Showing 201001 words to 204000 words out of 231718 words

Chapter 68 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt

28 Feb 2025

14681

ya yi shiga mai kyau. Sai ƙamshin Pur oud yake lokacin daya fito gari ya yi duhu sbd hadarin dake kwance a garin Kadunan.

Ba tare da sanin Hajiya Mama da Abba ba ya nufi Kano cikin duhun asuba sai gudu yake shararawa burinsa kafin 11 na safe ya yiwa Kano tsinke idanunsu ya sauka akan Afra ko ya samu sauƙin ciwon da zuciyarsa ke masa akoda yaushe. Cikin wannan tunanin ya ƙarawa motar giya.

Afra na zaune cikin wata white-collared t-shirts tare da wani red cropped trousers ta ɗora wata red ɗin kinomo a saman kayan, tayi kyau sosai domin duk a cikin kayan da Abbi ya bada akai mata shopping ne. Hannunta riƙe da Aishatul-humaira wacce a kullum ƙara wayo take. Mami data fito ta ce.
"My dear kinji daɗi Little bata miki halin nata, ko dai ta gane ke Mother ɗin ta ce?"

"Wallahi Mami ina sonta sosai, bana son rabuwa da ita kamar muna kama ko?" Kafin Mami tayi magana Salman dake gyara zaman babbar rigarsa ya ce.
"Dake da ita ban san wanda nafi so, ina tunanin burina ya kusa cika"

"What are you saying Salman?" Ya shafa sajan fuskarsa yana basarwa ya ce "No Mami,ina breakfast ɗina?" Mami ta Harare shi ta ce.

"Liar, It's like I heard you say something?" Ya girgiza yana zama kusa da Afra idanun shi akanta ya ce.

"It seems that Mami's ear is starting to have problems. Amma breakfast na ce ta, yunwa zata hallaka miki ɗan yaro Mami"

"Allah ya shiryaka Salman, yunwar ka kewa haka?" Ya marairaice fuska sosai wanda ya bawa Afra mamaki ya sanya ta buɗe baki tana kallon ƙato da shagwaɓa. Da ƙyar ya ce

"Da gaske Mami yunwa na keji sosai, Yaya Please abinci" ya faɗa tare da juyawa ya kalli Afra wacce ke riƙe da Aishatul-humaira tana mata tsalle tsalle da ƙafa a cinya.
Barin wajan Mami tayi cike da fatan samawa Salman nasara domin ta riga da taji abin da ya ce.

"Why are shy yaya my angel?" Ya faɗa yana saka hannunsa zuwa haɓarta tare da juyo da fuskarta suka fuskanci juna. Fararen idanunsa masu kaifi wanda suke ƙara sawa Afra kwarjinin Salman a idanunta ya zuba mata ya ce.
"Ba haka yaya Abra ke mini ba, na sama hira da yayata sosai wani lokacin daja hancina kamar like this" ya ƙare maganar yana jan hancinta cike da ƙaunar ta wacce lokaci guda ta mamaye dukkan zuciyar shi.
Cikin siririyar muryar ta ta ce "Uhm to aini ban girmeka ba" ya lumshe idanunsa yana mai girgiza kansa kaɗan tare da tura hular kansa zuwa gaba ya ce.

"Injiwa? Tsakanina da Abra good 3yrs ne, ke da Abra twins shekara ɗaya aka haife ku Kinga kin zama yayata"

"Kuma na ganka ƙatoto ni kuma ƙarama" zuba mata gajiyayyun idanun shi ya yi yana karantar yanayin ta sosai kafin speaking calmly ya ce.

"Sbd ni ne mijin ai" ta ware ido ta ce "me kace?" Ya girgiza yana miƙewa tsaye tare da ɗaukan Little ya ce "I'll explain later" kafin tai magana ya miƙar da ita tsaye ba zato taji ya jawota ɓarin jikinsa ya yi musu photo yana murmushi ya ce "My family my happiness, zuri'ar Salmanun-faris" ita dai bata fahimta ba, sai saurin zame jikinta da tayi zuciyarta na bugawa da ɗan ƙarfi.

