka mai Fuska biyu, ita kuma bata son duk wani abu da zai shafi mu'amalar ta da Khamal.
"Zaki ci Ubanki, ƴar banza mai siffa irin ta sadaka yalla!" Na'ima ta faɗa tana murɗe kunnen Abra cike da mugunta, zafin da Abra taji ya sa ta saki wata siririyar ƙara mara sauti, saboda rufe mata baki da Na'ima tayi.
A fusace kuma ta shiga zarewa Abra, kayan jikinta tare dayi mata tsirara.
Ficewa Na'ima tayi, daga cikin toilet ɗin ta nufi ƙofar part ɗin nata, cikin sauri ko lura da cikinta ba tayi, taja ƙofar ta rufe, ta sa mata key, saboda kada Khamal ya jiyo sautin kukan Abra.
Tana komawa toilet ta nemi wayar chaji, Abra na durƙushe in da ta ajiyeta, babu zato ta ji saukar bulala akan fatar gadon bayanta.
Ihu ta saki da dukkan ƙarfinta tana kiran sunan Abbi, bata taɓa tunanin akwai azaba irin wannan ba, saukar bulalar ya gigita Abra Khamal Khamis ƙwarai, har wani irin shiɗewa take na rashin sabo!.
Na'ima tace "Yadda ki ka rabani da farin ciki na, ki kai sanadiyyar shiga tsakani na da mijina, haka zaki dauwama cikin gidan nan ina gana maki azaba kala kala, wacce zata saka da ƙafarki ki fice ki bar min gida na,
Gidana nawa ne, da ga ni, sai Mijina sai kuma yaran da zan haifa masa, bana buƙatar kowa cikin rayuwarmu, zuwanki ya ruguza min dukkan wani burina, ba zaki taɓa jin daɗi ba in dai a gidan nan ne, mufuka, Algungumin".
Tai Maganar Kamar ta na yi