Dining room suka nufa a can suka samu Salima Abbi daman tun 7 yabar gida yin binciken asalin iyayen Afra da Abra. Jikin Salima na ɗan rawa ta ce "Salman my son bari na serving naka abinci" idanun shi akan Afra ya ce. "No thanks, Afra please serve me" ya faɗa fuska a kame.
Salima bata so hakan ba domin gaba ɗaya Salman birgeta yake tana neman duk yadda da zata samu connection da shi amma ya toshe ba lallai idan yana mata kallon matar Mahaifin nasa ba.
Afra tai serving nasa a nutse take har kar nan gudun kada ta kwafsa, ta nuna ƙauyancin nata shi ya sa ta kame kanta da kyau domin siyawa kanta martaba da ƙima a idanun jama'ar gidan.
Ganin daga Afra har Salman abinci suke ci babu wanda yako kalli inda Salima take, ya sanya jiki a sanyaye ta miƙe kamar zata ɗauki Little wacce take barci a jikin Salman ta wani ƙanƙame shi da duk hannunta biyu sai kawai ta fasa da ɗan sauri tabar wajan.

Suna cin Abinci Mami ta fito cikin kwalliya sai ƙamshi take, ganin Afra da Salman ya bata sha'awa. Ta ɗauki Little tare da bar musu wajan. Lokaci zuwa lokaci Salman ke satar kallon Afra yana jin kamar ya faɗa mata abin da ke zuciyarsa kada ya ƙara rasa damar shi a wannan karon.

"I love You"
Ya furta a hankali daidai yadda za taji da sauri ya ɗago kanta ta kalle shi ganin kamar ba shi ne ya yi maganar ba, yasa ta ɗauke taci gaba da cin abincin maybe kunnuwanta ne kawai suka ji haka.

Murmushi mai laushi Salman ya yi kyansa na fita calmly ya kuma cewa.
"Ina son ki Afra, and I ready to marry you....."

"Kai da Afra har abada domin ta haramta a gare ka ni ne zan aureta" daga Afra har Salman suka ɗago kansu, ganin mutum dake tsaye ya sanya Salman yin murmushi wato tarihi zai maimaita kansa kenan. Jikin Afra na rawa ta miƙe tsaye domin bata tsammani ganinsa ba a daidai wannan lokacin. Ƙoƙarin guduwa take ya sanya hannu tare da cafkota idanun shi sun kaɗa tare da yin jaa sosai kamar gauta cikin rawar murya ya ce.

"Ni nake son ki ƴar baba tun kina ƙauye, ni ne na yi sanadiyar zuwanki nan gida, kuma a shirye nake da aurenki idan kin amince Wallahi ina son ki Please don't say No!"

"Wallahi bana son ka, ba zan taɓa son ka ba, koda zaka mutu, ni ka rabu dani ka takura mini" Innalillahi Adnan gani yake da wannan maganar gwara ta ɗauki wuƙa ta caka masa zai fi masa sauƙin fahimta. Cikin damuwa ya ƙara matsawa gareta tare da ɗora hannunta a saitin ƙirjinsa idanunsa na sauya kala yana cika da hawaye ya ce.
"Ki taimaka, ki taimaki rayuwata Afra, ko baki so na ki aure ni haka, indai zaki zauna dani matsayin miji ban damu da rashin soyayyar ba.
"Ni dai ka sakeni, ba zan iya auren wanda bana so ba, sbd ba zan masa biyayya ba ga mata nan da yawa a duniya haba"

Tashin hankali ya bayyana akan fuskar Adnan yau shi ne mace ke wahalar da rayuwar shi har yake zubar mata da hawaye? Lallai soyayyar Abra tayi tasiri a zuciyar shi,
Domin son da yake mata ya sanya ba zai iya rayuwa babu Afra ba a yanzu komai nasu iri amma me ya sa halinsu ya bambanta?.

Yi ya yi kamar zai jawota jikinsa tayi saurin ja baya kusa da Salman hawaye na zuba a fuskar Adnan sosai ya ce.
"Don darajar Allah ki duba halin da zuciyata take ciki, ki sassauta yanayin ki a kai na, ki bani dama na sauya tunani zaki so ni ina da tabbacin zan sauya miki ra'ayi da kanki zaki furta kina so na, zan fifitaki da sauran mata, zan baki farin ciki da duk abin da kikeso, zaki rayuwar ƴan ci a gidan Adnan Aliyu Matawalle..... I love You Afra, i love You to the rest of my life, I can't imagine life without you wlh ina son ki ba zaki taɓa samun wanda zai so ki kamar ni ba"

Salman ya gyara tsaiwa tare da gyara zaman babbar rigarsa cikin nutsuwa ya kalli Adnan kana ya juya ya kalli Afra a hankali ya saka hannu ya kama nata cikin nutsuwa ya ce.
"Look into my eyes yaya" kasa kallonsa tayi Ubangiji yana gani Salman mugun kwarjini yake mata, yana yiwa idanunta tasiri sosai ba kaɗan ba.
"Please yaya" ya ƙara faɗa a taushashe har ƙamshin spraymintt mouth freshener ɗin bakinsa yana dokan hancinta wanda ya sanya tayi saurin lumshe idanunta. ganin da gaske ba zata kalle shi ba ya sanya gaba ɗaya ya tallafo haɓarta yana sauke mata numfashi a fuska kamar zai haɗe fuskokinsu ya ce.
"I love You Afra, From the moment I first laid eyes on you, I knew you were a perfect match for me. I love everything about you. Ina son ki so mai yawa, ina kishin da zai ɗauke numfashin sarrafa rayuwata, kada ki yi mamakin ganin bamu daɗe ba, ina jinki tamkar yaya a raina, ki bani dama na bayyanawa kowa irin soyayyar da nake maki, bana son nayi zurfin cikin da nayi a kan Abra. I will be always by your side in good and bad times, in happy and sad moments… because I love you! Accept my request please yaya"

Ya kama fuskarta da dukkan hannunsa wanda itama a lokacin ta buɗe idanunta tare zuba masa su. Tana son fahimtar da gaske wannan kyakkyawan farin ne yake son ta kuma yake son aurenta?

"Please yaya"
Ya marairaice fuska yana narke mata. Kasancewar rayuwar ƙauye tayi babu wanda kunya sosai a tare da ita bakinta kuma baya sarrafa wani abubuwan kafin ta faɗa. Muryar ta na rawa ta ce.
"Ina son ka ni ma, kuma zan aureka in dai da gaske kake zaka aure ni"
Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya Salman ya sauke yana ƙara riƙe fuskarta da kyau! Wani farin ciki na ratsa zuciyarsa.

A fusace Adnan ya fisge Afra daga wajan Salman idanunsa na zubar da ruwa bakinsa da gaba ɗaya jikinsa suna rawa kamar ana kaɗa masa gangi ya ce.
"Ƙarya yake Afra, ta ya ya zaki aure wanda ki ka girma yayanki ne shi bai dace ya zama mijinki ba, ni ne daidai da rayuwar ki" ya faɗa yana jawota jikinsa sbd zafin da zuciyarsa ke masa.

"Don't try to hug the girl I'm going to marry again, na fika hauka zafin kishina yafi naka, kuma ka kusa daina ganin ko fuskarta, ita ɗin mallakina ce"

"Idan kai namiji ne sai ka hanani abin da na yi niyya" Adnan ya faɗa cikin raunin murya tare da ƙoƙarin kama bakin Afra da niyyar kissing. Cikin zafin zuciya Salman ya tattare hannun rigarsa farar fuskarsa ta yi jajir sbd abin da Adnan ɗin yake ƙoƙarin yi ɗin.

Saukar marin da Salman ya ji ne ya sanya ya tsaya da sauri baki buɗe yake kallon Afra wacce ta fisge kanta da ƙyar daga hannun Adnan ta kuma sauke masa marin da ita kanta bata san tayi ba. Idanuna ya cika da hawaye sbd nauyin marin da tayi ya kalli Adnan ta ce.

"Wa kake da suna? Wallahi na tsaneka ba zan taɓa son ka maye kawai"

"Koda zan faɗa miki su waye iyayenki na gaskiya?" Ta watsa masa harara ta ce "Ai ƙarya kake tun a garinmu kake yaudarata, babu wasu iyayena daka sani"

Adnan ya fara tari sosai idanunsa na rufewa tari yaci ƙarfin sa. Abbi da Mami da suke tsaye tun ɗazo suka ji kuma suka kaga abin da ke faruwa suka shigo cikin parlourn da sauri.
"Subuhanallah! Adnan lafiya me ya sameka? Na'ima kawo mini ruwa" Adnan yakai hannu bakinsa sai ka jini ya wanke masa tafin hannun da alama kamar aman jini yake. Bai damu da halin da yake ciki ba, tarin na sarƙafe masa numfashi cikin mayuyacin hali ya kalli Afra da jikinta ya gama sanyi baki ɗaya ya ce.

"Ko da zance maki Dr G.Y Bulama shi ne mahaifinki na gaskiya..." Cak numfashin sa ya tsaya jikinsa ya saki a jikin Abbi, a kiɗime Abbi ya ce "Salman get the car"


A hankali cikin nutsuwa da kamala Abdullah ke driving motar daga Airport zuwa gida. Yana mamakin abin da ya hana Uncle ɗin magana, girgiza kai ya yi yana mai da idanunsa kan titi yasan yau Ummi kwanan farin ciki za tayi speaking calmly ya ce.
"Uncle lafiya dai?" Wanda aka kira da Uncle ya juya ya kalli Abdullah a hankali ya ce.
"Alhmd Abdullah" ba wanda ya sake magana a haka suka ƙarasa gida, Abdullah yai horn a gaban makaken gidan iya haɗuwa ya yi gatekeeper ya buɗe, a parking lot sukai parking kafin Abdullah ya fita ya riga shi.
Ummi na zaune ta yi ado cikin wani dakakken lace sai ɗaukan ido yake ga gwalalen dake zube a hannunta. Ƙamshin turaren shi yasa ta tabbatar da zuwan mijin nata bayan wasu watanni zuwa shekara. Tsaye ta gansa ya zuba mata idanu cike da tunani a ransa da kuma son Ummi ɗin saura kaɗan ya yi kuskure a rayuwarsa.
Ummi ta miƙe tsaye tare da ƙara sawa gabansa ta ce. "Wlcm Man" murmushi ya ƙirƙira kafin ya ce "I missing Maaah" girgiza kai kawai tayi suka ƙarasa parlour idanunsa a kanta ya ce "Kiran gaggawa ina tsaka da buɗe sabon company hope lafiya dai?" Tai murmushi cikin sanyin maganar ta ce.
"Ka fara yin wanka kaci abinci?"

"I can't dole na fara jin damuwarki a gigice na tahu" ta gyara zama cikin damuwa ta ce "Abubuwa ne suke ta fara, gaba ɗaya dukiyata na neman lalacewa kullum cikin asara da rasa kuɗaɗe nake, na rasa inda abin ya samu tushe ina son magance matsalar, wannan dalilin ya sanya na saka Abdullah ya rufe company ta kalman dana buɗe" Ya runtse idanunsa domin abin ya zo masa a bazata bai ɗauka abin zai sauri har haka ba, shi bama wannan ce damuwar shi ba.
Yana ƙoƙarin magana wayar shi tayi ringing ganin wata number ya share, Ummi ta kafe shi da idanu can dai ya ɗaga a fusace ya ce.
"Wai mene?" Tsaki kawai yaja ya ce.
"Allah ya sawwaƙe" Ummi ta ce "Waye ba lafiya?" Yaja tsaki ya ce "No wani ma'aikacina ne" tana ƙoƙarin wata maganar aka sake kiran shi da sauri ya miƙe ganin number wanda yake ta jira. Jikinsa na rawa yama mance a gaban waye yake.
"Hello, Assalamu alaika" daga can wayar aka ce "Muna magana da Dr Bulama" ya juya ya kalli Ummi ya ce "E, shi ne" aka ce "Mahaifin Adnan Aliyu Matawalle ke magana, ina son ganinka domin samun tabbaci shin da gaske Abra da Afra yaranka ne kai ne real father nasu?" Gaba ɗaya jikin Uncle ko nace Dr Bulama rawa yake ya ce "Oh!ok yanzu haka Ina Dubai, amma zuwa gobe zan sauka Nigeria I'll call you" Abba da Abbi suka kalli juna a tare suka ce "Dubai????" Ya ce "Eh, amma gobe zan zo Insha Allah" kashe wayar ya yi gaba ɗaya jikinsa rawa yake ya ce. "Rumaisa daman yaranmu ba mutuwa sukai ba???" Ummi da Abdullah suka ce "What???....
[11/22, 4:52 PM] Abk: Cikin gigicewa, da gurɓatacciyar hausarta, ta fara haɗa larabci, turanci da kuma hausa, ta kalli Bulama ta ce "Wane irin zance ne kake mini haka? Kamar yaya yaranmu ba mutuwa suka yi ba? Bayan ina labor room, aka ce mini na haifi yara tagwaye amma babu rai?".
Jiki a sanyaye Bulama ya ce "Nima abin da nake mamaki kenan, ta yaya za ce suna raye?".

Ummi ta ce "Wai wani irin zance ne wannan? Baka tabattar ba kenan, ya kake son ka yi mini wasa da hankali Yusuf Bulama?".
Abdullah ya tattaro nutsuwarsa ya kalli Bulama, shi ya iya hausa sosai ba kamr rumaisa ba, ya ce "Ka sakamuna ruɗu ya kai Yusuf, ka sani cewa wannan maganganun naka barazana ne ga tunaninmu, da kuma zukatanmu, amma kuma biri ya yi kama da mutum, zan iya gasgata ka akan abin da kake faɗa, amma bamu labari, kafin ni in sanar da ku wani abu mai mahimmanci da Yakamata in faɗa".
Bulama yayi jimm, sannan ya basu labari tiryan-tiryan yadda abubuwa suka wakana, har zuwa lokacin da Abra ta rasu.
Gigicewa Rumai ta yi, yarana suna raye, ɗaya ta mutu? Waye ya yi mini wannan zaluncin, na rayu shekaru Ashirin da huɗu cikin ɗacin rai da ƙunar zuciya, yarana na raye amma suk rayu nesa da ni, ya za ayi ace na haifi yara aka ce mini sun mutu? Meyasa aka mini haka Ya kai Yusuf, ya a kai ka tabbatar da yarana na raye? Ka kaini in gansu a ina suke, ko da yake kace mini ɗaya ta mutu, to ina ɗayar a ina take? Dan Allah kar ka gaya mini abin da ba zai yiwu ba, in saka rai kuma in zo ba yarana ba ne".

Abdallah yayi ajiyar zuciya ya ce "A shekarun baya,  da naje Nigeria, a garin Kano, naje sayayya wani mall, na haɗu da wata yarinya da sai da hantar cikina ta kaɗa saboda mamaki. Tana tsananin kama da shi Yusuf, kuma akwai wasu kamanni da ta ɗauko na ki, hatta wannan ɗigon baƙin na gefen idonki ta na da shi, mamaki da rikicewa ya sanya na kai hannu fuskarta, wanda suke tare da shi ya mareni, ina tunanin mijinta ne a wannan lokacin, ita yarinyar ta tsorata, har ta suma, ya ɗauketa suka bar wurin. Still a watannin da suka shuɗe, na haɗu da ita a nan Dubai, amma ita da wani daban n kuma ganinta, amma ban yi mata Magana ba saboda wanda suke tare ya mini kwarjini da yawa, kuma ina tsoron abin da ya faru wacan lokacin ya kuma faruwa, idan kuwa haka ne ina kyautata zaton ko da duk mutum ɗaya na gani, ko kuma su biyun ne Amma sanin gaibu sai Allah".

Fashewa da kuka Ummi tayi, tana fitar da tulin damuwar da ke mamaye a ranta, saboda tun bayan haihuwar yaran nan ba ta kuma samun wani rabon ba, kuma gashi Allah ya jarabce ta da son yara, yo ta ina ma zata samu rabo, miji ma wata ƙasar ita ma tana wata ƙasar daban, sai su shafe watanni huɗu wani bai sa wani a idonsa ba.
Cikin kuka ta ce "Abdallah, a gaggauta neman mini visa Nigeria, muje ya nuna mini 'ya'yana, ni da da yadda za ayi, a yanzun nan zamu tafi, amma ni haryanzu na kasa gazgata hakan"

Bulama ya rungumeta a jikinsa yana rarrashinta, tare da bata tabbacin cewa zasu tafi Nigeria tare, dan tabattar da abin da yake faɗa mata.

Afra kuwa ta ɗan fara tausayin Adnan, saboda yadda aka ce yana aman jini, gaba ɗaya baya hayyacinsa, amma sam ita Adnan bai mata ba, kallon mugu take masa, saboda yanayinsa yadda yake wasu abubuwan da zafi, Salman ya fishi kirki da bin komai a hankali, dan haka ita ba ta ga ta yadda zata zaɓi Adnan ba, ga salihi mai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login